• English
  • Business News
Sunday, June 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Barcelona Ta Dauki Kessie Da Christensen

by Abba Ibrahim Wada
3 years ago
in Wasanni
0
Kessie Da Christensen
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kungiyar kwallon kafa ta Barcelona ta cimma yarjejeniyar daukar ‘yan wasa guda biyu, Franck Yannick Kessier, wanda kwantiraginsa ya kare a AC Milan a watan jiya da kuma Andreas Christensen daga Chelsea.

Dan wasa Kessie ya saka hannu kan yarjejeniyar da za ta kare ranar 30 ga watan Yunin shekara ta 2026 haka kuma Barcelona ta sa farashin Yuro miliyan 500 ga duk kungiyar da ke son daukar dan wasan, idan yarjejeniyarsa ba ta kare ba a Camp Nou.

  • Rashford Ya Ce Ya Koma Kan Ganiyarsa

Ranar Laraba 6 ga watan Yuli, Barcelona ta gabatar da Franck Yannick Kessie a matakin dan wasanta kuma an haifi Franck Kessie ranar 19 ga watan Disambar shekarar 1996 a garin Ouragahio da ke Ibory Coast.

Dan wasan mai buga wasa daga tsakiya ko tsaron baya daga tsakiya ya fara wasa a Stella Club d’Adjame ta Ibory Coast daga baya ya koma Atalanta a shekarar 2014 kuma bayan da ya taka rawar gani a kakar wasa ta 2016 zuwa 2017 a Atalanta, daga nan ne AC Milan ta yi zawarcinsa.

Ya koma AC Milan buga wasannin aro a 2017 daga nan ta saye shi a 2019 kan Yuro miliyan 33 kuma tsawon kakar was biyar da Kessie ya yi a Milan ya kara samun gogewa, ya kuma ci kwallaye, ya kuma bayar an zura a raga.

Labarai Masu Nasaba

Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

Dan wasan tawagar Ibory Coast ya taimakawa AC Milan ta dauki Serie A a kakar da aka karkare, kofin farko da ta dauka tun bayan kakar wasa 11. Har ila yau, Barcelona ta sanar da daukar dan wasa Andreas Christensen daga Chelsea, bayan da kwantiraginsa shi ma ya kare a Stamford Bridge a karshen watan Yuni kuma Christensen ya amince da kunshin yarjejeniyar.

kaka hudu da saka farashin Yuro miliyan 500 ga duk kungiyar da ke son daukarsa, idan wa’adinsa bai kare ba a Camp Nou.
Dan kwallon ya koma Chelsea daga Brondby a shekarar 2012, wanda kaka biyu tsakani ya fara buga wasa a matakin kwararren dan wasa sai dai Chelsea ta bayar da aron dan wasan kaka biyu ga Borussia Monchengladbach, sai dai tun da ya koma Chelsea ya nuna kansa.

Ya buga wa kungiyar wasanni 167 har da 26 da ya yi a kakar da ta wuce da cin kwallo hudu kuma dan kwallon ya lashe Champions League da Europa League da Club World Cup da kuma UEFA Super Cup a wasannin da ya yi wa kungiyar Stamford Bridge.

Haka kuma Chelsea ta yi nasarar cin wasanni 92 a karawar da Christensen ya buga mata sai dai Bayan da Barcelona ta kammala daukar Christensen da Kessie, kungiyar za ta mayar da hankali kan zawarcin Raphinha na Leeds United.

Haka kuma Barcelona na tattaunawa da Ousmane Dembele kan tsawaita zamansa a Camp Nou, bayan da yarjejeniyar dan kwallon tawagar Faransa ta kare a kungiyar kuma tuni dai Manchester United ke ta kokarin ganin ta kammala sayen dan wasan Barcelona, Frenkie de Jong kafin fara kakar bana da za a yi a cikin watan Agusta.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Lauya Ya Koka Kan Jinkiri Wajen Yanke Hukunci A Kotuna

Next Post

Saboda Guardiola Na Koma Manchester City, Cewar Phillips

Related

Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu
Wasanni

Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

16 hours ago
Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan
Wasanni

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

18 hours ago
Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal
Wasanni

Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

19 hours ago
Diaz Ba Na Sayarwa Bane – Liverpool Ta Fadawa Barcelona
Wasanni

Diaz Ba Na Sayarwa Bane – Liverpool Ta Fadawa Barcelona

2 days ago
Kocin Inter Milan Simone Inzaghi Ya Bar Kungiyar Kwanaki Biyu Bayan Rashin Nasara A Hannun PSG
Wasanni

Kocin Inter Milan Simone Inzaghi Ya Bar Kungiyar Kwanaki Biyu Bayan Rashin Nasara A Hannun PSG

4 days ago
Manchester United Ta Kammala Ɗaukar Cunha Daga Wolves Akan Miliyan 62.5
Wasanni

Manchester United Ta Kammala Ɗaukar Cunha Daga Wolves Akan Miliyan 62.5

6 days ago
Next Post
Phillips

Saboda Guardiola Na Koma Manchester City, Cewar Phillips

LABARAI MASU NASABA

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

June 7, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

June 7, 2025
Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

June 7, 2025
Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

June 7, 2025
Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

June 7, 2025
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

June 7, 2025
Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

June 7, 2025
Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

June 7, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

June 7, 2025
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.