• English
  • Business News
Tuesday, August 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Yi Garkuwa Da Dalibai 1,680 Da Kashe 180 Cikin Shekara 10 A Nijeriya – UNICEF

by Idris Aliyu Daudawa
1 year ago
in Labarai
0
An Yi Garkuwa Da Dalibai 1,680 Da Kashe 180 Cikin Shekara 10 A Nijeriya – UNICEF
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Asusun kula da yara na Majalisar Dinkin Duniya (UNICEF) ya bayyana cewa an yi garkuwa da yara 1,680 yayin da kuma 180 daga cikinsu an kashe su ne tun lokacin da aka fara garkuwa da ‘yan makarantar mata a Nijeriya a shekarar 2014.

Wani sabon rahoton da asusun ya fitar na cewa kashi 37 ne kawai na makarantu daga jihohi 10 aka bayyana masu alamu masu tayar da hankali don su gane kamar kawo wa makaranta hari.

  • Sauyin Yanayi: Dabarun Da  Za Su Taimaka Wa Masu Kiwon Kifi
  • An Lalata Haramtattun Rijyoyin Mai 7 Da Jiragen Ruwa 4 A Ribas

Hakan yana kasancewa ne yayin da Nijeriya cika shekara 10 tun lokacin da aka fara garkuwa da ‘yan makaranta masu yawa, inda ‘yan mata 91 a Arewa maso gabas har yanzu ana ci gaba da garkuwa da su,yayin da Nijeriya ke kara shiga wani alhini na ‘yan makarantar Kaduna wanda aka yi a watan Maris na wannan shekarar.

UNICEF ya yi kira da a daukai matakan da suka dace wajen kare kananan yara wadanda sune abin ya fi shafa.

“Dauka da garkuwa da ‘yan matan a makarantar Chibok wani jirwaye mai kamar wanka ne, mai nuna irin hadarin da yara ke shiga a kokarin da suke wajen neman Ilimi,”Ms Cristian Munduate wakiliyar UNICEF a Nijeriya ta ce lokacin da ake gabatar da rahoton a ofishin Majalisar Dinkin Duniya.

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Tarayya Ta Sake Gargadin Jihohin Arewa 9 Kan Afkuwar Ambaliya 

ECOWAS Za Ta Kaddamar Da Rundunar Yaki Da Ta’addanci Mai Jami’ai 260,000

Ta ce a yau da ake tunawa da abin bakincikin na garkuwar da aka yi a sassa daban-daban na Nijeriya, “Hakan wata manuniya ce a kokarin da muke yi  domin kare lafiyar ‘ya’yanmu”.Wadannan alkalumma masu ta da hankali ba wai za mu tsaya kan alamu ba har ma abubuwan da suke sa ana samun su tashin hankalin da kan shiga.

“Ilimi wata dama ce da ake bi domin fita daga fatara, sai dai duk da hakan yawan kananan yara a Nijeriya har yanzu sun kasa cimma burinsu.

“Abin ya taso ne bayan wasu bayanai da aka samu na rahotanni masu ta da hankali na tashe- tashen hankula a makaranta da suka shafi garkuwa da dalibai lamarin da yake karuwa.

“Shekaru 10 da suka wuce an samu yin garkuwa da yara 1,680 lokacin da suke makaranta da wasu wurare, an kuma kashe 180 saboda harin da ake ka iwa makarantu, inda aka kiyasta an yi garkuwa da malamai 60 aka kashe 14, fiye da hari 70 da aka kai wa makarantu kamar yadda rahoton da aka tabbatar da sahihanci shi na Majalisar Dinkin Duniya ya bayyana.”

Babbar jami’ar Ilimi, Saadhna Panday-Soobrayan ta bayyana haka ne a ofishin hukumar UNICEF lokacin da take bayar da rahoto a Nijeriya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Tarkunan Da Aka Dana Wa Ganduje A Kano

Next Post

Halaye 8 Na Rayuwa Da Aka Fi So A Yi Shiru Maimakon Magana A Ciki (1)

Related

Gwamnatin Tarayya Ta Yi Hasashen Ambaliyar Ruwa A Jihohin Arewa 15
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Sake Gargadin Jihohin Arewa 9 Kan Afkuwar Ambaliya 

7 hours ago
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 3 Da Kubutar Da Mutum 16 Da Aka Sace A Kaduna
Labarai

ECOWAS Za Ta Kaddamar Da Rundunar Yaki Da Ta’addanci Mai Jami’ai 260,000

8 hours ago
Mauludi: Gwamnatin Kano Ta Sake Ɗage Ranar Komawa Makarantu
Manyan Labarai

Zargin Babban Hadimin Gwamnan Kano Ya Karkatar Da Kuɗaɗen Jama’a Ba Gaskiya Ba Ne

9 hours ago
Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya
Labarai

Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya

10 hours ago
Rashin Tsaro: Ana Ƙoƙarin Ganin Ƙarshen Haƙurin Arewa – ACF
Manyan Labarai

Rashin Tsaro: Ana Ƙoƙarin Ganin Ƙarshen Haƙurin Arewa – ACF

12 hours ago
Gwamnatin Sokoto Ta Ƙaryata Rahoton NBS Kan Talauci, Ta Ƙaddamar Da Sabon Bincike
Manyan Labarai

Gwamnatin Sokoto Ta Ƙaryata Rahoton NBS Kan Talauci, Ta Ƙaddamar Da Sabon Bincike

14 hours ago
Next Post
Halaye 8 Na Rayuwa Da Aka Fi So A Yi Shiru Maimakon Magana A Ciki (1)

Halaye 8 Na Rayuwa Da Aka Fi So A Yi Shiru Maimakon Magana A Ciki (1)

LABARAI MASU NASABA

An Yi Bikin Mu’ammalar Al’Adu Na SCO Na 2025 A Beijing

An Yi Bikin Mu’ammalar Al’Adu Na SCO Na 2025 A Beijing

August 25, 2025
Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Sin Ta Yi Rawar Gani A Fannin Bunkasa SCO

Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Sin Ta Yi Rawar Gani A Fannin Bunkasa SCO

August 25, 2025
CGTN Poll: Ba Da Kariya Shi Ne Tuna Baya—-Shekaru 80 Bayan Yakin Duniya Na II

CGTN Poll: Ba Da Kariya Shi Ne Tuna Baya—-Shekaru 80 Bayan Yakin Duniya Na II

August 25, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Yi Hasashen Ambaliyar Ruwa A Jihohin Arewa 15

Gwamnatin Tarayya Ta Sake Gargadin Jihohin Arewa 9 Kan Afkuwar Ambaliya 

August 25, 2025
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 3 Da Kubutar Da Mutum 16 Da Aka Sace A Kaduna

ECOWAS Za Ta Kaddamar Da Rundunar Yaki Da Ta’addanci Mai Jami’ai 260,000

August 25, 2025
Za A Watsa Shirin “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” a Manyan Kafofin Watsa Labarai Na Kasashen SCO

Za A Watsa Shirin “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” a Manyan Kafofin Watsa Labarai Na Kasashen SCO

August 25, 2025
Mauludi: Gwamnatin Kano Ta Sake Ɗage Ranar Komawa Makarantu

Zargin Babban Hadimin Gwamnan Kano Ya Karkatar Da Kuɗaɗen Jama’a Ba Gaskiya Ba Ne

August 25, 2025
Wani Rahoton Kasar Sin Ya Kalubalanci Halaccin Ayyukan Amurka Bisa Dogaro Da “’Yancin Zirga-zirga”

Wani Rahoton Kasar Sin Ya Kalubalanci Halaccin Ayyukan Amurka Bisa Dogaro Da “’Yancin Zirga-zirga”

August 25, 2025
Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya

Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya

August 25, 2025
Beijing Zai Bunkasa Amfani Da Fasahohin Zamani A Wuraren Adana Kayan Tarihi

Beijing Zai Bunkasa Amfani Da Fasahohin Zamani A Wuraren Adana Kayan Tarihi

August 25, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.