• English
  • Business News
Wednesday, September 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yawaitar Hare-haren ‘ Yan Bindiga A Jihar Kaduna…

by Shehu Yahaya
1 year ago
in Manyan Labarai
0
Yawaitar Hare-haren ‘ Yan Bindiga A Jihar Kaduna…
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Labarai Masu Nasaba

Sojoji Sun Kashe Mayaƙan ISWAP 11 A Borno Da Adamawa

Sowore Ya Maka DSS, Meta da X A Kotu Kan Take Masa Haƙƙi

Al’ummar Jihar Kaduna na ci gaba da zaman zulumi; bisa karuwar rashin tsaro, lamarin da ya tilasta wa wasu barin garuruwansu ba tare da sun shirya ba.

Masana harkokin tsaro sun bayyana cewa, karshen ‘yan ta’adda ne ya zo, musamman ganin yadda jami’an tsaron Nijeriya suka datse hanyoyin da ke da hadaka da junansu a dazukan da suke zama da kuma karancin makamai da suke fama da shi yanzu.

  • Sin Za Ta Inganta Zamanintarwa Bisa Bunkasuwa Mai Inganci Don Ba Da Karin Karfi Ga Ci Gaban Duniya
  • Majasirdin Sarkin Zazzau, Alhaji Yusuf Saleh Barde Ya Rasu

Hasali ma sun bayyana cewa, yawaitar garkuwa da mutane a Jihar Kaduna, wata alamace da ke nuna cewa kwanakin ‘yan ta’addan sun zo karshe a jihar kamar yadda suka shaida wa LEADERSHIP Hausa.

Har ila yau kuma, wasu na ganin Gwamnatin Jihar Kaduna; karkashin jagorancin Sanata Uba Sani, na da matukar sassaucin ra’ayi wajen yaki da wadannan ‘yan ta’adda, sabanin gwamnatin da ta shude ta Malam Nasiru El-Rufa’i; wacce ta rika yin fito-na-fito da masu tayar da kayar-baya a jihar.

Wakilinmu, ya yi kokarin jin ta bakin Kwamishinan Ma’aikatar Tsaro da Lamuran Cikin Gida na Jihar Kaduna, Samuel Aruwa, domin jin irin matakan da suke dauka wajen samar da tsaro a fadin jihar, amma abin ya ci tura. Duk da haka, wakilinmu bai yi kasa a guiwa ba; domin kuwa ya tura masa sakon tes, bai ba da amsa ba, haka nan kuma ya kai ziyara ofishinsa; nan ma bai samu damar ganawa da shi ba.

A wata ganawa da hukumomin tsaro a jihar ta Kaduna kwanan na, Gwamna Uba Sani ya yi kira da a kaddamar da tsarin tsaro na bai-daya, ta hanyar inganta cudanya da jama’a gami da wayar da kan al’ummar; kan muhimmacin samar da tsaro.

Bugu da kari, Gwamna Uba Sani ya sha alwashin samar da dukkanin kayan aikin da suka dace ga hukumomin na tsaro, domin samun damar gudanar da ayyukansu yadda ya kamata a fadin jihar ta Kaduna baki-daya.

A zantawarsa da wakilinmu,  Dakta Yahuza Getso; masanin tsaro a Nijeriya da kasashen Afirka ya bayyana cewa, matsalar rashin tsaro a Jihar Kaduna; abubuwa ne guda hudu: “Abu na farko shi ne, dole ne sai jami’an tsaro sun tashi tsaye wajen tabbatar da dakatar da wadannan hare-hare da ake kaiwa, duk kuwa da cewa; jami’an tsaron suna yi bakin kokarinsu wajen kai hari ga ‘yan ta’addan, wanda hakan ya sanya su kuma ‘yan ta’addan suka tunzura tare da kai hare-hare a kan al’ummar da ba su ji ba, ba su kuma gani ba.

“Abu na biyu shi ne, akwai abin da masu iya magana ke cewa,  ‘Tusa ta kusa kure wa Bodari’, dalili kuwa, yanzu haka karfin wadannan ‘yan ta’adda ya yi matukar raguwa, sakamakon hana shiga da kayan masarufi na rayuwa da kuma takura musu da aka yi wajen ci gaba da samun makaman da suke yin ta’addanci da su, saboda idan ka dubi irin yadda suke kawo hare-hare a halin yanzu, ba sa zuwa da makamai duk da cewa suna diban mutane da dama.

“Abu na uku kuma shi ne, jami’an tsaro sun datse hanyoyin da suke samun hadaka da junansu, inda suke kai komo a cikin dazukan, saboda haka; sai suke ganin babu wata mafita sai dai su rika daukar mutane masu yawa, wanda hakan zai jawo hankalin hukumomi ko da za a kai musu hari; za a koma tunanin cewa akwai wasu mutane masu a tare da su masu yawan gaske, don haka wajibi ne a daga kafa wajen kai musu farmaki.

“Kazalika, abu na hudu shi ne;  idan aka ci gaba da samun bayanai daga al’umma, babu shakka jami’an tsaron sojojin wannan kasa, za su kakkabe kafatanin wAdannan ‘yan ta’adda.

“Batun da suke yi yanzu na neman kudin fansa, wanda kowa ya sani cewa ya wuce hankali, abu ne wanda suke yi domin kara razana al’umma da kuma jefa musu zaman zuLlumi, amma su shugabannin jami’an tsaron Nijeriya, suna kara samun kaimi ne idan suka ji ‘yan ta’addan na neman irin wadannan makudan mudade, wanda hakan ke nuna cewa; lallai karfinsu ya fara karewa; suna neman kudin sayen makamai da sauran makamantansu”.

“Saboda haka, mafita kadai yanzu ita ce; shugabanni su kara jin tsoron Allah, sannan kuma su tuna irin nauyin da Allah ya dora musu, wanda zai tambaye su wata rana. Haka nan, su ma jami’an tsaron; su kara kaimi tare da sanin cewa, wannan yaki da suke yi da ‘yan ta’adda; wata rana ko shakka babu za a kai ga cimma gaci. Saboda haka, ka da su samu sanyin guiwa a kan irin fadi tashin da ake yi, sannan kuma dole ne a kara dankon zumunta tre da fahimtar juna a tsakanin jami’an tsaro da sauran al’umma, wanda hakan zai taimaka wajen samun bayanan sirri da kuma sa ido, domin kara taimakawa wajen samun nasarar yakin da ake yi wajen kawar da wadannan ‘yan ta’adda a fadin yankin baki-daya”, in ji Dakta Getso.

A nashi bangaren, Malam Muhammad Garba, Tsohon Malamin Makaranta ne a Kwalejin Kimiyya da Fasaha ta Gwamnatin Tarayya da ke Kaduna, sannan kuma mai yin fashin baki a kan harkokin siyasar ta Jihar Kaduna ya bayyan cewa, akwai hasashen da ake yi cewa, Gwamnatin Uba Sani; na da sassauci a kan harkokin tsaro, lamarin da ake ganin shi ne silar samun yawaitar matsalar rashin tsaron a fadin jihar.

“Lokacin Tsohon Gwamnan Jihar Kaduna, Malam Nasiru El-Rufa’i; ya hana kowa sakat, domin kuwa ya yi amfani da wasu bangarori na jami’an tsaro tare da sa ido a kowane lungu da sako, ya kuma kokarin tarwatsa wadannan ‘yan ta’adda; har sai da ta kai ga babu wani mai iya yin  motsi a jihar.

Wannan dalili ne, ya sa aka samu saukin yawaitar ire-iren wadannan hare-hare na ‘yan ta’adda a fadin jihar, amma yanzu ana ganin wannan gwamnatin ta Uba Sani, tana da matukar sassauci;” in ji shi.

Jibrin Aliyu Kuriga (Dan Bala), mazaunin garin Kuriga ne da ke cikin Karamar Hukumar Chikun da ke Jihar Kaduna, ya bayyana cewa, shi ne mutum na farko da ‘yan bindigar suka fara yin garkuwa da shi a tarihin wannan gari, inda ya kwashe kimanin kwanaki 53 a hannunsu; kafin da aka biya kudin fansa ya shaki iskar ‘yanci, a cewar tasa; “Wallahi cikin kwanaki 53 da na kwashe a hannunsu, ban taba sa ruwa na wanke fuskata da shi ba; haka nan duk hannayena sun sha duka, wanda ban taba tunanin za su ci gaba da aiki a gaba ba”.

 “Mu tara aka kwashe, amma bayan an yi sulhu da ‘yan bindigar daga baya sai suka sako mutum biyar; sauran hudun kuma suka kashe su. Saboda haka, mu al’ummar Jihar Kaduna; musamman mu da muke yin rayuwa a wajen jihar, shakka babu rayuwarmu na cikin wani mayuwacin hali na zaman zulumi, bisa wannan matsalar ta rashin tsaro da muke fama da ita,” a ta bakinsa.

Wani mai sana’ar sayar da Gawayi a Jihar Kaduna, Malam Abdulkarim Jibrin, ya bayyana cewa,  ko shakka babu rashin tsaro ya shafi sana’ar kasuwancinsu, musamman su da suke shiga kauyuka suna gudanar da kasuwancinsu, wanda a halin yanzu ‘yan ta’adda duk sun ta da wadannan kauyuka baki-daya.

“Duk inda za ka je ka sayo itace da gawayi, yanzu babu sakamakon tashin kauyakan da ‘yan ta’addar suka yi, sannan kuma ai duk garin da a yau aka ce babu kauye, ya zama nakasasshe komai girmansa. Mu dai yanzu, wanzuwar ‘yan bindiga ya taba rayuwarmu da ta iyalinmu “.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kisan Gillar Sojoji 17: Tinubu Ya Shafa Wa Idonsa Toka, Sojoji Sun Kai Mamaya

Next Post

Falalar Azumi Da Yadda Yake Sa Tsoron Allah

Related

Sojoji Sun Kashe Mayaƙan ISWAP 11 A Borno Da Adamawa
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kashe Mayaƙan ISWAP 11 A Borno Da Adamawa

34 minutes ago
Sowore Ya Maka DSS, Meta da X A Kotu Kan Take Masa Haƙƙi
Manyan Labarai

Sowore Ya Maka DSS, Meta da X A Kotu Kan Take Masa Haƙƙi

5 hours ago
Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Aka Yi Wa Sharrin Safarar Ƙwayoyi
Manyan Labarai

Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Aka Yi Wa Sharrin Safarar Ƙwayoyi

6 hours ago
NSCDC Za Ta Fara Sanyan Ido Kan Muhimman Abubuwan More Rayuwa A Jihar Kano
Manyan Labarai

NSCDC Za Ta Fara Sanyan Ido Kan Muhimman Abubuwan More Rayuwa A Jihar Kano

20 hours ago
DSS Ta Maka Sowore, Facebook Da X A Kotu Kan Wallafa Rubutu Game Da Tinubu
Da ɗumi-ɗuminsa

DSS Ta Maka Sowore, Facebook Da X A Kotu Kan Wallafa Rubutu Game Da Tinubu

23 hours ago
Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Yi Wa Hakimi Yankan Rago A Zamfara

1 day ago
Next Post
Falalar Azumi Da Yadda Yake Sa Tsoron Allah

Falalar Azumi Da Yadda Yake Sa Tsoron Allah

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kashe Mayaƙan ISWAP 11 A Borno Da Adamawa

Sojoji Sun Kashe Mayaƙan ISWAP 11 A Borno Da Adamawa

September 17, 2025
‘Yan Bindiga Sun Sace Mutum 7 A Jihar Neja

‘Yansanda Sun Kama ‘Yan Ƙungiyar Asiri Da Ɓarayin Kifi A Jihar Neja

September 17, 2025
Mataimakin Shugaban Jam’iyyar APC Na Nasarawa, Aliyu Barde, Ya Rasu

Mataimakin Shugaban Jam’iyyar APC Na Nasarawa, Aliyu Barde, Ya Rasu

September 17, 2025
Sowore Ya Maka DSS, Meta da X A Kotu Kan Take Masa Haƙƙi

Sowore Ya Maka DSS, Meta da X A Kotu Kan Take Masa Haƙƙi

September 17, 2025
Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Aka Yi Wa Sharrin Safarar Ƙwayoyi

Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Aka Yi Wa Sharrin Safarar Ƙwayoyi

September 17, 2025
Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo

Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo

September 16, 2025
Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani

Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani

September 16, 2025
Sauye-sauyen Manufofin Gwamnati Na Iya Hana Masu HND Zuwa NYSC

An Yi Garkuwa Da Wani Mai Hidimar Ƙasa Da Ɗalibi A Jos

September 16, 2025
Sin Da Amurka Sun Yi Tattaunawar Keke-da-keke Kan Batutuwan Cinikayya Da Manhajar TikTok

Sin Da Amurka Sun Yi Tattaunawar Keke-da-keke Kan Batutuwan Cinikayya Da Manhajar TikTok

September 16, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa

September 16, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.