• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ranar Yaki Da Talauci Ta Duniya: Sama Da Mutum Biliyan Daya Na Fama Da Talauci – Sakataren MDD

by Sulaiman
2 years ago
in Labarai
0
Ranar Yaki Da Talauci Ta Duniya: Sama Da Mutum Biliyan Daya Na Fama Da Talauci – Sakataren MDD
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Babban sakataren majalisar dinkin duniya MDD, Antonio Gutteres, acikin jawabinsa na ranar kawar da talauci ta Duniya, ya yi ikirarin cewa, a wannan duniyar ta mu mai cike da dimbin arziki, bai kamata Talauci ya yi ma ta katutu ba.

Gutteres ya ce, duk da dimbin arzikin cikin duniyarmu amma kusan mutane miliyan 700 ke fama da kalubalen rayuwa, inda suke rayuwa a kasa da dala 2.15 daidai da naira N2,000 a duk rana.

  • Ranar Abinci Ta Duniya: Gwamnatin Kaduna Za Ta Samar Da Tsaftataccen Ruwa Da Abinci Mai Gina Jiki
  • Gwamna Uba Sani Ya Nada Dakta Mayere Sabon Sakataren Gwamnatin Jihar Kaduna

Sama da mutane biliyan daya ne ke fama da matsananciyar rayuwa daga karancin abinci, ruwa, lafiya da ilimi.

Akwai biliyoyin mutanebda ba su da tsaftataccen muhalli, ayyukan yi, wurin kwana ballanta kuma samun ‘yancin zamantakewa.

A halin yanzu, duniyarmu tana fama da rikice-rikicen yaki, rikicin wariya na kara kamari – musamman kan mata da ‘yan mata.

Labarai Masu Nasaba

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

Duk abubuwan da suka janyo koma baya ga ci gaban mu da tsanancin talauci, na da alaka da tsarin tafiyar da harkokin kudi na duniya wanda ya tsufa da kuma rashin adalci wanda ke hana kasashe masu tasowa tallafawa don kawar da talauci da cimma manufar shirin ‘yancin zamantakewa da kawar da talauci na MDD (SDGs).

Kusan mutane miliyan 500 ne za su kasance cikin matsanancin talauci acikin 2030. Wannan, sam ba a abin da za a sa ido ana kallo ba ne kawai, dole a yi wani abu.

A taron koli na SDG da aka yi a watan Satumba, shugabannin kasashen duniya sun amince da bukatar yin garambawul ga tsarin hada-hadar kudi na kasa da kasa, tare da himmatuwa wajen yin wani kwakkwaran shiri don ceto muradun ci gaba mai dorewa da kuma kara kaimi wajen kawar da talauci a ko’ina.

Wannan ya hada da bayar da tallafi don karfafa shirin SDG na akalla dala biliyan 500 a kowace shekara.

Shugabannin sun kuma amince da matakin da aka dauka da niyyar kawar da talauci da wahalhalun rayuwa ga dukkan mutane – daga tsarin samar da abinci da ilimi zuwa ayyukan yi masu nagarta da fadada kariyar zamantakewa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Antonio GutteresMDDUN
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ranar Abinci Ta Duniya: Mata Manoma Zasu Samu Tallafin Aikin Gona A Zamfara

Next Post

Yadda Yaki Da Hamada Ke Samar Da Kudin Shiga A Jihar Xinjiang

Related

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno
Labarai

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

1 hour ago
Talauci
Rahotonni

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

2 hours ago
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023
Labarai

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

3 hours ago
Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya
Manyan Labarai

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

6 hours ago
2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC
Labarai

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

9 hours ago
Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi
Labarai

Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

9 hours ago
Next Post
Yadda Yaki Da Hamada Ke Samar Da Kudin Shiga A Jihar Xinjiang

Yadda Yaki Da Hamada Ke Samar Da Kudin Shiga A Jihar Xinjiang

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

June 7, 2025
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

June 7, 2025
Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

June 7, 2025
Talauci

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

June 7, 2025
Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

June 7, 2025
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

June 7, 2025
Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

June 7, 2025
Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

June 7, 2025
Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.