• English
  • Business News
Friday, July 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Taron LEADERSHIP: Moghalu Zai Yi Fashin Baki Kan Tattalin Arziki

by Sani Anwar
1 year ago
in Labarai
0
Taron LEADERSHIP: Moghalu Zai Yi Fashin Baki Kan Tattalin Arziki
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Tsohon Mataimakin Shugaban Babban Bankin Nijeriya, Farfesa Kingsley Moghalu, ya yi karin haske a kan abubuwan da zai yi fashin baki a kansu a wajen taron LEADERSHIP na mako mai zuwa, wanda za a gabatar a ranar Talata a matsayinsa na mai jawabi na musamman.

Har ila yau, tsohon mataimakin shugaban babban bankin, wanda ya rikide ya koma dan siyasa ya bayyana cewa, shi da sauran wadanda za su tofa albarkacin bakinsu a wajen taron, za su warware zare har abawa a kan al’amarin da ya shafi tabarbarewar tattalin arzikin wannan kasa da kuma wahalhalun da al’umma ke fama da su tare da mayar da hankali a kan zakulo hanyoyin magance matsalolin, musamman ganin yadda matsalar ke barazanar mamaye tattalin arzikin Afirka baki-daya.

  • Wa’adin Da Gwamna Kano Ya Dauka Na Yi Wa Kwamishinoni Hisabi Ya Cika: Kila Wasu Za Su Karbi Littafinsu A Hannun Hagu
  • Likitocin Saudiyya Sun Yi Nasarar Raba ‘Yan Biyun Da Aka Haifa Manne Da Juna A Kano

“A nawa ra’ayin, bai kamata mu dauki wadannan matsaloli da wasa ba, domin kuwa mutane na cikin halin kunci da yunwa; don haka mece ce mafita? Ina so kowa ya yi nasa tunanin a kan wannan kafin ranar da za a gudanar da wannan babban taro”, a cewar ta Moghalu.

Sannan, ya yi alkawarin yin tambayoyi a kan wannan matsala ta tabarbarewar tattalin arziki da ake fuskanta a halin yanzu tare da sanin hanyoyin da za a yi amfani da su wajen magance su.

“Haka zalika, akwai tambayoyi da dama da za su biyo baya a kan yadda za a warware wadannan matsaloli na tattalin arzikin kasa. Don haka, ya zama wajibi mu nemo amsoshinsu. Sannan, dole ne mu lalubo hanyoyin da za a samu mafita, amma ba ta hanyar ‘yan dabaru ba.

Labarai Masu Nasaba

Kayayyakin Sin Na Kara Samun Karbuwa A Kasuwar Duniya

Abba Ya Yi Sabbin Naɗe-naɗe A Jihar Kano

“Har wa yau, zan yi bayani a kan hanyoyin da ya kamata a bi, don fitar da Nijeriya daga wannan mummunan hali na tabarbarewar tattalin arziki; wanda ta samu kanta a ciki tare da hanyoyin da ya kamata a kirkiro, domin sama wa matasa ayyukan yi da kuma sake samun hanyoyin shigowar kudi da bunkasa tattalin arzikin ‘yan kasa baki-daya”, in ji shi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Wa’adin Da Gwamna Kano Ya Dauka Na Yi Wa Kwamishinoni Hisabi Ya Cika: Kila Wasu Za Su Karbi Littafinsu A Hannun Hagu

Next Post

Akwai Hannun Gwamnan Kano Wajen Fitar Da Murja Kunya Daga Gidan Gyaran Hali – Jaafar Jaafar

Related

Kayayyakin Sin Na Kara Samun Karbuwa A Kasuwar Duniya
Ra'ayi Riga

Kayayyakin Sin Na Kara Samun Karbuwa A Kasuwar Duniya

4 hours ago
Zabe: Gwamnatin Kano Ta Taƙaita Zirga-zirgar Mutane Da Ababen Hawa
Labarai

Abba Ya Yi Sabbin Naɗe-naɗe A Jihar Kano

5 hours ago
‘Yansanda Sun Kama Barayi 15, Sun Kwato Motocin Sata 20 A Kano
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama ’Yan Bindiga 17 Tare Da Kashe 3 A Abuja

5 hours ago
Haɗarin Da Ke Ƙunshe Da Jin Ɓangare Ɗaya Na Labari
Labarai

Haɗarin Da Ke Ƙunshe Da Jin Ɓangare Ɗaya Na Labari

6 hours ago
NUC Da Shugabannin Makarantu Sun Yi Kira A Sanya Tsarin Kere-kere A Jami’o’in Nijeriya
Labarai

NUC Da Shugabannin Makarantu Sun Yi Kira A Sanya Tsarin Kere-kere A Jami’o’in Nijeriya

7 hours ago
Neja: Cikin Wata 10 Ibtila’i Ya Lakume Rayuka Sama Da 400 – NSMA
Labarai

Neja: Cikin Wata 10 Ibtila’i Ya Lakume Rayuka Sama Da 400 – NSMA

8 hours ago
Next Post
Akwai Hannun Gwamnan Kano Wajen Fitar Da Murja Kunya Daga Gidan Gyaran Hali – Jaafar Jaafar

Akwai Hannun Gwamnan Kano Wajen Fitar Da Murja Kunya Daga Gidan Gyaran Hali - Jaafar Jaafar

LABARAI MASU NASABA

Shugaban Kwamitin AU: Kasar Sin Aminiya Ce Da Za A Iya Dogaro Da Ita

Shugaban Kwamitin AU: Kasar Sin Aminiya Ce Da Za A Iya Dogaro Da Ita

July 4, 2025
Yadda Taron Kungiyar Gwagwarmayar Talakawa Ta Kaya Kan Zaben 2023 A Zariya

INEC Ta Ayyana 16 Ga Agusta Don Gudanar Da Zaben Cike Gurbi A Jihohi 12

July 4, 2025
Ma’aikatar Cinikayya Ta Sin Ta Yi Karin Haske Game Da Soke Takunkumin Da Amurka Ta Kakabawa Sin

Ma’aikatar Cinikayya Ta Sin Ta Yi Karin Haske Game Da Soke Takunkumin Da Amurka Ta Kakabawa Sin

July 4, 2025
Ganduje Na Kara Shan Matsin Lamba A Kan Ya Sauka

APC: Ko Sadaukarwar Ganduje Za Ta Dakile Barazanar Jam’iyyun Adawa A Zaben 2027?

July 4, 2025
Sin Da Ghana Za Su Karfafa Hadin Gwiwarsu

Sin Da Ghana Za Su Karfafa Hadin Gwiwarsu

July 4, 2025
Zaben Gwamnoni: Za Mu Ba Marada Kunya – INEC

2027: Kungiyoyi 110 Ne Ke Neman Rajistan Zama Jam’iyyun Siyasa A Yanzu Haka – INEC

July 4, 2025
Sin: Tsawaitar Rikicin Ukraine Ba Zai Amfani Kowa Ba

Sin: Tsawaitar Rikicin Ukraine Ba Zai Amfani Kowa Ba

July 4, 2025
Lardin Hainan Na Kasar Sin Ya Samu Karuwar Cinikayyar Hajoji Da Aka Daukewa Haraji Cikin Shekaru Biyar

Lardin Hainan Na Kasar Sin Ya Samu Karuwar Cinikayyar Hajoji Da Aka Daukewa Haraji Cikin Shekaru Biyar

July 4, 2025
Kayayyakin Sin Na Kara Samun Karbuwa A Kasuwar Duniya

Kayayyakin Sin Na Kara Samun Karbuwa A Kasuwar Duniya

July 4, 2025
Zabe: Gwamnatin Kano Ta Taƙaita Zirga-zirgar Mutane Da Ababen Hawa

Abba Ya Yi Sabbin Naɗe-naɗe A Jihar Kano

July 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.