• English
  • Business News
Friday, June 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zaben Fitar Da Gwani Na APC A Edo Ya Bar Baya Da Kura

by Yusuf Shuaibu
1 year ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
“‘Yan Siyasa Ne Aka Bai Wa Gidaje Ba Malaman Makaranta Ba A Kano”
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Zaben fid da gwani na jam’iyyar APC na kokarin fitar da dan takarar gwamna a zaben gwamnan Jihar Edo da zai gudana ranar 21 ga Satumba, ya bar baya da kura, inda a yanzu haka ‘yan takara uku ne ke ikirarin sun yi nasara.

Tun da farko dai, shugaban kwamitin zaben fitar da gwani na APC, Gwamna Hope Uzodinma ya ayyana dan majalisar wakilai, Dennis Idahosa a matsayin wanda ya yi nasara a Otel din Protea da ke Benin, yayin da babban jami’in da ke kula da zaben, Dakta Stanley Ugboaja ya bayyana Sanata Mondaya Okpebholo a matsayin wanda ya lashe zaben a gidan Fasto Osagie Ize-lyamu.

  • Blinken: Idan Ba Ka Da Karfi, Za A Cinye Ka
  • Gwamnatin Kaduna Ta Tabbatar Da Kashe Jagoran ‘Yan Ta’adda Boderi

Haka zalika, jami’an da suka kula da zaben fitar da gwanin na kanana hukumomi su ayyana Anamero Sundaya Dekeri a matsayin wanda ya yi nasara.

Mai magana da yawun jami’an da suka kula da zaben a kananan hukumomi, Ojo Babatunde, ya sanar da sakamakon zaben ne a daren Asabar, inda ya ce Dekeri wanda ya kasance dan majalisa da ke wakiltar Etsaro a zauren majalisar wakilan Nijeriya, ya samu kuri’u 25,384, wanda ya doke abokin takaransa da ke kusa da shi, Dennis Idahosa da kuri’u 14,127.

Da yake zantawa da manema labarai a Abuja, shugaban kungiyar masu ruwa da tsaki na APC, Emmanuel Godwin ya bayyana cewa Gwamna Uzodinma bai da hurumin daukan nauyin da ya rataya a kan jami’an da suka kula da zaben a kananan hukumomi.

Labarai Masu Nasaba

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin Fadar Shugaban Kasa Da Peter Obi Kan Tallafin Mai

Sauya Sheka Ya Sa APC Ta Samu Gagarumin Rinjaye A Majalisun Tarayya

Da yake mayar da martani kan wannan dambarwar, kwamitin gudanarwa na jam’iyyar APC ya dage cewa bisa doka kwamitin da gwamna Uzodinma ke jagoranta shi kadai ne ke da hurumin bayyana sakamakon zaben fitar da gwani  na APC  Jihar Edo.

Sakataren yada labarai na APC, Felid Morka ya bayyana cewa mutane su yi watsi da duk wani sakamakon da bai cika ka’ida ba.

“Kwamitin gudanarwa na kasa na wannan babbar jam’iyyarmu ya jawo hankalin kan sanar da sakamakon zaben fitar da gwani na APC a Jihar Edo, wanda wasu wadanda ba su da ikon yin haka suke ta yadawa a gidajen talabijin da rediyo da kuma kafafen sada zumunta.

“Muna sanar da cewa kwamitin da Gwamna Hope Uzodinma yake jagoranta ne kadai ke da hurumin bayyana sakamakon zaben fid da gwani na APC a Jihar Edo bisa tsarin doka.

“Muna kira da ‘ya’yan jam’iyyarmu na jihar da kuma sauran mutane cewa su yi watsi da duk wata sanarwa da ba ta cika ka’idar doka ba,” in ji shi.

Idan za a iya tunawa dai, shugaban jam’iyyar APC na kasa, Abdullahi Umar Ganduje ya kafa kwamitin da zai jagoranta zaben fitar da gwani karkashin shugabancin Gwamna Uzodinma a ranar Alhamis da ta gabata, inda ya ce, “Duk abin da wannan kwamitin ta zantar, to ‘yan takara suna da damar daukaka kara. Domin haka ne ma muke da kwamitin daukaka kara wanda ya kasance kamar kotun koli.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Firaministan Sin Ya Jagoranci Taron Majalisar Gudanarwar Kasar 

Next Post

Babban Jami’in JKS Ya Bukaci A Himmantu Wajen Ciyar Da Kokarin Dunkulewar Kasar Gaba 

Related

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin Fadar Shugaban Kasa Da Peter Obi Kan Tallafin Mai
Tambarin Dimokuradiyya

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin Fadar Shugaban Kasa Da Peter Obi Kan Tallafin Mai

2 weeks ago
APC
Tambarin Dimokuradiyya

Sauya Sheka Ya Sa APC Ta Samu Gagarumin Rinjaye A Majalisun Tarayya

2 weeks ago
Adawa
Tambarin Dimokuradiyya

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

3 weeks ago
‘Yancin Kananan Hukumomi: Shekara Daya Da Hukuncin Kotun Koli Amma Ba A Aiwatar Ba
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yancin Kananan Hukumomi: Shekara Daya Da Hukuncin Kotun Koli Amma Ba A Aiwatar Ba

4 weeks ago
Ko Kwamitin Saraki Zai Iya Ceto PDP Daga Rikicin Cikin Gida?
Tambarin Dimokuradiyya

Ko Kwamitin Saraki Zai Iya Ceto PDP Daga Rikicin Cikin Gida?

1 month ago
Tsadar Rayuwa Da Karuwar Ta’addanci Na Ci Gaba Da Tagayyara ‘Yan Nijeriya
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yan Adawa Na Cacakar APC A Yankin Arewa Maso Yamma Bisa Goyon Bayan Tazarcen Tinubu

1 month ago
Next Post
Babban Jami’in JKS Ya Bukaci A Himmantu Wajen Ciyar Da Kokarin Dunkulewar Kasar Gaba 

Babban Jami'in JKS Ya Bukaci A Himmantu Wajen Ciyar Da Kokarin Dunkulewar Kasar Gaba 

LABARAI MASU NASABA

Sojojin Sama Sun Yi Lugudan Wuta Kan Ƴan Ta’adda A Jihar Neja

Sojojin Sama Sun Yi Lugudan Wuta Kan Ƴan Ta’adda A Jihar Neja

June 27, 2025
2027: An Samu Ruɗani Kan Buƙatar Yi Wa ADA Rajista Don Ta Zama Jam’iyya

2027: An Samu Ruɗani Kan Buƙatar Yi Wa ADA Rajista Don Ta Zama Jam’iyya

June 27, 2025
Sarkin Yarbawan Funtuwa Ya Nemi A Daƙile Aiyukan Masu Ba ‘Yan Ta’adda Bayanan  Sirri

Sarkin Yarbawan Funtuwa Ya Nemi A Daƙile Aiyukan Masu Ba ‘Yan Ta’adda Bayanan  Sirri

June 27, 2025
Rundunar Sojin Nijeriya Ta Tabbatar Da Kisan Jami’anta A Kaduna Da Neja

Rundunar Sojin Nijeriya Ta Tabbatar Da Kisan Jami’anta A Kaduna Da Neja

June 27, 2025
Ziyarar Manzon Allah (SAW) A Madinah (3)

Ziyarar Manzon Allah (SAW) A Madinah (3)

June 27, 2025
Amince Wa Al’umma Mallakar Makamai Zai Ƙara Tsananta Rashin Tsaro — IGP

Amince Wa Al’umma Mallakar Makamai Zai Ƙara Tsananta Rashin Tsaro — IGP

June 27, 2025
Wata 6 Da Haramta Kauyawa Day A Kano: Badalar Na Ci Gaba Da Gudana 

Wata 6 Da Haramta Kauyawa Day A Kano: Badalar Na Ci Gaba Da Gudana 

June 27, 2025
Kasar Sin Ta Bayyana Adawa Da Yadda NATO Ta Yi Amfani Da Ita A Matsayin Dalilin Neman Fadada

Kasar Sin Ta Bayyana Adawa Da Yadda NATO Ta Yi Amfani Da Ita A Matsayin Dalilin Neman Fadada

June 26, 2025
Tinubu Ya Nemi Ƴan Nijeriya Su Taimaka A Yaƙi Shan Muggan Kwayoyi

Tinubu Ya Nemi Ƴan Nijeriya Su Taimaka A Yaƙi Shan Muggan Kwayoyi

June 26, 2025
An Yi Bikin Nune-Nunen Kayan Al’adu Na Murnar Cika Shekaru 55 Da Kulla Huldar Diflomasiyya Tsakanin Sin Da Italiya A Rome

An Yi Bikin Nune-Nunen Kayan Al’adu Na Murnar Cika Shekaru 55 Da Kulla Huldar Diflomasiyya Tsakanin Sin Da Italiya A Rome

June 26, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.