• English
  • Business News
Thursday, May 22, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Akwai ‘Yancin Tofa Albarkacin Baki A Gwamnatin Tinubu – Minista

by Sulaiman
2 years ago
in Labarai
0
Minista
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ministan Yaɗa Labarai Da Wayar Da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya bayyana cewa Gwamnatin Tarayya ba za ta shigo da dokokin hana ‘yan jarida da sauran jama’ar Nijeriya fadin albarkacin bakin su ba.

Sai dai kuma ya ce, ya kamata mutane su sani cewa, “‘yancin faɗin albarkacin baki ya na tattare da haƙƙin sanin ya-kamata da ya rataya a wuyan kowa.”

  • Za A Kammala Aikin Bututun Iskar Gas Na AKK A Disambar 2024 – NNPC
  • Shari’un Zabe: A Kauce Wa Tarzoma Duk Yadda Ta Kaya

Ministan ya bayyana hakan ne a lokacin da ya fito a karon farko aka tattauna da shi a shirin “Newsnight” na gidan talabijin na ARISE a Abuja a daren Asabar, inda ya amsa tambayoyi dangane da ƙudirorin wannan gwamnatin kan harkar yaɗa labarai da shirin wayar da kan al’umma da kuma burukan ‘yan Nijeriya.

Idris ya bayyana cewa, ya shafe makwanni takwas da su ka gabata yana nazari kan ayyukan ita kan ta Ma’aikatar Yaɗa Labarai Da Wayar Da Kai ta Tarayya, tare da tattaunawa da Sassa da Hukumomin ma’aikatar daban-daban.

Ya ce: “Mun san abin da mu ke so ta zama, amma tilas ne mu fara da fahimtar inda ta ke a yanzu, da kuma dalilin da ya sa ba ta kai inda mu ke buƙata ta kai ba.”

Labarai Masu Nasaba

‘Yan PDP Na Komawa APC Ne Saboda Jam’iyyarsu Na Jin ƙamshin Mutuwa – Ganduje

Za Mu Riƙe Wa Minista Tijjani Muƙaminsa Bayan Hamɓarar Da Tinubu A 2027 – El-Rufai 

A kan batun aikin wayar da kan jama’a, ya ce, aiki ne da ke cikin alhakin da aka ɗora masa a matsayin sa na minista.

Ya ce, “Mutane su na rage yarda da gwamnati, don haka ya kamata mu tambayi kan mu, ina ne ba mu yi daidai ba? Me ya sa ‘yan Nijeriya ba su amince da Nijeriyar ba? Za mu fito da wani tsari na yadda za mu sake fahimtar ko mu su wanene kuma mu fara komawa mu amince da Nijeriya.

Da ya ke magana kan irin ƙasar da ‘yan Nijeriya su ke so su samu, sai ya ce, “Domin amsa wannan tambaya, mu na buƙatar tattaunawa a duk faɗin ƙasar nan kan irin ƙasar da mu ke muradin mu ga mun samu. Me ya sa yanzu a makarantu aka daina wajabta karanta Haƙƙin Ɗan Ƙasa, wato ‘Civics’? Wanene ɗan asalin Nijeriya? Shin mun san haka? Akwai buƙatar mu dawo da sanin kyawawan ɗabi’u da aka san mu da su.

Bugu da ƙari, ya yi tsokaci kan irin ‘yancin da jama’ar Nijeriya su ke da shi, ya ce, “Kafafen yaɗa labarai na Nijeriya su na da ‘yanci, kuma shi Shugaba Tinubu so ya ke ma ya ƙara musu ‘yanci. Yaɗa labarai ya na da muhimmanci wajen samun nasarar kowace gwamnati. Mai girma Shugaban Ƙasa ya na ƙoƙarin faɗin magana a yadda ta ke ba tare da wata ƙumbiya-ƙumbiya ba.

 

“Batun yaɗa labaran ƙirƙira da na ƙarya ba matsala ba ce ga Nijeriya ita kaɗai, matsala ce da ta shafi duniya baki ɗaya. Mun ga yadda yaɗa labaran ƙarya ya jawo a Amurka, wanda ya jawo harin ranar 6 ga Janairu da aka kai ainihin cibiyar dimokiraɗiyyar Amurka. Tilas ne mu tunkari matsalar yaɗa labaran ƙarya a duk duniya.

“Bari in ƙara maimaita cewa: Gwamnatin mu ba za ta ƙaƙaba wa kafafen yaɗa labarai ko sauran ‘yan Nijeriya takunkumi ba, ko ta yi wa ‘yancin ‘yan jarida zagon ƙasa. Sai dai kuma ya kamata a sani cewa, kowane ‘yanci ya na tattare ne da buƙatar mutum ya san alhakin da ke kan sa. ‘Yancin tofa albarkacin baki ya na tattare da sanin ya kamata.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 'Yan JaridaGwamnatin TinubuLabaran Karya
ShareTweetSendShare
Previous Post

Shawarar Ziri Daya Da Hanya Daya Ta Amfanawa Al’ummar Nijeriya

Next Post

’Yan Sama Jannatin Kumbon Shenzhou-16 Za Su Dawo Duniya Bayan Gama Mika Aikinsu 

Related

Ganduje Ya Zargi Gwamna Yusuf Da Ɗaukar Nauyin Zanga-zanga A Kano
Labarai

‘Yan PDP Na Komawa APC Ne Saboda Jam’iyyarsu Na Jin ƙamshin Mutuwa – Ganduje

2 hours ago
Za Mu Riƙe Wa Minista Tijjani Muƙaminsa Bayan Hamɓarar Da Tinubu A 2027 – El-Rufai 
Labarai

Za Mu Riƙe Wa Minista Tijjani Muƙaminsa Bayan Hamɓarar Da Tinubu A 2027 – El-Rufai 

4 hours ago
Ƙungiyar ’yan Majalisar Dokokin Ƙasa Ta APC Ta Amince Da Takarar Tinubu A Zaɓen 2027 
Manyan Labarai

Ƙungiyar ’yan Majalisar Dokokin Ƙasa Ta APC Ta Amince Da Takarar Tinubu A Zaɓen 2027 

5 hours ago
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023
Labarai

INEC Ta Samar Da Sashen Ƙirƙirarriyar Basira Domin Inganta Harkokin Zaɓe 

7 hours ago
Ingancin Tattalin Arzikin Sin Mai Bude Kofa Na Bayyana Sosai Duba Da Yawan Zuwan Baki Masu Sayayya
Ra'ayi Riga

Ingancin Tattalin Arzikin Sin Mai Bude Kofa Na Bayyana Sosai Duba Da Yawan Zuwan Baki Masu Sayayya

8 hours ago
Sanata Adamu Aliero Ya Ƙaddamar Da Rabon Kayan Tallafi Ga Ƙananan Hukumomi Takwas A Kebbi
Labarai

Sanata Adamu Aliero Ya Ƙaddamar Da Rabon Kayan Tallafi Ga Ƙananan Hukumomi Takwas A Kebbi

8 hours ago
Next Post
Shenzhou-16

’Yan Sama Jannatin Kumbon Shenzhou-16 Za Su Dawo Duniya Bayan Gama Mika Aikinsu 

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Sama Jannatin Shenzhou-20 Sun Kammala Aiki A Wajen Tashar Sararin Samaniyar Kasar Sin

‘Yan Sama Jannatin Shenzhou-20 Sun Kammala Aiki A Wajen Tashar Sararin Samaniyar Kasar Sin

May 22, 2025
Ba Zai Yiwu Amurka Ta Kafawa Chips Kirar Kasar Sin Wani Shinge Ba

Ba Zai Yiwu Amurka Ta Kafawa Chips Kirar Kasar Sin Wani Shinge Ba

May 22, 2025
Ganduje Ya Zargi Gwamna Yusuf Da Ɗaukar Nauyin Zanga-zanga A Kano

‘Yan PDP Na Komawa APC Ne Saboda Jam’iyyarsu Na Jin ƙamshin Mutuwa – Ganduje

May 22, 2025
Masanan Najeriya Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwar Afirka Da Sin A Fannin Tinkarar Kalubalen Harajin Kwastam Na Amurka

Masanan Najeriya Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwar Afirka Da Sin A Fannin Tinkarar Kalubalen Harajin Kwastam Na Amurka

May 22, 2025
Modric Zai Bar Real Madrid Bayan Kammala Gasar Cin Kofin Duniya Na Kungiyoyi

Modric Zai Bar Real Madrid Bayan Kammala Gasar Cin Kofin Duniya Na Kungiyoyi

May 22, 2025
Yawan Wutar Lantarkin Da Sin Ke Iya Samar Ta Amfani Da Karfin Ruwa Ta Kai Matsayin Koli A Duniya

Yawan Wutar Lantarkin Da Sin Ke Iya Samar Ta Amfani Da Karfin Ruwa Ta Kai Matsayin Koli A Duniya

May 22, 2025
Za Mu Riƙe Wa Minista Tijjani Muƙaminsa Bayan Hamɓarar Da Tinubu A 2027 – El-Rufai 

Za Mu Riƙe Wa Minista Tijjani Muƙaminsa Bayan Hamɓarar Da Tinubu A 2027 – El-Rufai 

May 22, 2025
Darussan Koyi Daga Salon Bunkasa Kasa Na Sin

Darussan Koyi Daga Salon Bunkasa Kasa Na Sin

May 22, 2025
Ƙungiyar ’yan Majalisar Dokokin Ƙasa Ta APC Ta Amince Da Takarar Tinubu A Zaɓen 2027 

Ƙungiyar ’yan Majalisar Dokokin Ƙasa Ta APC Ta Amince Da Takarar Tinubu A Zaɓen 2027 

May 22, 2025
Xi Jinping Ya Tattauna Da Shugaban Faransa

Xi Jinping Ya Tattauna Da Shugaban Faransa

May 22, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.