• English
  • Business News
Saturday, June 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne

by CMG Hausa
2 years ago
in Labarai
0
San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban kasar Sin Xi Jinping da takwaransa na Amurka Joe Biden, sun yi musayar ra’ayoyi mai zurfi, a rukunin gidajen alfarma na Filoli dake birnin San Francisco na kasar Amurka ranar Laraba. Taron kolin da aka dade ana jira, na zuwa ne shekara guda bayan ganawar shugabannin biyu a tsibirin Bali na kasar Indonesia.

A jawabinsa yayin ganawar shugaba Xi ya jaddada cewa, kasar Sin ta dukufa wajen samun daidaito, da dorewar dangantakar lumana da kasar Amurka. A lokaci guda kuma, kasar Sin tana da moriya da ka’idojin da suka kamata a kiyaye, da jan layin da ba za a iya ketarewa ba.

Kasar Sin na fatan kasashen biyu za su kasance abokan hulda masu mutunta juna da zaman tare cikin lumana. Taron dai ya kasance wani muhimmin zabi mai muhimmanci ga kasar Sin, don daidaita dangantakar dake tsakanin kasashen biyu, da kuma halin da ake ciki a duniya.
Masanin tattalin arziki na kasar Amurka Jeffrey Sachs ya shaidawa kamfanin dillancin labarai na Xinhua cewa, ra’ayin mutunta juna, da yin hadin gwiwa,da tattaunawa, da warware matsaloli tare, akwai “hikima sosai”, a cikinsa kuma yana da matukar muhimmanci.

Yana mai cewa, hadin gwiwar Sin da Amurka ba wai kawai kan muradun bai daya ne na kasashen biyu ba, yana kuma nuni da wani nauyi da ya rataya a wuyan kasashen duniya. A yayin taron, shugaba Xi ya yi kira ga kasashen biyu, da su hada kai a matsayinsu na manyan kasashe, yana mai jaddada cewa, za a iya magance matsalolin da ke addabar bil-Adama ne kawai ta hanyar hadin gwiwa tsakanin manyan kasashe.

Yarjejeniyar da aka cimma a yayin taron na San Francisco, ta nuna cewa, kasashen biyu suna da moriyar bai daya, kuma za su iya yin hadin gwiwa don samun sakamako mai tarin yawa. Dangantakar Sin da Amurka mai dorewa ba tunanin fata ba ne. Don haka, ya bukaci kasashen biyu su yi aiki tare.

Labarai Masu Nasaba

Za A Ci Gaba Da Tunawa Da Aminu Ɗantata A Ɓangaren Taimakon Jama’a — Buhari

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

Kuma tattaunawa shi ne mataki na farko na amincewa da juna, da mutunta juna da kuma hada kai. Daga Bali zuwa San Francisco, babban jirgin ruwa na hadin gwiwar kasashen Sin da Amurka, ya yi tattaki ta cikin duwatsun teku da kadawar igiyar ruwa. Amma ba a San Francisco za a tsaya ba. Birnin, wanda ya shaida tarihin musanya tsakanin Sinawa da Amurkawa na tsawon karni, wani sabon mafari ne na dangantakar kasashen Sin da Amurka. (Ibrahim)

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AlakaAmurkaDangantakaJoe BidenSan FranciscoSinTaroXi Jinping
ShareTweetSendShare
Previous Post

Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC

Next Post

Sakamakon Taron Kasashen Musulmi Da Larabawa: Saudiyya Da Nijeriya Za Su Jagoranci ‘Yantar Da Falasdin

Related

Bashin Da Ake Bin Nijeriya Ya Kai Tiriliyan 46.25
Labarai

Za A Ci Gaba Da Tunawa Da Aminu Ɗantata A Ɓangaren Taimakon Jama’a — Buhari

45 minutes ago
Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa
Manyan Labarai

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

54 minutes ago
Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)
Labarai

Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

2 hours ago
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe
Manyan Labarai

Rasuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Afirka – Atiku

2 hours ago
Rasuwar Ɗantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu
Manyan Labarai

Rasuwar Ɗantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu

5 hours ago
Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe
Manyan Labarai

Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe

6 hours ago
Next Post
Gaza

Sakamakon Taron Kasashen Musulmi Da Larabawa: Saudiyya Da Nijeriya Za Su Jagoranci 'Yantar Da Falasdin

LABARAI MASU NASABA

Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

June 28, 2025
Bashin Da Ake Bin Nijeriya Ya Kai Tiriliyan 46.25

Za A Ci Gaba Da Tunawa Da Aminu Ɗantata A Ɓangaren Taimakon Jama’a — Buhari

June 28, 2025
Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

June 28, 2025
Hukumar NPA Na Son Tara Kuɗaɗen Shiga Naira Tiriliyan 1.2 A 2025

Hukumar NPA Na Son Tara Kuɗaɗen Shiga Naira Tiriliyan 1.2 A 2025

June 28, 2025
An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata

An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata

June 28, 2025
Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

June 28, 2025
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe

Rasuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Afirka – Atiku

June 28, 2025
Sin Ta Samu Nasarorin A Zo A Gani Wajen Yaki Da Miyagun Kwayoyi

Sin Ta Samu Nasarorin A Zo A Gani Wajen Yaki Da Miyagun Kwayoyi

June 28, 2025
Kula Da  Kanki Bayan Haihuwa Abu Ne Muhimmi 4

Kula Da  Kanki Bayan Haihuwa Abu Ne Muhimmi 4

June 28, 2025
Mata Ku Kula Da Masu Tallan Maganin Hana Kishiya

Mata Ku Kula Da Masu Tallan Maganin Hana Kishiya

June 28, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.