• English
  • Business News
Tuesday, August 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Ke Kara Ci Gaban Kasashen Afirka

by CMG Hausa
3 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Yadda Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Ke Kara Ci Gaban Kasashen Afirka
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Layin dogo yana daya daga cikin muhimman ababen more rayuwa da kasashen nahiyar Afirka suka amfana da shi, karkashin hadin gwiwar Sin da kasashen na Afirka, baya ga hanyoyin mota, da gadoji na zamani, da makarantu da cibiyoyin lafiya da makamantansu.

Tun bayan kaddamar da layin dogo na zamani na SDR a ranar 31 ga watan Mayun shekarar 2017 tsakanin Mombasa zuwa Nairobo, da kasar Sin ta gina, shekaru biyar da suka gabata, yanzu haka kasar Kenya ta shiga wani sabon tsari na rayuwa, inda ya sauya harkokin sufuri, da kasuwanci da nishadi a kasar Kenya.

Bayanai na nuna cewa, layin dake tafiyar da jiragen kasa na fasinja guda shida a kullum, ya yi nasarar jigilar fasinjoji sama da miliyan 7.7 a cikin shekaru biyar din da suka gabata. Kana a cikin watanni biyar na farkon shekarar 2022, adadin fasinjojin da aka yi jigilar su ta hanyar layin dogon na zamani, ya kai 962,000, wanda ya kai kashi 63 cikin dari a duk shekara.

Haka kuma, a cikin shekaru biyar da suka gabata, layin dogon ya yi jigilar sama da Tan miliyan 1.7 na kwantenoni. Kana yawan kayayyakin da jirgin kasan dakon kaya ya yi jigilarsu a cikin watanni biyar da suka wuce, ya kai tan miliyan 2.54, karuwar kashi 8.3 bisa dari a shekara.

Layin dogon ya kuma samar da wata kafa ga matasan Kenya, wajen bunkasa fasaha da sana’o’insu da samun kudin shiga, da inganta fasaha da samar da aikin yi da raya manyan sassan tattalin arzikin kasar kamar aikin gona, da masana’antu da yawon shakatawa.

Labarai Masu Nasaba

An Yi Bikin Mu’ammalar Al’Adu Na SCO Na 2025 A Beijing

Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Sin Ta Yi Rawar Gani A Fannin Bunkasa SCO

Baya ga layin dogo tsakanin Mombasa da Nairobi, akwai na Tanzaniya zuwa Zambia (Tazara) da wadanda Sin ta gina a sassan daban-daban na Najeriya da sauran kasashen Afirka, kuma duk sun taimaka wajen saukaka jigilar jama’a da hajoji tsakanin kasashen nahiyar, baya da samar da guraben ayyukan yi da karin kudaden shiga ga mazauna wadannan yankuna, galibi matasa.

Sabon dakin taro na zamani da kasar Sin ta samar da kudin ginawa da aka kaddamar a Zambia a baya-bayan nan, ya kara nuna cewa, alakar Sin da Afirka, alaka ce ta amintakar kut-da kut da mutunta juna da samun nasara tare. Kuma duk kokarin da wasu kasashen yamma ke yi na neman illata wannan dangantaka, ba zai taba yin nasara ba. (Ibrahim Yaya)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Birnin Shanghai Ya Dawo Da Ayyukan Samar Da Kayayyaki Yadda Ya Kamata

Next Post

Jami’an Tsaro Sun Kai Samame A Sansanin Bayar Da Horo Na Kungiyar IPOB Sun Kashe 3

Related

An Yi Bikin Mu’ammalar Al’Adu Na SCO Na 2025 A Beijing
Daga Birnin Sin

An Yi Bikin Mu’ammalar Al’Adu Na SCO Na 2025 A Beijing

4 hours ago
Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Sin Ta Yi Rawar Gani A Fannin Bunkasa SCO
Daga Birnin Sin

Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Sin Ta Yi Rawar Gani A Fannin Bunkasa SCO

4 hours ago
CGTN Poll: Ba Da Kariya Shi Ne Tuna Baya—-Shekaru 80 Bayan Yakin Duniya Na II
Daga Birnin Sin

CGTN Poll: Ba Da Kariya Shi Ne Tuna Baya—-Shekaru 80 Bayan Yakin Duniya Na II

5 hours ago
Za A Watsa Shirin “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” a Manyan Kafofin Watsa Labarai Na Kasashen SCO
Daga Birnin Sin

Za A Watsa Shirin “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” a Manyan Kafofin Watsa Labarai Na Kasashen SCO

7 hours ago
Wani Rahoton Kasar Sin Ya Kalubalanci Halaccin Ayyukan Amurka Bisa Dogaro Da “’Yancin Zirga-zirga”
Daga Birnin Sin

Wani Rahoton Kasar Sin Ya Kalubalanci Halaccin Ayyukan Amurka Bisa Dogaro Da “’Yancin Zirga-zirga”

8 hours ago
Beijing Zai Bunkasa Amfani Da Fasahohin Zamani A Wuraren Adana Kayan Tarihi
Daga Birnin Sin

Beijing Zai Bunkasa Amfani Da Fasahohin Zamani A Wuraren Adana Kayan Tarihi

10 hours ago
Next Post
Jami’an Tsaro Sun Kai Samame A Sansanin Bayar Da Horo Na Kungiyar IPOB Sun Kashe 3

Jami'an Tsaro Sun Kai Samame A Sansanin Bayar Da Horo Na Kungiyar IPOB Sun Kashe 3

LABARAI MASU NASABA

An Yi Bikin Mu’ammalar Al’Adu Na SCO Na 2025 A Beijing

An Yi Bikin Mu’ammalar Al’Adu Na SCO Na 2025 A Beijing

August 25, 2025
Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Sin Ta Yi Rawar Gani A Fannin Bunkasa SCO

Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Sin Ta Yi Rawar Gani A Fannin Bunkasa SCO

August 25, 2025
CGTN Poll: Ba Da Kariya Shi Ne Tuna Baya—-Shekaru 80 Bayan Yakin Duniya Na II

CGTN Poll: Ba Da Kariya Shi Ne Tuna Baya—-Shekaru 80 Bayan Yakin Duniya Na II

August 25, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Yi Hasashen Ambaliyar Ruwa A Jihohin Arewa 15

Gwamnatin Tarayya Ta Sake Gargadin Jihohin Arewa 9 Kan Afkuwar Ambaliya 

August 25, 2025
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 3 Da Kubutar Da Mutum 16 Da Aka Sace A Kaduna

ECOWAS Za Ta Kaddamar Da Rundunar Yaki Da Ta’addanci Mai Jami’ai 260,000

August 25, 2025
Za A Watsa Shirin “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” a Manyan Kafofin Watsa Labarai Na Kasashen SCO

Za A Watsa Shirin “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” a Manyan Kafofin Watsa Labarai Na Kasashen SCO

August 25, 2025
Mauludi: Gwamnatin Kano Ta Sake Ɗage Ranar Komawa Makarantu

Zargin Babban Hadimin Gwamnan Kano Ya Karkatar Da Kuɗaɗen Jama’a Ba Gaskiya Ba Ne

August 25, 2025
Wani Rahoton Kasar Sin Ya Kalubalanci Halaccin Ayyukan Amurka Bisa Dogaro Da “’Yancin Zirga-zirga”

Wani Rahoton Kasar Sin Ya Kalubalanci Halaccin Ayyukan Amurka Bisa Dogaro Da “’Yancin Zirga-zirga”

August 25, 2025
Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya

Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya

August 25, 2025
Beijing Zai Bunkasa Amfani Da Fasahohin Zamani A Wuraren Adana Kayan Tarihi

Beijing Zai Bunkasa Amfani Da Fasahohin Zamani A Wuraren Adana Kayan Tarihi

August 25, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.