• English
  • Business News
Sunday, June 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yansanda Sun Kama Miyagun Kwayoyi Da Suka Kai Na Miliyan 600 A Kebbi

by Umar Faruk
2 years ago
in Labarai
0
‘Yansanda Sun Kama Miyagun Kwayoyi Da Suka Kai Na Miliyan 600 A Kebbi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Rundunar ‘yansandan Nijeriya reshen jihar Kebbi ta kama wasu manyan motoci guda biyu dauke da kwantena mai tsawon mita hudu zuwa hudu, mai dauke da lambobi T-21608 LA, T- 21520 LA duk lambar Legas da ke dauke da damtse na taba wiwi da ake zargin tabar wiwi ce a kan iyakar jihar Kebbi da Jamhuriyar Benin, a gundumar Maje- Tsamiya ta karamar hukumar Bagudo ta jihar.

Kakakin rundunar ‘yansandan jihar PPRO SP Nafi’u Abubakar, ya bayyana hakan a lokacin da ta kira taron ganawa da manema labarai a hedikwatar ‘yansanda a ranar Alhamis a Birnin Kebbi.

  • Gwamna Idris Ya Nada Dan Marigayi Sheikh Giro Mukami A Hukumar Alhazai Ta Kebbi

Ambaliyar Ruwan Sama Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutum 3 A Jihar Kebbi

Kakakin rundunar ya ce, jami’an hukumar ‘yansandan jihar Kebbi da ke aiki da rundunar jihar, sun kama motocin biyu ne a ranar 10 ga watan Satumba, 2023 a Maje-Tsamiya a karamar hukumar Bagudo ta jihar. Yana mai jaddada cewa bayan binciken manyan motocin guda biyu da ke shake da batar wiwi dauri 4,927, sai kuma harsasai masu rai 7,500 da kuma wasu fakiti 4,906 na damtse na bata wiwi duk an gano su a cikin motocin guda biyu.

Kazalika ya kara da bayyana cewa, motar ta farko an kama ta ne dauke da daurin bata wiwi guda 4,927 da aka damke wasu mutane uku, direta da wasu mutane biyu: Emmanuel Chukwuma na karamar hukumar Bende, jihar Abia, Kanta Bisa karamar hukumar Asaka, dan kasar Ghana da kuma Shola Adeyemi na karamar hukumar Olufan, karamar hukumar Akure, jihar Ondo duk a cikin mota daya ta taho daga Ghana zuwa Togo zuwa jamhuriyar Benin sannan ta wuce iyakar Nijeriya ta karamar hukumar Bagudo ta jihar Kebbi.

Labarai Masu Nasaba

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

Har ilayau, an kama motar ta biyu dauke da fakiti 7,500 na daurin bata wiwi da kuma harsashi 4,906 da kuma direban Abdulrazak Agboola na Unguwar Iyana-Ajiya a Ibadan, jihar OYO, amma wasu da ake zargin tare da shi yayin binciken motar sun tsere, amma rundunar ‘yansanda za ta gano su don tabbar da cewa an kama su nan ba da jimawa ba.

Ya kuma ce ana gudanar da bincike kan lamarin kuma nan ba da dadewa ba za a kama wasu jiga-jigan da suka gudu, bayan bincike rundunar za ta aiwatar da matakan da suka dace. Duk yawan na bata wiwi da aka kama tana Naira miliyan 600 a kiyasi.

A wata hira da ya yi da manema labarai, direban babbar motar ta farko, Emmanuel Chukwuma, ya ce ya dauki katan-katan abubuwan sha daga Legas zuwa Ghana a kan hanyarsa ta dawowa, an ba shi kwangilar daukar daurin bata wiwi guda 4,927 da zai kai garin Legas kan kudi Nair dubu dari hudu.

Ya kara da cewa an ba shi Naira dubu dari a matsayin kamun cinike, idan ya sauke kayan sai a biya shi sauran dubu dari, kuma daga Ghana zuwa iyakar Nijeriya ya wuce cikin nasara. Amma da ya isa kan iyakar Nijeriya inda ya ce na wuce wasu shingayen jami’an tsaro guda tara, amma na yi rashin sa’a tawagar ‘yan sandan da ke sintiri a kan iyaka suka tare motar suka mayar da ni maje-Tsamiya da ke karamar hukumar Bagudo inda suka yi bincike kan motar suka samu daurin bata wiwi shake da motar.

Ya ci gaba da cewa bayan haka an kama shi tare da wasu mutane biyu a cikin motar, daga nan aka dauke su zuwa babban ofishin bincike na SCID a hedikwatar ‘yansanda da ke Birnin Kebbi har da motar.

Hakazalika, direban manyan motoci na biyu, Abdulrazak Agboola daga Ibadan Oyo, ya bayyanawa manema labarai a rundunar ‘yansanda cewa, yana Ibadan ne aka kira shi ta wayar tarho daga jamhuriyar Benin cewa suna bukatar ya zo jamhuriyar Benin ya tuka babbar mota zuwa Akure, jihar Ondo akan kudi Naira dubu dari biyu amma bayan an sauke batar wiwi din, amma bai yi sa’a ba, inda aka kama shi da daurin bata wiwi guda 4,906 da kuma harsashin bindiga guda 7,500. Yanzu haka ina cikin ga hannun ‘yansanda, yayin da suke gudanar da bincike kan lamarin.

Ya ce mutanen da suka dauke ni kwangilar tuka mota sun gudu ne a lokacin da jami’an ‘yansandan da ke sintiri a kan iyakar, a yayin da suke binciken motar suka bar ni. Yanzu ina hannun ‘yansanda.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 'YansandaKebbi
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kwastam Ta Kama Fatun Jakuna Da Aka Yi Fasa Kwaurinsu A Jihar Adamawa

Next Post

Ya Kamata Tinubu Ya Nemi Shawarar Gowon, Babangida Da Jonathan Kan Hulda Da Waje – Shugaban Cibiyar Kasuwancin Nijeriya A Dubai

Related

‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi
Labarai

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

11 hours ago
Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote
Labarai

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

12 hours ago
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne
Ra'ayi Riga

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

13 hours ago
Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno
Labarai

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

17 hours ago
Kebbi
Rahotonni

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

18 hours ago
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023
Labarai

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

19 hours ago
Next Post
Tinubu

Ya Kamata Tinubu Ya Nemi Shawarar Gowon, Babangida Da Jonathan Kan Hulda Da Waje - Shugaban Cibiyar Kasuwancin Nijeriya A Dubai

LABARAI MASU NASABA

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

June 7, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

June 7, 2025
Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

June 7, 2025
Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

June 7, 2025
Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

June 7, 2025
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

June 7, 2025
Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

June 7, 2025
Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

June 7, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

June 7, 2025
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.