• English
  • Business News
Monday, November 10, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Za Mu Tabbatar Kotu Ta Hukunta Dakataccen Kwamishinan Zaben Adamawa Hudu Ari -Fintiri

by Muh'd Shafi'u Saleh
2 years ago
Fintiri

Gwamna Ahmadu Umaru Fintiri, na jihar Adamawa, ya tabbatar wa al’ummar jihar kudurin da ya rataya a wuyan gwamnatinsa na ganin ta gurfanar da mutanen da suka hadabaki, da dakatacce kwamishinan hukumar zabe ta kasa (INEC) a jihar, Hudu Yunusa Ari, kan rawar da ya daka a babban zaben 2023.

Ahmadu Umaru Fintiri, ya bayyana haka lokacin da yake yiwa jama’ar jihar jawabi da aka watsa kai tsaye ta kafofin sadarwa ranar Litinin, ya ce “mu na iya mu kare tsarin zabenmu da dimokuradiyya daga cin zarafin da bai kamata ba.

  • Zaɓen Cike-gurbi: PDP Ta Lashe Zaɓen Ɗan Majalisar Jiha A Mazaɓar Mayo-Belwa A Adamawa
  • Hukuncin Zaben Adamawa: Na Rungumi Kaddara – Binani

“It’s kanta kotun Koli a cikin hukuncinta ta yi Allahwadai da matakin da Hudu Ari ya dauka, ta ce matsayin wani aiki ne na ‘rashin hankali da aikata laifuka’ wanda ya jefa harkar dimokradiyya cikin kunya.da dimauta” inji gwamnan.

Haka kuma gwamna Fintiri, ya nuna gamsuwa da yadda alkalai a matakai daban-daban na kotuna suka jajirce wajen warware rudun da’aka kawo a matakai daban-daban tare da fitar da hukuncin da ya dace da al’ummar jihar Adamawa.

Ya ce “hukuncin da kotun koli na ranar 31/01/2024, ya kawo karshen duk wata hayaniyar zaben 2023 a Adamawa, kwanakin karya da yaudara sun kare, lokacin farfagandar karya da maganganun son zuciya sun shude.

LABARAI MASU NASABA

NBA Ta Yi Allah Wadai Da Yadda Hukuncin Alƙalai Ke Karo Da Juna

Mataimakin Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kebbi Bagudo Ya Shaƙi Iskar ‘Yanci Daga ‘Yan Bindiga

“Dole na yabawa hukumar zabe INEC da ta tsaya tsayin daka ta kare mutumci da kimarta ta gujewa son zuciya, lokacin da Kwamishina Hudu Ari, ya aikata son zuciya da rashin bin ka’idar doka” inji Fintiri.

Gwamna Ahmadu Fintiri, ya ce duk da yanzu ba lokacin takara ba ne, amma jihar Adamawa jiha ce ta jam’iyyar PDP, kamar yadda aka gani lokacin zabuka da kuma a yadda ta kasance a kotuna, anga yadda mutanen suka yi magana da katunan zabe.

“Shaidar hakan ita ce sabuwar nasarar da PDP ta samu a zaben dan majalisar dokokin jiha mai wakiltar mazabar karamar hukumar Mayo-Belwa, mu na kara godiya ga masu kada kuri’a da suka kara sanya nasara a kan hukuncin da kotun koli ta yanke” ya jaddada.

Gwamna Ahmadu Fintiri, ya kuma baiwa jama’ar jihar tabbacin gwamnatinsa za ta ci gaba da musu hidima, tsare-tsare da kyautata rayuwa, ilimi kyauta, samar da kiwon lafiya, kayayyakin more rayuwa a birane da karkara, karfafa mata da matasa da sauransu.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

NBA Ta Yi Allah Wadai Da Yadda Hukuncin Alƙalai Ke Karo Da Juna
Labarai

NBA Ta Yi Allah Wadai Da Yadda Hukuncin Alƙalai Ke Karo Da Juna

November 9, 2025
Mataimakin Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kebbi Bagudo Ya Shaƙi Iskar ‘Yanci Daga ‘Yan Bindiga
Labarai

Mataimakin Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kebbi Bagudo Ya Shaƙi Iskar ‘Yanci Daga ‘Yan Bindiga

November 9, 2025
Soludo Ya Sake Lashe Zaɓen Gwamnan Anambra
Labarai

Soludo Ya Sake Lashe Zaɓen Gwamnan Anambra

November 9, 2025
Next Post
Kayayyaki Kirar Kasar Sin Na Samun Karbuwa Sosai A Kasashen Ketare

Me Ya Sa Babur Da Kasar Sin Ta Samar Yake Samun Karbuwa

LABARAI MASU NASABA

Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Na Ci Gaba Da Zama Muhimmin Ginshiki Ga Ci Gaban Nahiyar 

Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Na Ci Gaba Da Zama Muhimmin Ginshiki Ga Ci Gaban Nahiyar 

November 9, 2025
An Rufe Taron Kolin Wuzhen Na Ayyukan Yanar Gizo Na Duniya Na Shekarar 2025

An Rufe Taron Kolin Wuzhen Na Ayyukan Yanar Gizo Na Duniya Na Shekarar 2025

November 9, 2025
Katsina United Ta Shiga Komar Hukuncin Hukumar NPFL

Katsina United Ta Shiga Komar Hukuncin Hukumar NPFL

November 9, 2025
Xi Ya Gana Da Shugabar IOC Tare Da Shugaban IOC Na Karramawa

Xi Ya Gana Da Shugabar IOC Tare Da Shugaban IOC Na Karramawa

November 9, 2025
CMG Ya Cimma Yarjejeniyar Samun Iznin Watsa Shirye-shiryen Wasannin Olympics Daga Shekarar 2026 Zuwa 2032

CMG Ya Cimma Yarjejeniyar Samun Iznin Watsa Shirye-shiryen Wasannin Olympics Daga Shekarar 2026 Zuwa 2032

November 9, 2025
Kasar Sin Ta Yi Nasarar Harba Sabbin Taurarin Dan Adam Na Gwaji

Kasar Sin Ta Yi Nasarar Harba Sabbin Taurarin Dan Adam Na Gwaji

November 9, 2025
Shugaba Xi Ya Ayyana Bude Gasar Wasanni Ta Kasa Karo Na 15

Shugaba Xi Ya Ayyana Bude Gasar Wasanni Ta Kasa Karo Na 15

November 9, 2025
Mizanin Farashin Kayan Masarufi Na Kasar Sin Ya Karu Da 0.2% A Watan Oktoba

Mizanin Farashin Kayan Masarufi Na Kasar Sin Ya Karu Da 0.2% A Watan Oktoba

November 9, 2025
Me Ke Haddasa Yawaitar Farmakar Ƴan Wasa A Gasar Firimiyar Nijeriya

Me Ke Haddasa Yawaitar Farmakar Ƴan Wasa A Gasar Firimiyar Nijeriya

November 9, 2025
NBA Ta Yi Allah Wadai Da Yadda Hukuncin Alƙalai Ke Karo Da Juna

NBA Ta Yi Allah Wadai Da Yadda Hukuncin Alƙalai Ke Karo Da Juna

November 9, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.