• English
  • Business News
Sunday, August 3, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mahara Sun Sace Sarki Da Fadawansa A Garin Pupule Na Jihar Taraba

by Muhammad
2 years ago
in Al'ajabi, Manyan Labarai
0
Mahara Sun Sace Sarki Da Fadawansa A Garin Pupule Na Jihar Taraba
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wasu ‘yan bindiga sun kai hari garin Pupule na yankin karamar hukumar Yorro ta jihar Taraba, inda suka sace mutum 23 ciki har da basarake mai daraja ta biyu da fadawansa.

BBC ta rawaito cewa, lamarin ya afku ne a ranar Talata da daddare inda ‘yan bindigar masu yawan gaske suka shiga garin tare da kewaye shi.

  • An Sace Mai Ciki, Hakimi Da ‘Yansanda A Taraba
  • Mutane 32 Sun Mutu A Wani Sabon Hatsarin Kwale-kwale A Jihar Taraba

Wani mazaunin garin ya shaida wa BBC cewa, ba su san adadin ‘yan bindigar da suka shiga garin nasu ba saboda yawansu.

Ya ce,” sun shiga cikin dare suka dauki na dauka suka bar na bari, kuma a cikin wadanda suka dauka baya ga basaraken da dogarinsa, akwai limamin masallacin Jumma’a da fastoci biyu da kuma sauran jama’ar gari.”

Ya ƙara da cewa ‘yan bindigar sun fasa shaguna tare da satar kayan abinci da abubuwan sha.

Labarai Masu Nasaba

Borno Za Ta Sake Tsugunar Da ‘Yan Gudun Hijira 5,000 Kafin Damuna Ta Kare

Ma’aikatan Jinya Sun Janye Yajin Aiki Bayan Gwamnatin Tarayya Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu 

“Ba wannan ne zuwan su na farko ba, wannan shi ne karo na hudu da suka je garinmu” In ji mazaunin garin na Pupule.

Tuni dai rundunar ‘yan sanda Nijeriya reshen jihar ta Taraba ta ce ta fara bincike tare da neman mutanen da aka sacen.

Mai magana da yawun rundunar SP Abdullahi Usman Jada, ya ce suna samun labarin abin da ya farun, nan da nan kwamishinan ‘yan sandan jihar bai yi kasa a gwiwa ba ya tura wani sashe na musamman na jami’ansu wadanda ke kula da masu satar mutane domin su je garin da kuma bin sawun ‘yan bindigar.

Ya ce an baza jami’an tsaro a jejin domin neman mutanen da aka sace, “amma har yanzu ba mu ji komai ba,” a cewarsa.

Jama’ar garin na Pupule dai, sun ce a duk hare-haren da aka kai masu sau uku a can baya, wannan shi ne mafi muni da tayar da hankali, kuma sun yi kira da a girke masu karin jami’an tsaro a yankin.

Matsalar tsaro a Najeriya dai na ci gaba da zama ruwan dare gama duniya musamman ta masu satar mutane domin kudin fansa a yankunan arewa maso yammacin kasar da kuma wasu yankuna na arewa maso gabashin kasar.

Kuma duk da kokarin da gwamnatin tarayyar kasar ta ce tana yi don kawo karshen wannan matsala har yanzu ba ta sauya zani ba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: MaharaSace SarkiTaraba
ShareTweetSendShare
Previous Post

INEC Za Ta Gudanar Da Zaɓuɓɓuka 34 Cikin Fabrairun 2024 – Yakubu

Next Post

Gwamnati Ta Shirya Fatattakar ‘Yan Bindiga A Duk Inda Suke – Ministan Tsaro

Related

Borno Za Ta Sake Tsugunar Da ‘Yan Gudun Hijira 5,000 Kafin Damuna Ta Kare
Manyan Labarai

Borno Za Ta Sake Tsugunar Da ‘Yan Gudun Hijira 5,000 Kafin Damuna Ta Kare

11 hours ago
Ma’aikatan Jinya Sun Janye Yajin Aiki Bayan Gwamnatin Tarayya Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu 
Da ɗumi-ɗuminsa

Ma’aikatan Jinya Sun Janye Yajin Aiki Bayan Gwamnatin Tarayya Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu 

1 day ago
Kongo Na Neman Goyon Bayan Nijeriya Kan Shugabancin UNESCO
Manyan Labarai

Kongo Na Neman Goyon Bayan Nijeriya Kan Shugabancin UNESCO

1 day ago
Yarjejeniyar Dala Biliyan Ɗaya Da Ƙasar Brazil Za Ta Haɓaka Fannin Noma A Nijeriya —Tinubu
Manyan Labarai

Yarjejeniyar Dala Biliyan Ɗaya Da Ƙasar Brazil Za Ta Haɓaka Fannin Noma A Nijeriya —Tinubu

2 days ago
ADC Za Ta Kayar Da Tinubu A 2027 – Dino Melaye
Manyan Labarai

ADC Za Ta Kayar Da Tinubu A 2027 – Dino Melaye

2 days ago
Tinubu Ya Sauke Gawuna A Matsayin Shugaban Kwamitin Gudanarwar BUK, Ya Maye Gurbinsa Da Kaita 
Manyan Labarai

Tinubu Ya Sauke Gawuna A Matsayin Shugaban Kwamitin Gudanarwar BUK, Ya Maye Gurbinsa Da Kaita 

2 days ago
Next Post
Shugaban EFCC Ya Nemi Cin Hancin $2m A Wajena, Ina Da Hujja –Matawalle

Gwamnati Ta Shirya Fatattakar 'Yan Bindiga A Duk Inda Suke - Ministan Tsaro

LABARAI MASU NASABA

Wani Babban Jigon APC Ya Fice Daga Jam’iyyar A Katsina

Wani Babban Jigon APC Ya Fice Daga Jam’iyyar A Katsina

August 3, 2025
Sanata Shehu Buba Ya Ƙaddamar Da Rabon Taki Da Rigakafin Shanu A Bauchi

Sanata Shehu Buba Ya Ƙaddamar Da Rabon Taki Da Rigakafin Shanu A Bauchi

August 3, 2025
Waɗanne Ƙasashe Ne Suka Amince Da Kafa Ƙasar Falasɗinu?

Waɗanne Ƙasashe Ne Suka Amince Da Kafa Ƙasar Falasɗinu?

August 3, 2025
Dangote Ya Ɗauki Nauyin Bikin Baje Kolin Gidajen Afrika Da Mahalarta Ƙasashe 21

Dangote Ya Ɗauki Nauyin Bikin Baje Kolin Gidajen Afrika Da Mahalarta Ƙasashe 21

August 3, 2025
An Fara Bayar Da Hidimomin Da Suka Shafi Sauka Da Tashi Domin Gasar Wasanni Ta Duniya Ta Chengdu

An Fara Bayar Da Hidimomin Da Suka Shafi Sauka Da Tashi Domin Gasar Wasanni Ta Duniya Ta Chengdu

August 3, 2025
Rikici Ya Ɓarke A Zaɓen Ribas, Ƴan PDP Sun Fito A Matsayin Ƴan Takarar APC

Rikici Ya Ɓarke A Zaɓen Ribas, Ƴan PDP Sun Fito A Matsayin Ƴan Takarar APC

August 3, 2025
Ana Gaggauta Ayyukan Gyara Tituna Da Gadojin Da Ambaliya Ta Lalata A Arewacin Kasar Sin

Ana Gaggauta Ayyukan Gyara Tituna Da Gadojin Da Ambaliya Ta Lalata A Arewacin Kasar Sin

August 3, 2025
Shugabar Tanzania Ta Kaddamar Da Cibiyar Cinikayya Da Jigila Da Sin Ta Gina A Kasar

Shugabar Tanzania Ta Kaddamar Da Cibiyar Cinikayya Da Jigila Da Sin Ta Gina A Kasar

August 3, 2025
Manoma Sun Caccaki Tinubu Kan Ƙarfafa Shigo Da Shinkafa Da Masara Daga Ƙasashen Waje

Manoma Sun Caccaki Tinubu Kan Ƙarfafa Shigo Da Shinkafa Da Masara Daga Ƙasashen Waje

August 3, 2025
Amurka Ta Gargaɗi Ƴan Nijeriya Kan Zuwa Ƙasarta Domin Haihuwa

Amurka Ta Gargaɗi Ƴan Nijeriya Kan Zuwa Ƙasarta Domin Haihuwa

August 3, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.