• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hanyoyi Hudu Na Samun Kudin Shiga A Kasuwancin Shanu

by Abubakar Abba
2 years ago
in Noma Da Kiwo
0
Shanu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hada-hadar kasauwancin shanu, na daya daga cikin kasuwanci mai riba da ake yi a Nijeriya. Akwai hanyoyi hudu da za a iya samun kudin shiga a sana’ar sayar da shanu baya ga kiwata su. Wadannan hanyoyi guda hudu su ne kamar haka:

Saye da sayar da Shanu:
Ana neman shanu kwarai da gaske a Nijeriya, ana kuma yanka su a kowace rana, musamman a lokacin gudanar da shagulgulan bukukuwa da kuma mayanka. Za a iya samun kudaden shiga masu yawan gaske ta hanyar tura shanu gonaki domin yi musu baye, ana kuma sayen shanu a Arewacin Nijeriya a kai su kudancin wannan kasa a sayar, a kuma samu riba mai tarin yawa.

Kazalika, idan ba a son kai su mayankar yanka dabbobi, za a iya yanka su a rika sayar da naman kilo-kilo ga masu saha’awar saya. Har ila yau kafin a sayo shanu, yana da kyau a gano kasuwar da ake sayar da su wadda ta dace, domin gujewa kashe kudi da yawa kafin a sayar da su.

Bugu da kari, za a iya tattaunawa da kungiyoyi da manyan kamfanoni wadanda ke bukatar saye, domin kai musu har inda suke su saya.

Kashin Shanu:
Wasu masana’antun na bukatar kashin shanu, domin sarrafa su zuwa abincin kajin gidan gona, musamman ganin yadda kashi ke dauke da sinadarin ‘calcium’, wanda kai tsaye ke gina jikin Kaji.

Labarai Masu Nasaba

Gwamna Zulum Ya Nemi A Zuba Hannun Jari A Harkar Noman Rani

Gwamnatin Jihar Gombe Ta Rattaba Hannu Kan Yarjejeniya Domin Gina Mayankar Dabbobi

Ana samun kashin shanu a mayankar dabbobi, sannan ana shanya su ne su bushe, kamin a kai ga sayar wa manyan masana’antun da ke sarrafa shi zuwa abincin Kaji.

Haka zalika, za a iya nika kashin shanu a mayar da shi zuwa kilo 50, domin fitar da shi zuwa wasu jihohi ko sauran kasashen ketare a sayar.

Fatar Shanu:
A Nijeriya, ana yi wa fatar shanu lakabi da “Pomo”, wadda wasu ke ci a matsayin nama. Ana kuma yin amfani da fatar shanun wajen sarrafa ta a yi takalma, jakunkuna da sauran makamantansu.

Biyo bayan haramta cin fatar shanu da ake kira da Ganda “Pomo”, hakan ya kara sanya matukar bukatar ta a tsakanin masana’antun da ke sarrafa ta, musamman zuwa wasu nau’ika daban-daban a wannan kasa. Kazalika, ana sarrafa wannan fata ta shanu a kuma fitar da ita zuwa Nahiyar Turai da sauran yankin Asiya.

Kahon Shanu:
Za a iya samun dalolin kudi yayin fitar da kahon shanu zuwa kasashen waje, ana kuma son a tabbatar da kauce wa rubewarsa da kare shi daga wasu ababen da za su iya janyo wa ya rube a jikinsa kafin a sayar wa da masu bukatar sa. sannan, ana sarrafa shi zuwa wasu nau’ikan kaya da suka hada da kofuna, cokula, sarkoki, tebura da sauransu. Kazalika, hada-hadar kasuwancin kahon shanu a Nijeriya, na ci gaba kara fadada da kuma samun tagomashi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: NomaShanu
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ina Ne Damar Kasuwa Ta Gaba? Sun Ce Har Yanzu Tana A Sin

Next Post

Sabuwar Masara Ta Karya Farashin Tsohuwa A Kasuwar Filato 

Related

Gwamna Zulum Ya Nemi A Zuba Hannun Jari A Harkar Noman Rani
Noma Da Kiwo

Gwamna Zulum Ya Nemi A Zuba Hannun Jari A Harkar Noman Rani

7 days ago
Gwamnonin Arewa Na Kokarin Farfado Da Hadin Kan Yankin
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Jihar Gombe Ta Rattaba Hannu Kan Yarjejeniya Domin Gina Mayankar Dabbobi

7 days ago
Rashin Daukar Tsauraran Matakai Na Iya Durkusar Da Bangaren Noma – Shehu Galadima
Noma Da Kiwo

Nau’ikan Amfanin Gona Da Ke Saurin Girma Cikin ‘Yan Watanni

7 days ago
Rashin Daukar Tsauraran Matakai Na Iya Durkusar Da Bangaren Noma – Shehu Galadima
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Ta Bukaci A Sama Wa Manoma Masu Renon Tsirrai Rancen Kudi

2 weeks ago
Hikimar Gwamnatin Tarayya Ta Zuba Dala Biliyan 74 A Fannin Kiwon Dabbobi
Noma Da Kiwo

Hikimar Gwamnatin Tarayya Ta Zuba Dala Biliyan 74 A Fannin Kiwon Dabbobi

2 weeks ago
Tinubu Ya Kira Taron Manyan Kafafen Yada Labarai Kan Samar Da Wadataccen Abinci
Noma Da Kiwo

Tinubu Ya Kira Taron Manyan Kafafen Yada Labarai Kan Samar Da Wadataccen Abinci

3 weeks ago
Next Post
Masara

Sabuwar Masara Ta Karya Farashin Tsohuwa A Kasuwar Filato 

LABARAI MASU NASABA

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

June 6, 2025
Daurarru

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

June 6, 2025
Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

June 6, 2025
Wutar lantarki

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

June 6, 2025
Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

June 6, 2025
Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

June 6, 2025
Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

June 6, 2025
An Kama Wadanda Ake Zargi Da Kai Wa Shugaban Kwadago Hari Ribadu

Ribadu Ya Kara Jaddada Gargadinsa Kan Biyan Kudin Fansa Ga Masu Garkuwa Da Mutane

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.