• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shugaba Tinubu Ya Dawo Abuja Daga Qatar

by Sulaiman
1 year ago
in Labarai
0
Shugaba Tinubu Ya Dawo Abuja Daga Qatar
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban Ƙasa Bola Tinubu ya sauka Abuja bayan ziyarar aiki ta kwanaki biyu da ya kai a ƙasar Ƙatar.

Jirgin shugaban ƙasa, mai lamba NAF 001, ya sauka a Filin Jirgin Sama na Nnamdi Azikiwe da misalin ƙarfe 7 na dare.

  • Nijeriya Da Qatar Sun Rattaba Hannu Kan Yarjeniyoyi Daban-Daban
  • Ramadan: Sanata Abdulaziz Yari Zai Raba Tirela 358 Na Kayan Abinci A Jihar Zamfara

Tinubu ya kammala ziyararsa zuwa ƙasashen waje karo na 12 tun bayan da ya karɓi ragamar shugabancin ƙasar watanni tara da suka gabata, kuma ya yi kwana 75 a ƙasashen waje.

Tinubu ya samu tarba daga manyan jami’an gwamnati da suka haɗa da Mataimakin Shugaban Ƙasa Kashim Shettima; Shugaban Ma’aikatan sa, Femi Gbajabiamila; Sakataren Gwamnatin Tarayya, George Akume; Ministan Babban Birnin Tarayya, Nyesom Wike; Shugaban jam’iyyar APC, Abdullahi Ganduje; da Darakta Janar na Hukumar Tsaro, Yusuf Bichi, da dai sauran su.

A ranar farko ta ziyarar tasa, shugaban na Nijeriya ya ziyarci gidan adana kayan tarihi na Ƙatar inda ya jaddada muhimmancin rubuta sahihin bayanan tarihin ƙasa, da al’adu, da cigaba, da ƙalubale.

Labarai Masu Nasaba

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

Da yake rangaɗin jibgegen ginin wanda ya kai murabba’in mita 39,994 da ke kewaye da asalin fadar Sheikh Abdullah bin Jassim Al-Thani, shugaban ya ce, “Yana da kyau a rubuta al’adu tun farkon tarihi, al’adun wayewa, haɗin gwiwa, ƙalubale da jajircewar shugabanci.”

Washegari, Tinubu tare da Sarkin Ƙatar, Sheikh Tamim bin Hamad Al Thani sun shaida rattaba hannu kan wasu muhimman yarjejeniyoyi guda bakwai a tsakanin ƙasashen biyu, bayan ganawar sirri da suka yi a fadar shugaban ƙasa dake Doha.

Sun haɗa da: yarjejeniyar haɗin gwiwa a fagen ilimi; sanya ƙa’idojin ɗaukar ma’aikata tare da gwamnatin Ƙatar; kafa majalisar hada-hadar kasuwanci tsakanin Ƙungiyar ‘Yan Kasuwa da Masana’antu ta Ƙatar da Ƙungiyar ‘Yan Kasuwa da Masana’antu da Ma’adinai da Noma ta Najeriya; baya ga yarjejeniyar haɗin gwiwa a fagen matasa da wasanni.

Sauran yarjejeniyoyin sun haɗa da haɗin gwiwa a fannin yawon buɗe ido da harkokin kasuwanci, da kuma yarjejeniyar fahimtar juna da ke yaƙi da haramtacciyar fataucin miyagun ƙwayoyi.

Ministan Harkokin Waje, Yusuf Tuggar, da jami’an gwamnatin Ƙatar, Buthaina bint Ali Al Jabr Al Nuaimi, Ministar Ilimi da Ilimi Mai Zurfi; Dr. Ahmad Hassen Al-Hammadi, Babban Sakataren Ma’aikatar Harkokin Waje; Sheikh Khalifa Bin Jassim Al Thani, Shugaban Cibiyar Kasuwanci da Masana’antu ta Ƙatar da Abdullah bin Khalaf bin Hattab Al Kaabi, Mataimakin Sakatare na Ma’aikatar Cikin Gida ne suka sanya hannu kan takardun.

A ranar Lahadi ne Tinubu ya jagoranci Taron Kasuwanci da Saka Hannun Jari na Najeriya da Ƙatar inda ya buƙaci shugabannin masana’antu na Ƙatar da su kai rahoton duk wani jami’in Najeriya da ya nemi cin hanci kafin a bar su su yi kasuwanci a ƙasar.

Ya nanata cewa Najeriya ba zai ƙi cigaba ba saboda abubuwan da suka faru a baya da ke cike da jinkiri na gwamnati da cin hanci da rashawa da ke daƙile sauƙin kasuwanci.

“Kada ku ba da cin hanci ga kowa daga cikin jama’armu. Za ku sami damar zuwa gare ni, ” inji Tinubu.

Shugaban ya kuma tabbatar wa da ‘yan kasuwar duniya cewa Nijeriya a shirye take ta gudanar da harkokin kasuwanci da gaske domin gwamnatin sa za ta yi maganin duk wata maslaha a ƙasar da ke kawo cikas ga masu zuba jari a tattalin arziƙin Najeriya.

Ya kuma yi alƙawarin kawar da duk wasu matsaloli da ke kawo cikas ga harkokin kasuwanci yana mai cewa, “Kada ku bari hasashe ya zama cikas ga shirin ku na saka hannun jari. Nijeriya da gaske take game da kawo sauyi a fannin zuba jari.”

Ƙatar dai ita ce ƙasa ta uku a yankin Gulf da Tinubu ya kai ziyara tun bayan da ya ɗare kujerar shugabancin ƙasar da kuma ziyarar sa ta 16 a ƙasashen waje.

Ya zuwa yanzu, ya ziyarci birnin Paris na ƙasar Faransa (sau uku); Landan, Birtaniya; Bissau, Guinea-Bissau (sau biyu); Nairobi, Kenya; Porto Norvo, Jamhuriyar Benin; New Delhi, Indiya; Abu Dhabi da Dubai a Haɗaɗɗiyar Daular Larabawa; New York, Amurka, Riyadh, Saudi Arabia, Berlin, Jamus da Addis Ababa, Habasha.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Gwamnatin shugaba TinubuZiyarar Aiki
ShareTweetSendShare
Previous Post

Labaran Karyar Cewa “Tattalin Arzikin Sin Na Dakushewa” Ba sa Tasiri A zukatan Jama’a 

Next Post

Birnin Beijing Na Shirin Samar Da Karin Masana’antu Da Wuraren Kere-kere Masu Amfani Da Fasahohin Zamani 100

Related

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya
Manyan Labarai

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

2 hours ago
2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC
Labarai

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

5 hours ago
Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi
Labarai

Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

5 hours ago
Daurarru
Labarai

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

15 hours ago
Wutar lantarki
Labarai

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

17 hours ago
Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka
Labarai

Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

18 hours ago
Next Post
Birnin Beijing Na Shirin Samar Da Karin Masana’antu Da Wuraren Kere-kere Masu Amfani Da Fasahohin Zamani 100

Birnin Beijing Na Shirin Samar Da Karin Masana’antu Da Wuraren Kere-kere Masu Amfani Da Fasahohin Zamani 100

LABARAI MASU NASABA

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

June 7, 2025
Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

June 7, 2025
Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

June 7, 2025
Neja

Dalilin Rashin Fara Aikin Kamfanin Takin Zamani Na Gwamnatin Jihar Neja

June 7, 2025
Adawa

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

June 7, 2025
2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

June 7, 2025
Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

June 7, 2025
Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

June 6, 2025
Daurarru

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.