• English
  • Business News
Saturday, November 1, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bankwana Da 2023: Wainar Da Aka Toya A Fagen Wasanni

by Abba Ibrahim Wada
2 years ago
2023

A yayin da shekara ta 2023 ke bankwana a wannan makon, Kamfanin Jaridar LEADERSHIP HAUSA ya zakulo wasu daga cikin muhimman abubuwan da suka faru a wannan shekarar ta 2023 a bangaren wasanni.

Wasu daga cikin abubuwan da suka faru a bangaren wasanni a shekara mai karewa shi ne a ranar Laraba 6 ga watan Yuli na shekara ta 2023 aka kece-raini a tsakanin kungiyar kwallon kafa ta Kano Pillars da takwararta ta Katsina United a wasan raba-gardama na neman tsallakewa zuwa gasar Firimiyar Nijeriya na kungiyoyi 8 da ke kira Super 8, inda a ciki za a dauki kungiyoyi hudu, biyu a Arewa, biyu a Kudu su dawo gasar Firimiyar.

  • Gwamnan Katsina Ya Yi Wa Ma’aikatan Jihar Ƙarin ₦10,000 Kan Albashi, ‘Yan Fansho ₦5,000
  • INEC Ta Tilasta Wa Daraktocinta 4 Yin Ritaya

A wasan karshe, Katsina United ta doke Kano Pillars da ci daya mai ban-haushi, inda Bictor Mbaoma ya zura kwallo a ragar Kano Pillars a bugun finareti, sai dai duk da an doke Pillars, kasancewar kungiyar DMD ta doke kungiyar EFCC ta Abuja, sai kungiyoyin Katsina United da Kano Pillars suka samu nasarar tsallakawa zuwa Firimiya.

DMD ta lallasa EFCC da ci 3-0, inda Kano Pillars ta kare da maki shida, Katsina United ta samu maki shida, DMD da EFCC suka samu maki uku-uku. A kakar bara ce dai kungiyar ta Kano Pillars ta yi rashin nasara, inda ta koma rukuni na biyu na gajiyayyu a gasar Nijeriya kuma a tarihin Kano Pillars, wadda aka kafa a 1990, sau uku tana buga gasar rukuni na biyu a 1994 da 1999 da kuma bana.

Daga cikin dalilan da suka jawo faduwar Pillars, akwai samunta da laifi da hukumar shirya gasar ta yi bayan ta dawo buga wasa a filin wasa na Sani Abacha, inda aka mayar da Pillars din Kaduna da buga wasannin gida.

LABARAI MASU NASABA

Barcelona Na Shirin Ɗauko Victor Osimhen Na Galatasaray

Ina Fatan Buga Kofin Duniya Na 2026 — Messi

A wasan da aka buga na Arewa mafi zafi wato Northern Derby da Katsina United ce aka samu rikici, inda magoya bayan Pillars suka farfasa motar Katsina United haka kuma a wasan da aka buga tsakanin Kano Pillars da Dakkada FC, shugaban kungiyar Kano Pillars na lokacin, Surajo Shu’aibu Yahaya wanda aka fi sani da Jambul ya yi wani laifin, inda aka sake kwashe wa Pillars maki uku, ya kama maki shida kenan.

Sai dai ba don cire maki shidan ba, da kungiyar ba ta koma baya ba kuma a lokacin Pillars ta daukaka kara domin a dawo mata da makinta, amma ba ta samu nasara ba.

A daya bangaren, kungiyar Sporting Lagos ce ta bayar da mamaki, inda ta samu nasarar zuwa gasar Firimiya a shekara biyu kacal da kafuwarta inda kungiyar ta doke Stormers da ci 2-0, inda nan take ta samu tsallakawa zuwa Firimiyar.

An kafa kungiyar ne a shekarar 2022 a Legas, sai dai tana da karfin dukiya, inda a watan Maris na bana ta shiga kwantiragi da kulob din Aarhus Fremad da ke kasar Denmark, sannan ta shiga yarjejeniyar buga rigunan wasa da Kamfanin Klasha.

Shugaban kungiyar, Godwin Enakhena ne ya jagoranci kungiyar MFM lokacin da ya dago ta zuwa gasar Firimiya, kamar yadda ya yi da Sporting Lagos a yanzu sannan a lokacin hada wannan rahoto, ba a kammala daya wasann Kudu ba, inda za a samu kungiyar da za ta hadu da Sporting Lagos wajen tsallakowa gasar Firimiyar da kungiyar Heartland.

  • Osimhen Ya Zama Gwarzon Dan Wasan Afirka

Sannan a ranar 11 ga watan Disamba na shekarar 2023 dan wasan tawagar Nijeriya, Bictor Osimhen ya lashe kyautar gwarzon dan wasan kwallon kafar Afirka na shekarar 2023.

Dan wasan na Super Eagles ya lashe kyautar a bikin da aka gudanar a Marrakech, wanda ya ja ragamar kungiyar kwallon kafa ta Napoli ta lashe Serie A karon farko bayan shekara 33.

Osimhen ya yi takara tare da dan wasan Morocco Achraf Hakimi da na Masar Mohamed Salah kuma gaba daya ya doke su ya lashe wannan kyautar wadda rabon da dan Nijeriya ta lashe shekara 33 kenan.

Dan wasan shi ne ya kai Super Eagles gasar kofin Afirka da za a yi a Ibory Coast a farkon wannan shekarar, wanda ya ci kwallo 10 a karawar cancantar shiga gasar cin kofin.

Osimhen ya ci kwallo 27 a dukkan fafatawa a Napoli, wadda ta koma kan ganiya a kwallon Italiya a kakar wasa ta 2022 zuwa 2023, sannan dan wasan mai shekara 24 ya zama na farko a Napoli da ya zama kan gaba a cin kwallaye a babbar gasar kwallon kafar kasar ta Italiya tun bayan Diego Maradona a 1987 zuwa 1988, sannan Osimhen ya zama dan Nijeriya na farko da ya lashe kyautar tun bayan Kanu Nwankwo a 1999.

A fannin mata Asisat Oshoala (Nijeriya, Barcelona) ita ce ta lashe gwarzuwar kwallon kafa ta Afirka ta 20223, sannan ta kuma yi takara tare da Thembi Kgatlana (Afirka ta Kudu, Racing Louisbille) da kuma Barbara Banda (Zambia, Shanghai Shengli).

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Barcelona Na Shirin Ɗauko Victor Osimhen Na Galatasaray
Wasanni

Barcelona Na Shirin Ɗauko Victor Osimhen Na Galatasaray

October 30, 2025
Ina Fatan Buga Kofin Duniya Na 2026 — Messi
Wasanni

Ina Fatan Buga Kofin Duniya Na 2026 — Messi

October 28, 2025
El Classico: Abinda Ya Kamata Ku Sani Dangane Da Wasan Barcelona Da Real Madrid
Wasanni

El Classico: Abinda Ya Kamata Ku Sani Dangane Da Wasan Barcelona Da Real Madrid

October 26, 2025
Next Post
Kwamitin Kolin JKS Ya Gabatar Da Abubuwan Da Kasar Sin Za Ta Yi A Fannin Harkar Diplomasiyya A Shekarar 2024

Kwamitin Kolin JKS Ya Gabatar Da Abubuwan Da Kasar Sin Za Ta Yi A Fannin Harkar Diplomasiyya A Shekarar 2024

LABARAI MASU NASABA

CMG Ta Kammala Gabatar Da Rahoto Kan Ganawar Shugabannin Sin Da Amurka

CMG Ta Kammala Gabatar Da Rahoto Kan Ganawar Shugabannin Sin Da Amurka

October 31, 2025
Ministan Wajen Malawi: Tsarin Ci Gaban Kasar Sin Ya Samar Da Darussa Ga Kasashe Masu Tasowa

Ministan Wajen Malawi: Tsarin Ci Gaban Kasar Sin Ya Samar Da Darussa Ga Kasashe Masu Tasowa

October 31, 2025
Xi: A Shirye Sin Take Ta Hada Hannu Da Canada Wajen Mayar Da Dangantakarsu Bisa Turbar Da Ta Dace

Xi: A Shirye Sin Take Ta Hada Hannu Da Canada Wajen Mayar Da Dangantakarsu Bisa Turbar Da Ta Dace

October 31, 2025
Donald Trump Zai Gurfana A Gaban Kotu Kan Tuhumar Da Ake Masa

Trump Ya Ayyana Nijeriya A Matsayin Ƙasar Da Rayuwar Kiristoci Ke Cikin Hatsari

October 31, 2025
Yadda Waliyin Amarya Ya Sace Sadaki A Kano

An Tsare Wani Mutum A Gidan Yari Kan Zargin Kashe Matarsa Saboda Ƙuli-Ƙuli A Kano

October 31, 2025
Xi Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Kolin Shugabannin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

Xi Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Kolin Shugabannin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

October 31, 2025
Gwamna Uba Sani Ya Gabatar Da Kudirorin Raya Jihar Kaduna A Taron Ƙoli Na Biranen Asiya A Dubai 

Gwamna Uba Sani Ya Gabatar Da Kudirorin Raya Jihar Kaduna A Taron Ƙoli Na Biranen Asiya A Dubai 

October 31, 2025
Ya Kamata Sin Da Amurka Su Zama Kawayen Juna Ba Abokan Gaba Ba

Ya Kamata Sin Da Amurka Su Zama Kawayen Juna Ba Abokan Gaba Ba

October 31, 2025
Zaben 2027 Zai Kasance Ne Tsakanin Mulkin Tinubu Da Zabin Ƴan Nijeriya —Atiku Abubakar

Zaben 2027 Zai Kasance Ne Tsakanin Mulkin Tinubu Da Zabin Ƴan Nijeriya —Atiku Abubakar

October 31, 2025
Makarantar Kogi Poly Ta Bankaɗo Masu Ƙirƙirar Takardun Kammala Karatu na Bogi

Makarantar Kogi Poly Ta Bankaɗo Masu Ƙirƙirar Takardun Kammala Karatu na Bogi

October 31, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.