• English
  • Business News
Friday, September 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wang Yi: Manufar Sin Daya Tak A Duniya Ce Ta Tabbatar Da Kwanciyar Hankali A Mashigin Tekun Taiwan

by CMG Hausa
3 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Wang Yi: Manufar Sin Daya Tak A Duniya Ce Ta Tabbatar Da Kwanciyar Hankali A Mashigin Tekun Taiwan
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Mamban majalisar gudanarwar kasar Sin, kana ministan harkokin wajen kasar Wang Yi, ya bayyana a jiya cewa, manufar kasar Sin daya tak a duniya, ita ce ta tabbatar da zaman lafiya a mashigin tekun Taiwan.

Wang ya bayyana hakan ne a lokacin da aka tambaye shi, kan musabbabin tashin hankalin da ake fama da shi a mashigin tekun Taiwan da kuma yadda za a wanzar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a mashigin tekun na Taiwan, yayin da ya gabatar da jawabi game da manufofin kasar Sin game da nacewa kan bude yankin tare da amsa wasu tambayoyi a sakatariyar kungiyar kasashen ASEAN.

  • Kasar Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dauki Jerinta Da Muhimmanci

Da yake jaddada cewa, batun yankin Taiwan shi ne ginshikin babbar moriyar kasar Sin.

Wang Yi ya bayyana cewa, kiyaye ikon mulkin kasa da cikakkun yankuna, wani nauyi ne da ya rataya a wuyan duk wani Basine, kuma babu wani mutum, ko karfi ko wata kasa da za ta yi mafarkin raba yankin Taiwan da kasar Sin.

Wang ya ce, a baya-bayan nan, kasar Amurka ta sha jaddada cewa, za ta kiyaye ‘yancin kai da kuma yankunan kowace kasa, kuma kasar Sin tana mai da hankali sosai, kan yadda take martaba ka’idojin dangantakar kasa da kasa da manufofin MDD.

Labarai Masu Nasaba

Sin Ta Wanzar Da Ruhin Juriya Ta Hanyar Yakar Tafarkin Murdiya

An Kaddamar Da Cibiyar Raya Ilimin Dijital Ta Sin Da Afirka A Tanzania

Amma Wang Yi ya bayyana cewa, bisa la’akari da tarihin Amurka, a gefe guda, dole ne a jaddada cewa, bai kamata Amurka ta rika nuna fuska biyu, da yin kwangaba-kwan baya, da kuma sauya matsayinta ba.

A jawabin nasa, Wang ya ce, yankin Asiya yana cikin wani sabon matsayi na tarihi, yana kuma fuskantar damar samun ci gaba da ba a taba ganin irinsa ba. Kasar Sin ta zabi yin hadin gwiwa da mambobin kungiyar ASEAN da sauran kasashen yankin, don tsayawa tsayin daka kan manufar samun zaman lafiya, da ci gaba, da ‘yancin kai da kuma damawa da kowa.
Wang Yi ya ce, kamata ya yi kasashen Sin da Amurka, su kulla kyakkyawar mu’amala a yankin Asiya da tekun Pasifik. Yayin da aka tambaye shi game da yunkurin da Amurka da sauran kasashe ke yi na karfafawa da fadada karfinsu a yankin kuwa.

Ya jaddada cewa, babu wani abin kirki da ya wuce kasashen Sin da Amurka su cimma kyakkyawar mu’amala a yankin, wanda ba wai kawai zai taimaka wajen kara kyakkyawar fata ga kasashen biyu ba, har ma zai gamsar da tsammanin da baki dayan kasashen yankin ke yi. (Ibrahim)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kalubalen Rashin Tsaro: Ba Za Mu Kara Cewa Buhari Uffan Ba – ACF

Next Post

Gwamnatin Kano Ta Kwace Gurbatacciyar Fulawa Buhu 487

Related

Sin Ta Wanzar Da Ruhin Juriya Ta Hanyar Yakar Tafarkin Murdiya
Daga Birnin Sin

Sin Ta Wanzar Da Ruhin Juriya Ta Hanyar Yakar Tafarkin Murdiya

9 hours ago
An Kaddamar Da Cibiyar Raya Ilimin Dijital Ta Sin Da Afirka A Tanzania
Daga Birnin Sin

An Kaddamar Da Cibiyar Raya Ilimin Dijital Ta Sin Da Afirka A Tanzania

10 hours ago
Babban Sha’anin Dan Adam Na Wanzar Da Zaman Lafiya Da Ci Gaba Zai Samu Nasara
Daga Birnin Sin

Babban Sha’anin Dan Adam Na Wanzar Da Zaman Lafiya Da Ci Gaba Zai Samu Nasara

11 hours ago
Dakarun PLA Sun Gudanar Da Sintiri A Yankin Tekun Kudancin Sin
Daga Birnin Sin

Dakarun PLA Sun Gudanar Da Sintiri A Yankin Tekun Kudancin Sin

12 hours ago
Xi Ya Gana Da Shugaban Zimbabwe Da Na Jamhuriyar Kongo
Daga Birnin Sin

Xi Ya Gana Da Shugaban Zimbabwe Da Na Jamhuriyar Kongo

13 hours ago
Xi Jinping Ya Gana Da Kim Jong Un
Daga Birnin Sin

Xi Jinping Ya Gana Da Kim Jong Un

14 hours ago
Next Post
Gwamnatin Kano Ta Kwace Gurbatacciyar Fulawa Buhu 487

Gwamnatin Kano Ta Kwace Gurbatacciyar Fulawa Buhu 487

LABARAI MASU NASABA

Manzon Allah

Muna Murna Da Maulidin Cikar Manzon Allah (SAW) Shekara 1,500 Da Haihuwa (1)

September 5, 2025
Bukatar Dakatar Da Karuwar Hare-hare A Kan Likitoci – Ra’ayinmu

Barazanar Yajin Aiki: Likitoci Sun Bai Wa Gwamnati Wa’adin Kwana 10

September 5, 2025
Jami’ar Bayero Ta Yi Rashin Fitaccen Masanin Ilimin Harshe, Farfesa Hafizu Miko Yakasai

Jami’ar Bayero Ta Yi Rashin Fitaccen Masanin Ilimin Harshe, Farfesa Hafizu Miko Yakasai

September 5, 2025
Ministan Tsaro

Dawowar Matsalar Tsaro: Ta Haifar Da Cece-kuce Kan Daukar Matakin Kare Kai

September 5, 2025
Sin Ta Wanzar Da Ruhin Juriya Ta Hanyar Yakar Tafarkin Murdiya

Sin Ta Wanzar Da Ruhin Juriya Ta Hanyar Yakar Tafarkin Murdiya

September 4, 2025
An Kaddamar Da Cibiyar Raya Ilimin Dijital Ta Sin Da Afirka A Tanzania

An Kaddamar Da Cibiyar Raya Ilimin Dijital Ta Sin Da Afirka A Tanzania

September 4, 2025
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 13 A Wani Harin Kwanton-ɓauna A Borno

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 13 A Wani Harin Kwanton-ɓauna A Borno

September 4, 2025
Babban Sha’anin Dan Adam Na Wanzar Da Zaman Lafiya Da Ci Gaba Zai Samu Nasara

Babban Sha’anin Dan Adam Na Wanzar Da Zaman Lafiya Da Ci Gaba Zai Samu Nasara

September 4, 2025
Dakarun PLA Sun Gudanar Da Sintiri A Yankin Tekun Kudancin Sin

Dakarun PLA Sun Gudanar Da Sintiri A Yankin Tekun Kudancin Sin

September 4, 2025
Spence Na Dab Da Kafa Tarihin Zama Musulmi Na Farko Da Zai Buga Wa Ingila Ƙwallo

Spence Na Dab Da Kafa Tarihin Zama Musulmi Na Farko Da Zai Buga Wa Ingila Ƙwallo

September 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.