• English
  • Business News
Sunday, November 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Kaduna Ta Kaddamar Da Kwamitin Mutum 8 Don Inganta Harkokin Aikin Hajjin 2024

by Sulaiman
2 years ago
Hajjin 2024

A ci gaba da kokarin ganin an saukaka wa alhazan jihar Kaduna gudanar da ayyukan aikin hajji cikin kwanciyar hankali, gwamnatin jihar Kaduna ta kaddamar da wani kwamiti mai mutum 8 wanda zai tabbatar da samar da masaukai, ciyarwa, sufuri, hidimomin Hadaya, da tantuna don amfanin alhazan Jihar.

Mataimakiyar gwamnan jihar, Dakta Hadiza Balarabe, a lokacin da take kaddamar da kwamitin a gidan gwamnatin jihar Kaduna a ranar Larabar da ta gabata, ta ce zaben mambobin kwamitin an yi shi ne bisa la’akari da kwarewa, kwazo, da jajircewarsu wajen ci gaban jihar Kaduna da kuma rayuwar al’ummarta baki daya.

  • Muna Rokon Shugaba Tinubu Ya Hana Ministoci Tafiye-tafiye Zuwa Kasashen Waje – Akpabio
  • Sanatocin Arewacin Nijeriya Sun Matsa Wa Tinubu Lamba Kan Sake Bude Iyakar Nijar

Dakta Balarabe ta bayyana cewa, gwamnatin jihar Kaduna ta san irin kalubalen da aka fuskanta a hajjin bara, wanda ya jefa alhazan cikin kunci da damuwa.

A cewarta, wannan hakki ne na gwamnatin ta hada gwiwa da hukumomi domin lalubo inda matsalar take kuma ta gyara kura-kuran da aka samu tare da samar da ingantaccen tsari wanda zai ba da fifiko ga jin dadin Alhazan.

Ta bayyana cewa, muhimman bangarorin da kwamitin zai fi mayar da hankali su ne: bukatar kulawa da himma musamman wajen samar da kyakkyawan wurin kwana, ciyarwa, sufuri, da tantuna.

LABARAI MASU NASABA

Zargin Ɓatanci Ga Annabi: Alaƙar Triumph Da Gwamnatin Kano Da Majalisar Shura

Turkiyya Na Karbar Bakuncin Wasu Kasashen Musulmai Game Da Makomar Gaza

“Ina son mika godiya ta musamman ga Sheikh Salisu Abubakar bisa yadda ya amince ya jagoranci kwamitin kula da aikin hajjin 2024. Allah (SAW) Ya saka muku da alkairi kan sadaukarwarku da kuke yi kan ci gaban Jiharmu mai daraja”. Inji Dakta Hadiza

A nasa jawabin, Shugaban Kwamitin, Sheikh Salisu Abubakar, wanda ya yaba wa Uba Sani bisa yadda ya yi musu kyakkyawan zato ya mika musu ragamar wannan aiki, ya yi alkawarin yin aiki tukuru domin cimma bukatun da gwamnatin ke nema.

Sauran mambobin kwamitin sun hada da Baba Ahmed Rufa’i, Imam Buhari, Maimuna Waziri, Aminu Kasimu, Farfesa Muhammadu Mustapha Gwadabe, AVM Muhammad Rabiu Dabo, da Ummakulsum Jibril Maigwari.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Triumph
Manyan Labarai

Zargin Ɓatanci Ga Annabi: Alaƙar Triumph Da Gwamnatin Kano Da Majalisar Shura

November 9, 2025
Turkiyya Na Karbar Bakuncin Wasu Kasashen Musulmai Game Da Makomar Gaza
Labarai

Turkiyya Na Karbar Bakuncin Wasu Kasashen Musulmai Game Da Makomar Gaza

November 8, 2025
Kasashen Afirka Bakwai Da Sojojin Amurka Suka Shiga
Labarai

Kasashen Afirka Bakwai Da Sojojin Amurka Suka Shiga

November 8, 2025
Next Post
Kwace Wa NNPP Zaben Kano Na Iya Haddasa Tashin Hankali A Afrika – NNPP

Kwace Wa NNPP Zaben Kano Na Iya Haddasa Tashin Hankali A Afrika - NNPP

LABARAI MASU NASABA

Triumph

Zargin Ɓatanci Ga Annabi: Alaƙar Triumph Da Gwamnatin Kano Da Majalisar Shura

November 9, 2025
Kasar Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Kan Samun Ci Gaba Mai Karancin Fitar Da Hayaki

Kasar Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Kan Samun Ci Gaba Mai Karancin Fitar Da Hayaki

November 8, 2025
Kasar Sin Ta Sake Jaddada Cikakken Goyon Bayanta Ga Muhimmiyar Rawar Da MDD Ke Takawa A Harkokin Kasa Da Kasa 

Kasar Sin Ta Sake Jaddada Cikakken Goyon Bayanta Ga Muhimmiyar Rawar Da MDD Ke Takawa A Harkokin Kasa Da Kasa 

November 8, 2025
Turkiyya Na Karbar Bakuncin Wasu Kasashen Musulmai Game Da Makomar Gaza

Turkiyya Na Karbar Bakuncin Wasu Kasashen Musulmai Game Da Makomar Gaza

November 8, 2025
Babban Yankin Sin Da Taiwan Sun Yi Tarukan Bita Don Tunawa Da Taron Xi Da Ma Mai Tarihi

Babban Yankin Sin Da Taiwan Sun Yi Tarukan Bita Don Tunawa Da Taron Xi Da Ma Mai Tarihi

November 8, 2025
Kasashen Afirka Bakwai Da Sojojin Amurka Suka Shiga

Kasashen Afirka Bakwai Da Sojojin Amurka Suka Shiga

November 8, 2025
Firaministan Kasar Georgia: CIIE Muhimmin Dandali Ne

Firaministan Kasar Georgia: CIIE Muhimmin Dandali Ne

November 8, 2025
Yadda Aka Tsara Gudanar Da Gasar Kofin Afirka A Moroko

Yadda Aka Tsara Gudanar Da Gasar Kofin Afirka A Moroko

November 8, 2025
CMG Ya Watsa Jerin Shirye-Shirye Don Tunawa Da Cika Shekaru 80 Da Dawowar Yankin Taiwan Kasar Sin

CMG Ya Watsa Jerin Shirye-Shirye Don Tunawa Da Cika Shekaru 80 Da Dawowar Yankin Taiwan Kasar Sin

November 8, 2025
CMG Ya Gabatar Da Jerin Rahotannin Talabijin Kan Tunawa Da Cika Shekaru 80 Da Dawowar Yankin Taiwan Kasar Sin

CMG Ya Gabatar Da Jerin Rahotannin Talabijin Kan Tunawa Da Cika Shekaru 80 Da Dawowar Yankin Taiwan Kasar Sin

November 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.