• English
  • Business News
Wednesday, August 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tsadar Magunguna Na Barazana Ga Rayukan Majinyata A Nijeriya

by Khalid Idris Doya
2 years ago
in Labarai
0
Tsadar Magunguna Na Barazana Ga Rayukan Majinyata A Nijeriya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Tarayya Ta Dakatar Da Kafa Sabbin Manyan Makarantu Na Tsawon Shekaru 7

Majalisar Kano Ta Dakatar Da Shugaban Karamar Hukuma Bisa Zargin Kara Farashin Takin Gwamnati

Kamuwa da rashin lafiya a Nijeriya ya zama kalubalen da za a iya cewa ruwan dare, amma samun jinya da magani kuma sai su zama babban kakanikayi sakamakon tsadar magunguna da ‘yan Nijeriya da dama ba su iya saye.

Tsadar magungunan musamman wadanda ake amfani da su yau da gobe irinsu rigakafi, maganin suga, ciwon kai, mura, maleriya da sauran cutukan da jama’a ke yawan fama da su na yau da kullum, abun da kawai majinyatan ke iyawa shi ne tururuwa zuwa asibitoci domin neman waraka.

  • Gwamnatin Zamfara Zata Raba Dabbobi Kyauta Ga Mata
  • Gwamnatin Zamfara Zata Raba Dabbobi Kyauta Ga Mata

Tsadar kayan magunguna babban barazana ne da ke fuskantar yawaitan zuwa asibitoci domin neman jinya, lamarin da ke neman a gaggauta daukan matakin shawo kansa domin kauce wa yawaitar mace-macen majinyata sakamakon rashin kudi ko kasa sayen magunguna.

Majinyata da dama sun nuna halin da suke ciki na mawuyacin yanayi musamman wadanda suke fama da karamin karfi kuma ba su cikin shirin inshuran kiwon lafiya, kamar wata uwa, Idowu Akinyemi wacce take fama da ciwon suga, ta shiga mamaki lokacin da ta je sayen magungunanta bisa gano yadda maganin ya yi tashin gwauron zabi farad daya.

“Lokacin da na sayi maganina na karshe shi ne, naira dubu 3,000, amma yanzu maganin da na je shagon sayar da magunguna ya kai naira 5,000,” Idowu ta nuna damuwarta kan tashin magungunan.

Dokun Bolarinwa, mai fama da ciwon hawan jini, ya ce, yana kan magani da jinya a kowani lokaci, amma tsadar magungunan sannu a hankali ya sanya shi kauce wa ka’ida da dokokin da likita ta dora shi a kai.

“Ni tsohon ma’aikaci ne ba na da wata hanyar samun kudi a kowani lokaci. ‘Yan shekaru, ina ta fama da jinyar da ke damuna tare da gudunmawar ahlina, amma a ‘yan kwanakin nan gaskiya lamuran sun mana wuya. Na koma tsallake ranakun shan magani domin ba mu iya sayen maganin a kowani lokaci.”

Ade Ogun, wanda ya sayo maganinsa, sai dai ransa a bace cikin damuwa yayin da ya gano cewa maganin da yake amfani da shi ya tashi, “Na sayi maganina a baya kan kudi naira 500, amma da na koma ya tashi da kaso 100, na yi matukar mamakin tashin maganin har haka,” Ade ya shaida.

Funmi Olaoye, matar aure ce wacce uwa ce kuma, da take jinyar danta mai fama da ciwon Asma, ta ce, “Yarona yana matukar bukatar kulawar magani kan ciwon asma da yake fama da shi, amma ba na iya sayen rashin maganin da ya dace na saya saboda tsada,” ta koka.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kofin Afirka 2023: Yadda Manyan Kasashe Ke Tafka Abin Kunya

Next Post

Kyan Alkawari Cikawa

Related

Gwamnatin Tarayya Ta Dakatar Da Kafa Sabbin Manyan Makarantu Na Tsawon Shekaru 7
Manyan Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Dakatar Da Kafa Sabbin Manyan Makarantu Na Tsawon Shekaru 7

57 minutes ago
Majalisar Kano Na Shirin Zartar Da Dokar Gwajin Kwayoyin Jini, Kanjamau Da Cutar Hanta Kafin Aure
Manyan Labarai

Majalisar Kano Ta Dakatar Da Shugaban Karamar Hukuma Bisa Zargin Kara Farashin Takin Gwamnati

2 hours ago
NDLEA Ta Kama Dilolin Ƙwaya 49 A Kano
Labarai

NDLEA Ta Kama Dilolin Ƙwaya 49 A Kano

4 hours ago
Za Mu Nome Dazuka Don Magance Matsalar Tsaro A Neja – Bago
Manyan Labarai

Gwamnatin Neja Ta Tabbatar Da Kama Hatsabibin Ɗan Bindiga, Abubakar Abba

7 hours ago
ADC Ta Dakatar Da Shugabanta Da Wasu Jiga-jigai 3 A Kebbi
Labarai

ADC Ta Dakatar Da Shugabanta Da Wasu Jiga-jigai 3 A Kebbi

8 hours ago
An Kama Hakimi Kan Zargin Yi Wa ‘Yar Shekara 12 Fyaɗe A Gombe
Labarai

An Kama Hakimi Kan Zargin Yi Wa ‘Yar Shekara 12 Fyaɗe A Gombe

9 hours ago
Next Post
alkawari

Kyan Alkawari Cikawa

LABARAI MASU NASABA

Farfado Da Karkarar Sin: Canjin Gaisuwa Daga “Shin Ka Ci Abinci?” Zuwa “Yaya Rayuwarka A Gari?”

Farfado Da Karkarar Sin: Canjin Gaisuwa Daga “Shin Ka Ci Abinci?” Zuwa “Yaya Rayuwarka A Gari?”

August 13, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Dakatar Da Kafa Sabbin Manyan Makarantu Na Tsawon Shekaru 7

Gwamnatin Tarayya Ta Dakatar Da Kafa Sabbin Manyan Makarantu Na Tsawon Shekaru 7

August 13, 2025
Aikin Hakar Kwal Ta Hanyar Amfani Da Fasahar Zamani Ya Fara Wuce 50% a Kasar Sin

Aikin Hakar Kwal Ta Hanyar Amfani Da Fasahar Zamani Ya Fara Wuce 50% a Kasar Sin

August 13, 2025
Majalisar Kano Na Shirin Zartar Da Dokar Gwajin Kwayoyin Jini, Kanjamau Da Cutar Hanta Kafin Aure

Majalisar Kano Ta Dakatar Da Shugaban Karamar Hukuma Bisa Zargin Kara Farashin Takin Gwamnati

August 13, 2025
PLA Ta Kori Jirgin Ruwan Yakin Amurka Daga Yankin Ruwan Kasar Sin A Kusa Da Huangyan Dao

PLA Ta Kori Jirgin Ruwan Yakin Amurka Daga Yankin Ruwan Kasar Sin A Kusa Da Huangyan Dao

August 13, 2025
NDLEA Ta Kama Dilolin Ƙwaya 49 A Kano

NDLEA Ta Kama Dilolin Ƙwaya 49 A Kano

August 13, 2025
Za Mu Nome Dazuka Don Magance Matsalar Tsaro A Neja – Bago

Gwamnatin Neja Ta Tabbatar Da Kama Hatsabibin Ɗan Bindiga, Abubakar Abba

August 13, 2025
ADC Ta Dakatar Da Shugabanta Da Wasu Jiga-jigai 3 A Kebbi

ADC Ta Dakatar Da Shugabanta Da Wasu Jiga-jigai 3 A Kebbi

August 13, 2025
An Kama Hakimi Kan Zargin Yi Wa ‘Yar Shekara 12 Fyaɗe A Gombe

An Kama Hakimi Kan Zargin Yi Wa ‘Yar Shekara 12 Fyaɗe A Gombe

August 13, 2025
PDP Ta Soki Gwamnatin Tinubu Kan Tsare Tambuwal Da EFCC Ta Yi

Tambuwal: ’Yan Nijeriya Sun Soki EFCC Kan Rashin Kama Okowa, Ganduje Da Yahaya Bello

August 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.