• English
  • Business News
Tuesday, August 12, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Barcelona Ta Dauki Kessie Da Christensen

by Abba Ibrahim Wada
3 years ago
in Wasanni
0
Kessie Da Christensen
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kungiyar kwallon kafa ta Barcelona ta cimma yarjejeniyar daukar ‘yan wasa guda biyu, Franck Yannick Kessier, wanda kwantiraginsa ya kare a AC Milan a watan jiya da kuma Andreas Christensen daga Chelsea.

Dan wasa Kessie ya saka hannu kan yarjejeniyar da za ta kare ranar 30 ga watan Yunin shekara ta 2026 haka kuma Barcelona ta sa farashin Yuro miliyan 500 ga duk kungiyar da ke son daukar dan wasan, idan yarjejeniyarsa ba ta kare ba a Camp Nou.

  • Rashford Ya Ce Ya Koma Kan Ganiyarsa

Ranar Laraba 6 ga watan Yuli, Barcelona ta gabatar da Franck Yannick Kessie a matakin dan wasanta kuma an haifi Franck Kessie ranar 19 ga watan Disambar shekarar 1996 a garin Ouragahio da ke Ibory Coast.

Dan wasan mai buga wasa daga tsakiya ko tsaron baya daga tsakiya ya fara wasa a Stella Club d’Adjame ta Ibory Coast daga baya ya koma Atalanta a shekarar 2014 kuma bayan da ya taka rawar gani a kakar wasa ta 2016 zuwa 2017 a Atalanta, daga nan ne AC Milan ta yi zawarcinsa.

Ya koma AC Milan buga wasannin aro a 2017 daga nan ta saye shi a 2019 kan Yuro miliyan 33 kuma tsawon kakar was biyar da Kessie ya yi a Milan ya kara samun gogewa, ya kuma ci kwallaye, ya kuma bayar an zura a raga.

Labarai Masu Nasaba

Sadiq Umar Da Bello El-Rufai Sun Sayi Ƙungiyar Rancher Bees FC Ta Kaduna

Man United Sun Kammala Sayen Benjamin Sesko Daga RB Leipzig

Dan wasan tawagar Ibory Coast ya taimakawa AC Milan ta dauki Serie A a kakar da aka karkare, kofin farko da ta dauka tun bayan kakar wasa 11. Har ila yau, Barcelona ta sanar da daukar dan wasa Andreas Christensen daga Chelsea, bayan da kwantiraginsa shi ma ya kare a Stamford Bridge a karshen watan Yuni kuma Christensen ya amince da kunshin yarjejeniyar.

kaka hudu da saka farashin Yuro miliyan 500 ga duk kungiyar da ke son daukarsa, idan wa’adinsa bai kare ba a Camp Nou.
Dan kwallon ya koma Chelsea daga Brondby a shekarar 2012, wanda kaka biyu tsakani ya fara buga wasa a matakin kwararren dan wasa sai dai Chelsea ta bayar da aron dan wasan kaka biyu ga Borussia Monchengladbach, sai dai tun da ya koma Chelsea ya nuna kansa.

Ya buga wa kungiyar wasanni 167 har da 26 da ya yi a kakar da ta wuce da cin kwallo hudu kuma dan kwallon ya lashe Champions League da Europa League da Club World Cup da kuma UEFA Super Cup a wasannin da ya yi wa kungiyar Stamford Bridge.

Haka kuma Chelsea ta yi nasarar cin wasanni 92 a karawar da Christensen ya buga mata sai dai Bayan da Barcelona ta kammala daukar Christensen da Kessie, kungiyar za ta mayar da hankali kan zawarcin Raphinha na Leeds United.

Haka kuma Barcelona na tattaunawa da Ousmane Dembele kan tsawaita zamansa a Camp Nou, bayan da yarjejeniyar dan kwallon tawagar Faransa ta kare a kungiyar kuma tuni dai Manchester United ke ta kokarin ganin ta kammala sayen dan wasan Barcelona, Frenkie de Jong kafin fara kakar bana da za a yi a cikin watan Agusta.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Lauya Ya Koka Kan Jinkiri Wajen Yanke Hukunci A Kotuna

Next Post

Saboda Guardiola Na Koma Manchester City, Cewar Phillips

Related

Sadiq Umar Da Bello El-Rufai Sun Sayi Ƙungiyar Rancher Bees FC Ta Kaduna
Wasanni

Sadiq Umar Da Bello El-Rufai Sun Sayi Ƙungiyar Rancher Bees FC Ta Kaduna

11 hours ago
Man United Sun Kammala Sayen Benjamin Sesko Daga RB Leipzig
Wasanni

Man United Sun Kammala Sayen Benjamin Sesko Daga RB Leipzig

3 days ago
Ina Fatan Taka Inda Yayana Ya Taka A Fagen Ƙwallon Ƙafa A Duniya -Jobe Bellingham
Wasanni

Ina Fatan Taka Inda Yayana Ya Taka A Fagen Ƙwallon Ƙafa A Duniya -Jobe Bellingham

3 days ago
Tinubu Ya Gwangwaje Ƴan Wasan Ƙwallon Kwando Ta Mata Da Dala $100,000 Kowace
Wasanni

Jerin Ƴan Wasa Mata Da Suka Samu Kyautar Dala 100,000 Daga Gwamnatin Nijeriya

3 days ago
UEFA Ta Ci Tarar Lamine Yamal Da Lewandowski Kan Karya Dokar Shan Ƙwayar Ƙara Kuzari
Wasanni

UEFA Ta Ci Tarar Lamine Yamal Da Lewandowski Kan Karya Dokar Shan Ƙwayar Ƙara Kuzari

4 days ago
Barcelona Ta Tube Ter Stergen Daga Mukaminsa Na Kaftin Din Kungiyar 
Wasanni

Barcelona Ta Tube Ter Stergen Daga Mukaminsa Na Kaftin Din Kungiyar 

5 days ago
Next Post
Phillips

Saboda Guardiola Na Koma Manchester City, Cewar Phillips

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Kano Za Ta Horar Da Tubabbun ‘Yandaba 718 Sana’o’i 

Gwamnatin Kano Za Ta Horar Da Tubabbun ‘Yandaba 718 Sana’o’i 

August 12, 2025
Xi: Sin Da Brazil Na Iya Zama Misalin Hadin Kai Da Dogaro Da Kai Ga Kasashe Masu Tasowa

Xi: Sin Da Brazil Na Iya Zama Misalin Hadin Kai Da Dogaro Da Kai Ga Kasashe Masu Tasowa

August 12, 2025
Jiragen saman NAF Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 592, Sun Lalata Kayayyakin Yaki 372

Jiragen saman NAF Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 592, Sun Lalata Kayayyakin Yaki 372

August 12, 2025
Ma’aikatar Cinikayya Ta Kasar Sin Ta Yi Karin Haske Kan Batun Saka Wasu Sassa Cikin Wadanda Ta Sanyawa Takunkumin Sayar Musu Da Kayayyaki

Ma’aikatar Cinikayya Ta Kasar Sin Ta Yi Karin Haske Kan Batun Saka Wasu Sassa Cikin Wadanda Ta Sanyawa Takunkumin Sayar Musu Da Kayayyaki

August 12, 2025
Ronaldo Zai Daura Aurensa Na Farko A Rayuwa Tare Da Budurwarsa Georgina

Ronaldo Zai Daura Aurensa Na Farko A Rayuwa Tare Da Budurwarsa Georgina

August 12, 2025
Sin Ta Gabatar Da Sanarwar Hadin Gwiwa Kan Taron Tattalin Arziki Da Cinikayya Tsakaninta Da Amurka A Stockholm

Sin Ta Gabatar Da Sanarwar Hadin Gwiwa Kan Taron Tattalin Arziki Da Cinikayya Tsakaninta Da Amurka A Stockholm

August 12, 2025
Kano

Gwamnatin Kano Ta Bayar Da Kwangilar Hanyoyi 17 Akan Naira Biliyan 40.8

August 12, 2025
Fasahohin AI Sun Bude Sabon Babi Na Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

Fasahohin AI Sun Bude Sabon Babi Na Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

August 12, 2025
‘Yan Nijeriya Miliyan 14 Sun Yi Bikin Murnar Karɓar Kyautar N23m Daga Bankin STANBIC IBTC

‘Yan Nijeriya Miliyan 14 Sun Yi Bikin Murnar Karɓar Kyautar N23m Daga Bankin STANBIC IBTC

August 12, 2025
PDP Ta Soki Gwamnatin Tinubu Kan Tsare Tambuwal Da EFCC Ta Yi

PDP Ta Soki Gwamnatin Tinubu Kan Tsare Tambuwal Da EFCC Ta Yi

August 12, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.