• English
  • Business News
Monday, November 10, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne

by CMG Hausa
2 years ago
san francisco

Shugaban kasar Sin Xi Jinping da takwaransa na Amurka Joe Biden, sun yi musayar ra’ayoyi mai zurfi, a rukunin gidajen alfarma na Filoli dake birnin San Francisco na kasar Amurka ranar Laraba. Taron kolin da aka dade ana jira, na zuwa ne shekara guda bayan ganawar shugabannin biyu a tsibirin Bali na kasar Indonesia.

A jawabinsa yayin ganawar shugaba Xi ya jaddada cewa, kasar Sin ta dukufa wajen samun daidaito, da dorewar dangantakar lumana da kasar Amurka. A lokaci guda kuma, kasar Sin tana da moriya da ka’idojin da suka kamata a kiyaye, da jan layin da ba za a iya ketarewa ba.

Kasar Sin na fatan kasashen biyu za su kasance abokan hulda masu mutunta juna da zaman tare cikin lumana. Taron dai ya kasance wani muhimmin zabi mai muhimmanci ga kasar Sin, don daidaita dangantakar dake tsakanin kasashen biyu, da kuma halin da ake ciki a duniya.
Masanin tattalin arziki na kasar Amurka Jeffrey Sachs ya shaidawa kamfanin dillancin labarai na Xinhua cewa, ra’ayin mutunta juna, da yin hadin gwiwa,da tattaunawa, da warware matsaloli tare, akwai “hikima sosai”, a cikinsa kuma yana da matukar muhimmanci.

Yana mai cewa, hadin gwiwar Sin da Amurka ba wai kawai kan muradun bai daya ne na kasashen biyu ba, yana kuma nuni da wani nauyi da ya rataya a wuyan kasashen duniya. A yayin taron, shugaba Xi ya yi kira ga kasashen biyu, da su hada kai a matsayinsu na manyan kasashe, yana mai jaddada cewa, za a iya magance matsalolin da ke addabar bil-Adama ne kawai ta hanyar hadin gwiwa tsakanin manyan kasashe.

Yarjejeniyar da aka cimma a yayin taron na San Francisco, ta nuna cewa, kasashen biyu suna da moriyar bai daya, kuma za su iya yin hadin gwiwa don samun sakamako mai tarin yawa. Dangantakar Sin da Amurka mai dorewa ba tunanin fata ba ne. Don haka, ya bukaci kasashen biyu su yi aiki tare.

LABARAI MASU NASABA

NBA Ta Yi Allah Wadai Da Yadda Hukuncin Alƙalai Ke Karo Da Juna

Mataimakin Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kebbi Bagudo Ya Shaƙi Iskar ‘Yanci Daga ‘Yan Bindiga

Kuma tattaunawa shi ne mataki na farko na amincewa da juna, da mutunta juna da kuma hada kai. Daga Bali zuwa San Francisco, babban jirgin ruwa na hadin gwiwar kasashen Sin da Amurka, ya yi tattaki ta cikin duwatsun teku da kadawar igiyar ruwa. Amma ba a San Francisco za a tsaya ba. Birnin, wanda ya shaida tarihin musanya tsakanin Sinawa da Amurkawa na tsawon karni, wani sabon mafari ne na dangantakar kasashen Sin da Amurka. (Ibrahim)

 

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

NBA Ta Yi Allah Wadai Da Yadda Hukuncin Alƙalai Ke Karo Da Juna
Labarai

NBA Ta Yi Allah Wadai Da Yadda Hukuncin Alƙalai Ke Karo Da Juna

November 9, 2025
Mataimakin Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kebbi Bagudo Ya Shaƙi Iskar ‘Yanci Daga ‘Yan Bindiga
Labarai

Mataimakin Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kebbi Bagudo Ya Shaƙi Iskar ‘Yanci Daga ‘Yan Bindiga

November 9, 2025
Soludo Ya Sake Lashe Zaɓen Gwamnan Anambra
Labarai

Soludo Ya Sake Lashe Zaɓen Gwamnan Anambra

November 9, 2025
Next Post
Gaza

Sakamakon Taron Kasashen Musulmi Da Larabawa: Saudiyya Da Nijeriya Za Su Jagoranci 'Yantar Da Falasdin

LABARAI MASU NASABA

Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Na Ci Gaba Da Zama Muhimmin Ginshiki Ga Ci Gaban Nahiyar 

Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Na Ci Gaba Da Zama Muhimmin Ginshiki Ga Ci Gaban Nahiyar 

November 9, 2025
An Rufe Taron Kolin Wuzhen Na Ayyukan Yanar Gizo Na Duniya Na Shekarar 2025

An Rufe Taron Kolin Wuzhen Na Ayyukan Yanar Gizo Na Duniya Na Shekarar 2025

November 9, 2025
Katsina United Ta Shiga Komar Hukuncin Hukumar NPFL

Katsina United Ta Shiga Komar Hukuncin Hukumar NPFL

November 9, 2025
Xi Ya Gana Da Shugabar IOC Tare Da Shugaban IOC Na Karramawa

Xi Ya Gana Da Shugabar IOC Tare Da Shugaban IOC Na Karramawa

November 9, 2025
CMG Ya Cimma Yarjejeniyar Samun Iznin Watsa Shirye-shiryen Wasannin Olympics Daga Shekarar 2026 Zuwa 2032

CMG Ya Cimma Yarjejeniyar Samun Iznin Watsa Shirye-shiryen Wasannin Olympics Daga Shekarar 2026 Zuwa 2032

November 9, 2025
Kasar Sin Ta Yi Nasarar Harba Sabbin Taurarin Dan Adam Na Gwaji

Kasar Sin Ta Yi Nasarar Harba Sabbin Taurarin Dan Adam Na Gwaji

November 9, 2025
Shugaba Xi Ya Ayyana Bude Gasar Wasanni Ta Kasa Karo Na 15

Shugaba Xi Ya Ayyana Bude Gasar Wasanni Ta Kasa Karo Na 15

November 9, 2025
Mizanin Farashin Kayan Masarufi Na Kasar Sin Ya Karu Da 0.2% A Watan Oktoba

Mizanin Farashin Kayan Masarufi Na Kasar Sin Ya Karu Da 0.2% A Watan Oktoba

November 9, 2025
Me Ke Haddasa Yawaitar Farmakar Ƴan Wasa A Gasar Firimiyar Nijeriya

Me Ke Haddasa Yawaitar Farmakar Ƴan Wasa A Gasar Firimiyar Nijeriya

November 9, 2025
NBA Ta Yi Allah Wadai Da Yadda Hukuncin Alƙalai Ke Karo Da Juna

NBA Ta Yi Allah Wadai Da Yadda Hukuncin Alƙalai Ke Karo Da Juna

November 9, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.