• English
  • Business News
Sunday, June 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ba A Yabon Dan Kuturu…

by CGTN Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Ba A Yabon Dan Kuturu…
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A wannan mako ne, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya fadawa shugaban masu rinjaye na majalisar dattawan kasar Amurka Chuck Schumer, wanda ya jagoranci wata tawagar ’yan majalisar dokokin Amurka don kawo ziyara kasar Sin cewa, a wannan duniya mai cike da sauye-sauye da rudani, yadda kasashen Sin da Amurka za su daidaita, shi ne zai iya tabbatar da makomar bil Adama.

Shugaba Xi ya ce, a matsayinsu na manyan kasashe biyu, ya kamata Sin da Amurka su nuna himma, da hangen nesa, da kaiwa ga matsayin da kasashen duniya ke fata, da kokarin inganta jin dadin jama’arsu, da ingiza ci gaban bil Adama.

  • Sakamako Da Aka Samu Bayan Gina Shawarar Ziri Daya Da Hanya Daya
  • Daliban Cibiyar Koyar Da Ilmin Sana’a Ta Luban Dake Djibouti

Bugu da kari, yayin da duniya da ma zamani ke sauyawa, har yanzu tunanin tarihi na zaman lafiya tsakanin kasashen Sin da Amurka bai sauya ba, haka kuma babban burin jama’arsu na yin mu’amala da yin hadin gwiwa bai canja ba, kana fatan da kasashen duniya ke yi na samun kwanciyar hankali da bunkasuwar dangantakar dake tsakanin Sin da Amurka bai sauya ba.

Ya kuma bukaci bangarorin biyu da su mutunta juna, su zauna tare cikin lumana, da yin hadin gwiwa domin samun nasara tare. Manufar kasashen 2 dai ita ce, su daidaita da kuma kyautata alakarsu, da samar da hanyar da ta dace don yin cudanya da juna a sabon zamani na tarihi.

A nasa bangare Schumer ya gabatar da ra’ayoyin da suka dace na bangaren Amurka, ya kuma bayyana aniyar karfafa tuntuba da tattaunawa da kasar Sin bisa gaskiya da mutunta juna, da kuma lura da bambance-bambance dake tsakaninsu bil hakki da gaskiya da kaucewa tayar da rikice-rikice, kuma Amurka ba za ta raba gari da Sin ba.

Labarai Masu Nasaba

Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

Haka ma yayin ziyarar da sakatariyar baitul malin Amurka Janet Yellen ta kawo kasar Sin ta bayyana aniyarta ta kara yaukaka alaka, da cudanya da hadin gwiwa, da mutunta juna tsakanin kasashen biyu. Amma da komarwa Amurka sai aka ji ta tana furta wasu manufofin Amurka da ba su dace ba kan kasar Sin., ta hanyar fakewa da batun tsaron kasa.

Wannan dai ba shi ne karon farko da ake jin kasashen biyu na furta irin wadannan kalamai ba, amma daga karshe sai a wayi gari Amurka ta sa kafa ta yi fatali da abin da ta furta ko aka cimma, matakin dake sake mayar da hannun agogon baya a hadin gwiwar kasashen dake zama mafiya karfin tattalin arziki a duniya.

Idan ba a manta ba, ko shi ma sakataren harkokin wajen Amurka Anthony Blinken yayin da ya kawo makamanciyar wannan ziyara kasar Sin a wannan shekara, ya furta irin wadannan kalamai na karfafa alaka da mutunta alkawuran da aka cimma, amma bayan komawarsa gida, sai aka ji shi yana furta wasu kalamai marasa dacewa game da alakar sassan biyu.

Masu fashin baki dai na cewa, ya dace Amurka ta rika nuna sanin ya kamata ta kuma cika alkawuran da ta yi, tare da daina neman bata sunan kasar Sin ko kakaba mata takunkuman da ko kadan ba su dace ba. Don haka, a wannan karon ma, ba za a yi saurin gaskata kalaman jagoran tawagar ’yan majalisun dokokin na Amurka ba. Masu iya magana na cewa, ba a yabon dan kuturu, sai ya shekara da dan yatsa.

Duniya dai ta zuba ido tare da fatan gwamnatin Amurka, za ta dauki hakikanin matakai domin ciyar da huldarta da Sin gaba yadda ya kamata, wadda ke da muhimmanci ba ma ga kasashen biyu ba, har ma ga duniya baki daya. (Ibrahim Yaya)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

‘Yansanda Sun Cafke Mutum 3 Bisa Zargin Fashi Da Makami A Jihar Kano

Next Post

Wanda Ya Shuka Zamba, Shi Zai Yi Girbinta

Related

Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

6 hours ago
An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin
Daga Birnin Sin

An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

7 hours ago
Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana
Daga Birnin Sin

Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

8 hours ago
Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa
Daga Birnin Sin

Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

9 hours ago
An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata
Daga Birnin Sin

An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata

10 hours ago
Sin Na Kokarin Gaggauta Taimakawa Kasashen Afirka Da Kara Hadin Gwiwa Da Su
Daga Birnin Sin

Sin Na Kokarin Gaggauta Taimakawa Kasashen Afirka Da Kara Hadin Gwiwa Da Su

1 day ago
Next Post
Wanda Ya Shuka Zamba, Shi Zai Yi Girbinta

Wanda Ya Shuka Zamba, Shi Zai Yi Girbinta

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

June 28, 2025
An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

June 28, 2025
Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

June 28, 2025
Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

June 28, 2025
Bashin Da Ake Bin Nijeriya Ya Kai Tiriliyan 46.25

Za A Ci Gaba Da Tunawa Da Aminu Ɗantata A Ɓangaren Taimakon Jama’a — Buhari

June 28, 2025
Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

June 28, 2025
Hukumar NPA Na Son Tara Kuɗaɗen Shiga Naira Tiriliyan 1.2 A 2025

Hukumar NPA Na Son Tara Kuɗaɗen Shiga Naira Tiriliyan 1.2 A 2025

June 28, 2025
An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata

An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata

June 28, 2025
Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

June 28, 2025
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe

Rasuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Afirka – Atiku

June 28, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.