• English
  • Business News
Sunday, June 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tsadar Magunguna Na Barazana Ga Rayukan Majinyata A Nijeriya

by Khalid Idris Doya
1 year ago
in Labarai
0
Tsadar Magunguna Na Barazana Ga Rayukan Majinyata A Nijeriya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Labarai Masu Nasaba

Jirgin Alhazai Na Farko Ya Iso Jihar Jigawa

Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100

Kamuwa da rashin lafiya a Nijeriya ya zama kalubalen da za a iya cewa ruwan dare, amma samun jinya da magani kuma sai su zama babban kakanikayi sakamakon tsadar magunguna da ‘yan Nijeriya da dama ba su iya saye.

Tsadar magungunan musamman wadanda ake amfani da su yau da gobe irinsu rigakafi, maganin suga, ciwon kai, mura, maleriya da sauran cutukan da jama’a ke yawan fama da su na yau da kullum, abun da kawai majinyatan ke iyawa shi ne tururuwa zuwa asibitoci domin neman waraka.

  • Gwamnatin Zamfara Zata Raba Dabbobi Kyauta Ga Mata
  • Gwamnatin Zamfara Zata Raba Dabbobi Kyauta Ga Mata

Tsadar kayan magunguna babban barazana ne da ke fuskantar yawaitan zuwa asibitoci domin neman jinya, lamarin da ke neman a gaggauta daukan matakin shawo kansa domin kauce wa yawaitar mace-macen majinyata sakamakon rashin kudi ko kasa sayen magunguna.

Majinyata da dama sun nuna halin da suke ciki na mawuyacin yanayi musamman wadanda suke fama da karamin karfi kuma ba su cikin shirin inshuran kiwon lafiya, kamar wata uwa, Idowu Akinyemi wacce take fama da ciwon suga, ta shiga mamaki lokacin da ta je sayen magungunanta bisa gano yadda maganin ya yi tashin gwauron zabi farad daya.

“Lokacin da na sayi maganina na karshe shi ne, naira dubu 3,000, amma yanzu maganin da na je shagon sayar da magunguna ya kai naira 5,000,” Idowu ta nuna damuwarta kan tashin magungunan.

Dokun Bolarinwa, mai fama da ciwon hawan jini, ya ce, yana kan magani da jinya a kowani lokaci, amma tsadar magungunan sannu a hankali ya sanya shi kauce wa ka’ida da dokokin da likita ta dora shi a kai.

“Ni tsohon ma’aikaci ne ba na da wata hanyar samun kudi a kowani lokaci. ‘Yan shekaru, ina ta fama da jinyar da ke damuna tare da gudunmawar ahlina, amma a ‘yan kwanakin nan gaskiya lamuran sun mana wuya. Na koma tsallake ranakun shan magani domin ba mu iya sayen maganin a kowani lokaci.”

Ade Ogun, wanda ya sayo maganinsa, sai dai ransa a bace cikin damuwa yayin da ya gano cewa maganin da yake amfani da shi ya tashi, “Na sayi maganina a baya kan kudi naira 500, amma da na koma ya tashi da kaso 100, na yi matukar mamakin tashin maganin har haka,” Ade ya shaida.

Funmi Olaoye, matar aure ce wacce uwa ce kuma, da take jinyar danta mai fama da ciwon Asma, ta ce, “Yarona yana matukar bukatar kulawar magani kan ciwon asma da yake fama da shi, amma ba na iya sayen rashin maganin da ya dace na saya saboda tsada,” ta koka.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kofin Afirka 2023: Yadda Manyan Kasashe Ke Tafka Abin Kunya

Next Post

Kyan Alkawari Cikawa

Related

Jirgin Alhazai Na Farko Ya Iso Jihar Jigawa
Labarai

Jirgin Alhazai Na Farko Ya Iso Jihar Jigawa

23 minutes ago
Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100
Labarai

Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100

3 hours ago
Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki
Manyan Labarai

Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki

5 hours ago
Bashin Da Ake Bin Nijeriya Ya Kai Tiriliyan 46.25
Labarai

Za A Ci Gaba Da Tunawa Da Aminu Ɗantata A Ɓangaren Taimakon Jama’a — Buhari

20 hours ago
Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa
Manyan Labarai

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

20 hours ago
Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)
Labarai

Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

21 hours ago
Next Post
alkawari

Kyan Alkawari Cikawa

LABARAI MASU NASABA

Jirgin Alhazai Na Farko Ya Iso Jihar Jigawa

Jirgin Alhazai Na Farko Ya Iso Jihar Jigawa

June 29, 2025
Madarar Shanu Da Nijeriya Ke Samarwa Ta Karu Da Tan Miliyan 1.4 A Shekara Biyar

Madarar Shanu Da Nijeriya Ke Samarwa Ta Karu Da Tan Miliyan 1.4 A Shekara Biyar

June 29, 2025
Babu Irin Arziƙin Da Babu A Masana’antar Kannywood – Bashir Maishadda

Babu Irin Arziƙin Da Babu A Masana’antar Kannywood – Bashir Maishadda

June 29, 2025
Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100

Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100

June 29, 2025
Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki

Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki

June 29, 2025
Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

June 28, 2025
An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

June 28, 2025
Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

June 28, 2025
Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

June 28, 2025
Bashin Da Ake Bin Nijeriya Ya Kai Tiriliyan 46.25

Za A Ci Gaba Da Tunawa Da Aminu Ɗantata A Ɓangaren Taimakon Jama’a — Buhari

June 28, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.