• English
  • Business News
Tuesday, November 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kotu Ta Daure Dillalin Tabar Wiwi Shekara 10 A Kano

by Khalid Idris Doya
2 years ago
Kotu

Babbar kotun tarayya da ke zamanta a jihar Kano karkashin jagorancin S.A. Amobeda, ta yanke hukuncin zaman gidan yari na tsawon shekara 10 ga wani dillalin tabar wiwi, Muhammad Bako Sambo. 

Sambo na daga cikin masu safarar miyagun kwayoyi guda bakwai da hukumar hana sha da fataucin miyagun kwayoyi (NDLEA) a jihar Kano ta gurfanar da su a watan Oktoba.

  • Najeriya Ta Yi Imanin Shawarar BRI Za Ta Inganta Ci Gaban Kasashen Afirka
  • Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Da Su Agazawa Bunkasuwar Afirka

A wata sanarwa da kakakin hukumar, Sadiq Muhammad Maigatari, ya raba ga ‘yan jarida a Kano jiya, inda ya nuna cewa an samu Sambo da laifi kuma an yanke masa hukuncin shekara 10 a gidan gyaran hali.

Sadiq, ya ce an samu nasarar daure mai laifin ne bisa kokarin kwamandan hukumar, Abubakar Idris Ahmad.

Sadiq, ya kara da cewa NDLEA ta tashi tsaye wajen yin aiki tukuru domin dakile dukkanin ayyukan safara da shan miyagun kwayoyi, ya kara da cewa, samun nasarar daure dilar kwayoyin wata alamar nasara ce da ke nuni da cewa masu yunkurin safarar tabar wiwi su sani Kano ba wurin cin burinsu ba ne.

LABARAI MASU NASABA

China Ta Gargaɗi Amurka Kan Tsoma Baki A Harkokin Nijeriya

Atiku Ya Fice Daga PDP Saboda Na Ƙi Bari Ya Lalata Mana Jam’iyya – Wike

“Sambo, wanda ya kasance mai safarar tabar wiwi daga Ondo da wasu jihohin kudancin Nijeriya zuwa wasu jihohin arewacin Nijeriya, ya fada hannu ne a ranar 11 ga watan Nuwamban 2020.

“Jami’an NDLEA da ke aikin sintiri a kan hanyar Kano zuwa Zariya ne suka kama shi a lokacin da suka ga wata mota kirar Honda da suke zarginta, an cafke wanda ake zargin ne a Hotoro da ke Kano.

“Da aka kaddamar da bincike an gano cewa Sambo ya dauko wiwi mai nauyin kilogiram 201 a motarsa. Kuma asalinsa mazaunin Lokogoma da ke Abuja.”

Sanarwar ta kara da cewa kotun ta daure Sambo ne bayan gwajin da aka yi kan tabar wiwin.

Ya kara da cewa, kwamandan hukumar Ahmad ya jinjina wa kokarin tawagar jami’ansu bisa kokarinsu wajen yaki da safarar miyagun kwayoyi da nasarar da suka samu a kotun.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

China Ta Gargaɗi Amurka Kan Tsoma Baki A Harkokin Nijeriya
Manyan Labarai

China Ta Gargaɗi Amurka Kan Tsoma Baki A Harkokin Nijeriya

November 4, 2025
2023: Me Ya Sa Ake Rububin Wike?
Manyan Labarai

Atiku Ya Fice Daga PDP Saboda Na Ƙi Bari Ya Lalata Mana Jam’iyya – Wike

November 4, 2025
Kalaman Trump A Kan Nijeriya Abun Damuwa Ne – Peter Obi 
Manyan Labarai

Kalaman Trump A Kan Nijeriya Abun Damuwa Ne – Peter Obi 

November 4, 2025
Next Post
Majalisar Wakilai Za Ta Amince Da Kasafin Kudin 2024 Kafin Karshen Disamba

Majalisar Wakilai Za Ta Amince Da Kasafin Kudin 2024 Kafin Karshen Disamba

LABARAI MASU NASABA

China Ta Gargaɗi Amurka Kan Tsoma Baki A Harkokin Nijeriya

China Ta Gargaɗi Amurka Kan Tsoma Baki A Harkokin Nijeriya

November 4, 2025
2023: Me Ya Sa Ake Rububin Wike?

Atiku Ya Fice Daga PDP Saboda Na Ƙi Bari Ya Lalata Mana Jam’iyya – Wike

November 4, 2025
Dalilin Da Ya Sa Sanatoci Ba Su Goyi Bayana Ba Lokacin Da Aka Dakatar Da Ni – Natasha

Dalilin Da Ya Sa Sanatoci Ba Su Goyi Bayana Ba Lokacin Da Aka Dakatar Da Ni – Natasha

November 4, 2025
Kalaman Trump A Kan Nijeriya Abun Damuwa Ne – Peter Obi 

Kalaman Trump A Kan Nijeriya Abun Damuwa Ne – Peter Obi 

November 4, 2025
Jami’an Tsaro Sun Dawo Da Fasfo Ɗin Sanata Natasha Bayan Ƙwace Shi A Abuja

Natasha Ta Zargi Akpabio Da Sanya Jami’an Tsaro Su Ƙwace Mata Fasfo A Filin Jirgin Saman Abuja 

November 4, 2025
Masu Kashe Mutane A Kudu Maso Gabas Kiristoci Ne – Soludo

Masu Kashe Mutane A Kudu Maso Gabas Kiristoci Ne – Soludo

November 4, 2025
Ribadu Ya Gana Da Hafsoshin Tsaro Biyo Bayan Kalaman Trump 

Ribadu Ya Gana Da Hafsoshin Tsaro Biyo Bayan Kalaman Trump 

November 4, 2025
Sarkin Kasar Spaniya Zai Kawo Ziyara Kasar Sin

Sarkin Kasar Spaniya Zai Kawo Ziyara Kasar Sin

November 3, 2025
Sin Ta Yi Watsi Da Zargin Trump Dangane Da Gwajin Nukiliya A Asirce

Sin Ta Yi Watsi Da Zargin Trump Dangane Da Gwajin Nukiliya A Asirce

November 3, 2025
An Bude Taron Kasuwanci Na Duniya Na 18 A Macau

An Bude Taron Kasuwanci Na Duniya Na 18 A Macau

November 3, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.