• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jakadan Sin Ya Bayyana Matsayin Kasar Sin Da Matakanta Da Ra’ayinta Kan Batun Falasdinu Da Isra’ila

by CGTN Hausa
1 year ago
in Daga Birnin Sin
0
Jakadan Sin Ya Bayyana Matsayin Kasar Sin Da Matakanta Da Ra’ayinta Kan Batun Falasdinu Da Isra’ila
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kwamitin gudanarwar hukumar kiwon lafiya ta duniya wato WHO, ya gudanar da taro na musamman game da batun kiwon lafiya a yankunan Falasdinu da aka mamaye. 

Jakadan Sin dake ofishin Geneva na MDD, da sauran hukumomin kasa da kasa dake kasar Switzerland Chen Xu, ya gabatar da jawabi a yayin taron, inda ya bayyana matsayin kasar Sin, da kuma matakanta da ra’ayinta na kawo karshen tashin hankali.

  • Xi Ya Bukaci A Tsagaita Bude Wuta Tare Da Gudanar Da Tattaunawar Zaman Lafiya Kan Rikicin Falasdinu Da Isra’ila
  • Jami’in Diflomasiyyar Falasdinu: PA Ta Godewa Kasar Sin Bisa Aikewa Da Agaji Ga ’Yan Gaza Cikin Sa’o’in Bukata

Chen Xu ya bayyana ra’ayoyinsa uku game da jigon taron. Na farko akwai batun inganta tsagaita bude wuta. Ya ce bangaren kasar Sin yana nuna damuwa game da dorewar yaki a zirin Gaza. Ya ce ya kamata bangarori masu alaka da hakan su kwantar da hankali, su ba da damar samun zaman lafiya, da baiwa jama’ar wurin zarafin zaman lafiya da kwanciyar hankali.

Kaza lika a cewar jami’in, bangaren Sin ya yi kira ga sassan kasa da kasa, musamman kasashen dake da tasiri kan batun Falasdinu da Isra’ila, da su ba da gudummawarsu ta sauke nauyi, ta inganta tsagaita wuta cikin dogon lokaci, kuma su kiyaye lafiya da ’yancin kasancewar fararen hula a yankin.

Na biyu, a warware matsalar kiwon lafiya. Ya ce kamata ya yi bangarori daban daban su yi iyakacin kokarin kiyaye tsaron likitoci da kayayyakin kiwon lafiya, su nuna goyon baya ga ayyukan WHO, da sauran hukumomin jin kai, da ba da magunguna, da kayayyakin aikin kiwon lafiya da ake bukata cikin gaggawa a yankin, da kuma ceto da kwashe wadanda suka jikkata. Ya ce ya kamata a yi hangen nesa, a taimaki Falasdinawa, wajen sake gina manyan kayayyakin more rayuwa na likitanci, ta yadda za a inganta ci gaban fannin kiwon lafiyar Falasdinu.

Labarai Masu Nasaba

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Na uku, a yi kokarin “Kafa kasashe biyu”. Wato ya kamata a gaggauta sake fara tattaunawa kan batun shimfida zaman lafiya tsakanin Falasdinu da Isra’ila, da sa kaimi wajen hanzarta aiwatar da manufar “Kafa kasashe biyu” kamar yadda ya kamata, da tabbatar da ‘yancin al’ummar Falasdinu na kafa wata kasarsu, da kasancewarsu, da kuma na komarwasu a yankin. (Safiyah Ma)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: GazaHamasIsra'ila
ShareTweetSendShare
Previous Post

Harin Tudun Biri: Tawagar ‘Yan Majalisar Wakilai Na Arewa Ta Bayar Da Gudunmuwar Naira Miliyan N350m

Next Post

Sin Za Ta Ci Gaba Da Sa Kaimi Ga Kare Hakkin Dan Adam

Related

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe
Daga Birnin Sin

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

1 hour ago
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

1 hour ago
Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata
Daga Birnin Sin

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

3 hours ago
Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4
Daga Birnin Sin

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

6 hours ago
Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

8 hours ago
Namibia Za Ta Karfafa Hulda Da Sin Yayin Baje Kolin Cinikayya Da Tattalin Arziki
Daga Birnin Sin

Namibia Za Ta Karfafa Hulda Da Sin Yayin Baje Kolin Cinikayya Da Tattalin Arziki

9 hours ago
Next Post
Sin Za Ta Ci Gaba Da Sa Kaimi Ga Kare Hakkin Dan Adam

Sin Za Ta Ci Gaba Da Sa Kaimi Ga Kare Hakkin Dan Adam

LABARAI MASU NASABA

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

June 6, 2025
Daurarru

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

June 6, 2025
Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

June 6, 2025
Wutar lantarki

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

June 6, 2025
Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

June 6, 2025
Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

June 6, 2025
Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

June 6, 2025
An Kama Wadanda Ake Zargi Da Kai Wa Shugaban Kwadago Hari Ribadu

Ribadu Ya Kara Jaddada Gargadinsa Kan Biyan Kudin Fansa Ga Masu Garkuwa Da Mutane

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.