• English
  • Business News
Wednesday, September 10, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Bukaci Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Aikin Samar Da Wutar Lantarki Ta Mambila

by Muh'd Shafi'u Saleh
2 years ago
in Labarai
0
An Bukaci Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Aikin Samar Da Wutar Lantarki Ta Mambila
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamna Ahmadu Umaru Fintiri na jihar Adamawa, ya bukaci gwamnatin tarayya da ta gaggauta fara aikin samar da wutar lantarkin ta madatsar ruwan (Mambila Hydro Power Project) a jihar Taraba, domin samun ci gaba a yankin baki daya.

Ahmadu Umaru Fintiri, ya bayyana haka a lokacin da yake jawabi a bukin cika shekaru 10, na Mai Martaba Sarkin Mambila, Dakta Shehu Baju II, a karamar hukumar Sardauna ta jihar Taraba.

  • Samar Da Tsaro: Ribadu Ya Yaba Wa Sarakunan Gargajiya A Adamawa
  • Za Mu Garzaya Kotun Koli Don Daukaka Kara Kan Zaben Gwamnan Adamawa- APC

Gwamnan wanda shi ne shugaban taron, da ya samu wakilcin sakataren gwamnatin jihar Awwal Bamanga Tukur, ya jaddada mahimmancin irin wadannan ayyukan samar da wutar da cewa zai taimaka ga ababen more rayuwa da bunkasa tattalin arziki, da ma inganta rayuwar jama’a.

Gwamna Ahmadu Umaru Fintiri, ya yi kira ga al’ummar yankin Mambila da su rungumi zaman lafiya da hadin kai, tare da sanin muhimmancin zaman lafiya wajen samar da ci gaba a tsakanin al’umma.

Gwamna Fintiri ya jaddada muhimmancin hadin gwiwa da kokarin samar da ci gaba a tsakanin jihohin Adamawa da Taraba, ya kuma bayyana bukatar samar da ayyukan more rayuwa don bunkasa ci gaban yankin.

Labarai Masu Nasaba

INEC Ta Amince Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

An Ɗauke Wuta Sakamakon Lalacewar Babbar Tashar Lantarkin Nijeriya

A jawabinsa na fatan alheri a taron Sarkin Wukari, Aku Uka, wanda shi ne shugaban majalisar sarakunan gargajiyar jihar Taraba, Manu Ishaku, Ada Ali, ya bukaci mai masaukin biki da sarakunan gargajiya a jihar da su goyawa gwamnatin jihar baya wajen ganin an samar da zaman lafiya a jihar ya kuma yaba da goyon bayan da jama’ar masarautar ke baiwa masarautun gargajiya ta Mambila.

Da yake jawabin godiyar mai masaukin biki, Dakta Shehu Baju II, ya bayyana godiya da jin dadinsa ga duk wadanda suka bayar da gudumawa na ganin taron ya samu nasara, ya kuma yi godiya ta musamman ga hakimai da manyan baki, jama’a da masu hannu da shuni bisa goyon bayan da suka bayar.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AdamawaMambilaWutar Lantarki
ShareTweetSendShare
Previous Post

2024: Gwamnan Kebbi Ya Bukaci ‘Yan Nijeriya Su Yi Wa Kasa Addu’a Da Marawa Tinubu Baya

Next Post

Shugaban CMG Ya Aike Da Sakon Barka Da Sabuwar Shekara Ga Al’ummun Ketare

Related

INEC Ta Amince Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC
Manyan Labarai

INEC Ta Amince Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

32 minutes ago
An Ɗauke Wuta Sakamakon Lalacewar Babbar Tashar Lantarkin Nijeriya
Manyan Labarai

An Ɗauke Wuta Sakamakon Lalacewar Babbar Tashar Lantarkin Nijeriya

2 hours ago
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna
Labarai

Gwamnatin Kaduna Ta Umarci Makarantu Masu Zaman Kansu Da Su Nemi Amincewarta Kafin Ƙara Kuɗi

4 hours ago
Gwamnatin Tarayya Ta Yi Hasashen Ambaliyar Ruwa A Jihohin Arewa 15
Labarai

Yadda Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Yaya Da Ƙannuwa Da Wasu A Zaria

5 hours ago
Kwankwaso Ya Gana Da Shugabannin NNPP A Kuros Ribas Don Tunkarar Zaɓen 2027
Manyan Labarai

Kwankwaso Ya Gana Da Shugabannin NNPP A Kuros Ribas Don Tunkarar Zaɓen 2027

7 hours ago
Akwai Tara Mai Tsauri Ga Duk Wanda Ya Sare Bishiya Ba Bisa Ƙa’ida Ba – Gwamnatin Kano
Labarai

Akwai Tara Mai Tsauri Ga Duk Wanda Ya Sare Bishiya Ba Bisa Ƙa’ida Ba – Gwamnatin Kano

8 hours ago
Next Post
CMG

Shugaban CMG Ya Aike Da Sakon Barka Da Sabuwar Shekara Ga Al’ummun Ketare

LABARAI MASU NASABA

Tayar Da Yaki A Zamanin Nan Kauyanci Ne

Tayar Da Yaki A Zamanin Nan Kauyanci Ne

September 10, 2025
INEC Ta Amince Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

INEC Ta Amince Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

September 10, 2025
Sin Za Ta Kafa Yankin Kare Muhallin Halittu Na Huangyan Dao

Sin Za Ta Kafa Yankin Kare Muhallin Halittu Na Huangyan Dao

September 10, 2025
An Ɗauke Wuta Sakamakon Lalacewar Babbar Tashar Lantarkin Nijeriya

An Ɗauke Wuta Sakamakon Lalacewar Babbar Tashar Lantarkin Nijeriya

September 10, 2025
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamnatin Kaduna Ta Umarci Makarantu Masu Zaman Kansu Da Su Nemi Amincewarta Kafin Ƙara Kuɗi

September 10, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Yi Hasashen Ambaliyar Ruwa A Jihohin Arewa 15

Yadda Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Yaya Da Ƙannuwa Da Wasu A Zaria

September 10, 2025
Kwankwaso Ya Gana Da Shugabannin NNPP A Kuros Ribas Don Tunkarar Zaɓen 2027

Kwankwaso Ya Gana Da Shugabannin NNPP A Kuros Ribas Don Tunkarar Zaɓen 2027

September 10, 2025
Akwai Tara Mai Tsauri Ga Duk Wanda Ya Sare Bishiya Ba Bisa Ƙa’ida Ba – Gwamnatin Kano

Akwai Tara Mai Tsauri Ga Duk Wanda Ya Sare Bishiya Ba Bisa Ƙa’ida Ba – Gwamnatin Kano

September 10, 2025
majalisar kasa

Majalisa Ta Bai Wa Minista Sa’o’i 48 Ya Bayyana A Gabanta Kan Hatsarin Jirgin Abuja Zuwa Kaduna

September 10, 2025
Kasar Sin Ta Zama Dandalin Karfafa Cudanya Da Cinikayya Tsakanin Kasa Da Kasa

Kasar Sin Ta Zama Dandalin Karfafa Cudanya Da Cinikayya Tsakanin Kasa Da Kasa

September 9, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.