• English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Xi Jinping Ya Gana Da Sakataren Harkokin Wajen Amurka Antony Blinken

by CGTN Hausa
1 year ago
Xi

Da yammacin yau Juma’a, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gana da sakataren harkokin wajen Amurka Antony Blinken, a babban dakin taron jama’a dake birnin Beijing na kasar Sin.

A yayin ganawar, shugaba Xi ya yi nuni da cewa, ya kamata Sin da Amurka su zama abokai, a maimakon abokan gaba, kana su samu bunkasuwa tare, a maimakon kawo matsala ga juna, da neman ra’ayi daya da amincewa da bambance-bambancensu, a maimakon yin mugun takara da juna, da kuma cika alkawarinsu.

  • Yanzu-yanzu: Wasu Magina Sun Makale A Baraguzan Wani Gini Da Ya Rushe A Kano
  • An Kaddamar Da Bikin Nune-nunen Shirye-shiryen Bidiyo Da Sinima Na Kasar Sin A Kasar Serbia

Shugaba Xi ya jaddada cewa, kasar Sin a shirye take ta yi hadin gwiwa da bangarorin da suke son yin hadin gwiwa da ita. Sin ba ta jin tsoron yin takara, amma ya kamata a yi hakan don samun bunkasuwa tare, a maimakon cin moriya da faduwar wani. Kana kasar Sin ta tsaya tsayin daka kan kauracewa kafa kawance, kuma tana fatan Amurka ba za ta kafa kawancenta, da nufin yin adawa da Sin ba. Bangarorin biyu suna da abokan huldarsu, amma babu bukatar nuna kiyayya da juna da kawo matsaloli ga juna.

A nasa bangare, Blinken ya bayyana cewa, a halin yanzu, ana fuskantar kalubale mai sarkakiya a duniya, ana bukatar Amurka da Sin su yi hadin gwiwa wajen tinkarar kalubalen tare. A yayin ziyararsa a kasar Sin, ya gano bangarori daban daban na Amurka dake kasar Sin suna son kyautata dangantakar dake tsakanin Amurka da Sin. Amurka ba za ta ta da sabon yakin cacar baka, da canja tsarin kasar Sin, da dakile bunkasuwar kasar Sin, da kin amincewa da Sin ta hanyar kafa kawance, da kuma ta da rikici da kasar Sin ba. Amurka ta tsaya tsayin daka kan manufar “Sin daya tak a duniya”, kana tana son kiyaye yin mu’amala da kasar Sin, da aiwatar da matsayar da shugabannin kasashen biyu suka cimma a birnin Los Angeles, da neman karin hadin gwiwa, da magance rashin fahimtar juna, da daidaita matsalolinsu, ta hakan za a sa kaimi ga raya dangantakar dake tsakanin Amurka da Sin yadda ya kamata.

Yau Jumma’a, mamban ofishin siyasa na kwamitin kolin jam’iyyar kwaminis ta kasar Sin, kana ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi, ya yi shawarwari da takwaransa na kasar Amurka Antony Blinken a birnin Beijing, a ci gaba da ziyarar aiki da mista Blinken din ke yi a nan kasar Sin.

LABARAI MASU NASABA

An Yi Tafiye-tafiye Miliyan 16.34 Da Suka Shafi Shiga Da Fita Daga Kasar Sin Yayin Hutun Kwanaki 8 Na Kasar 

Duniya Ta Kara Ganin Bunkasuwar Sin a Lokacin Hutun Murnar Ranar Kafuwar Sabuwar Kasar

Yayin zantawarsu, Wang Yi ya yi tsokaci kan huldar kasashen biyu. A cewarsa, huldar kasashen biyu tana dan kara kyautata karkashin jagorancin shugabannin kasashen biyu, amma a wani bangare na daban, wasu abubuwan dake kawo cikas ga huldarsu na kara karuwa.

Wang, ya kuma jadadda cewa, Sin na tsayawa kan raya huldar kasashen biyu bisa ra’ayin kafa kyakkyawar makomar bil Adama ta bai daya, kuma tana tsayawa tsayin daka kan ka’idar da Xi Jinping ya gabatar, wato mutunta juna, da zama tare cikin lumana, da hadin kai, da cin moriya tare.

Kaza lika, Sin na fatan bangarorin biyu za su mai da hankali kan muradun da suka fi jawo hankalinsu, da fatan Amurka za ta kaucewa tsoma baki cikin harkokin cikin gidan kasar Sin, da yiwa bunkasuwar Sin matsin lamba. Kana ta kauracewa keta tushen muradun Sin, wato bangaren ikon mulkin kasar, da tsaro da bunkasuwa. (Zainab Zhang&Amina Xu)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

An Yi Tafiye-tafiye Miliyan 16.34 Da Suka Shafi Shiga Da Fita Daga Kasar Sin Yayin Hutun Kwanaki 8 Na Kasar 
Daga Birnin Sin

An Yi Tafiye-tafiye Miliyan 16.34 Da Suka Shafi Shiga Da Fita Daga Kasar Sin Yayin Hutun Kwanaki 8 Na Kasar 

October 9, 2025
Duniya Ta Kara Ganin Bunkasuwar Sin a Lokacin Hutun Murnar Ranar Kafuwar Sabuwar Kasar
Daga Birnin Sin

Duniya Ta Kara Ganin Bunkasuwar Sin a Lokacin Hutun Murnar Ranar Kafuwar Sabuwar Kasar

October 9, 2025
An Samu Karuwar Sayayya Yayin Hutun Bikin Kafuwar Kasar Sin
Daga Birnin Sin

An Samu Karuwar Sayayya Yayin Hutun Bikin Kafuwar Kasar Sin

October 9, 2025
Next Post
Sanusi

Zaman Lafiya: Malaman Kirista Na Arewa Sun Ziyarci Khalifa Sanusi Na II

LABARAI MASU NASABA

TCN

Jami’an Tsaro Sun Cafke Ɓarayin Kayayyakin Turakun Wutar Lantarki Na Hanyar Mando Zuwa Jos

October 9, 2025
An Yi Tafiye-tafiye Miliyan 16.34 Da Suka Shafi Shiga Da Fita Daga Kasar Sin Yayin Hutun Kwanaki 8 Na Kasar 

An Yi Tafiye-tafiye Miliyan 16.34 Da Suka Shafi Shiga Da Fita Daga Kasar Sin Yayin Hutun Kwanaki 8 Na Kasar 

October 9, 2025
Nijeriya Ta Yi Asarar Ganga Miliyan 13.5 Na Ɗanyen Mai Ta Hanyar Sata Da Zagon-ƙasa – NEITI

Nijeriya Ta Yi Asarar Ganga Miliyan 13.5 Na Ɗanyen Mai Ta Hanyar Sata Da Zagon-ƙasa – NEITI

October 9, 2025
Duniya Ta Kara Ganin Bunkasuwar Sin a Lokacin Hutun Murnar Ranar Kafuwar Sabuwar Kasar

Duniya Ta Kara Ganin Bunkasuwar Sin a Lokacin Hutun Murnar Ranar Kafuwar Sabuwar Kasar

October 9, 2025
Fursunoni Ba Za Su Samu Damar Kada Kuri’a Ba A Zaben 2023 – INEC

Batun Umarnin Kotu Na Kama Tsohon Shugaban INEC Ƙage Ne Kawai – Shugaban Jam’iyyar AA 

October 9, 2025
An Samu Karuwar Sayayya Yayin Hutun Bikin Kafuwar Kasar Sin

An Samu Karuwar Sayayya Yayin Hutun Bikin Kafuwar Kasar Sin

October 9, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Zaɓi Farfesa Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC 

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Zaɓi Farfesa Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC 

October 9, 2025
Adadin Biyan Kudade Ta Intanet Yayin Hutun Bikin Kafuwar Jamhuriyar Jama’ar Sin Ya Kai Yuan Tiriliyan 13.26

Adadin Biyan Kudade Ta Intanet Yayin Hutun Bikin Kafuwar Jamhuriyar Jama’ar Sin Ya Kai Yuan Tiriliyan 13.26

October 9, 2025
SSANU Da NASU Sun Yi Zanga-Zanga A Abuja Kan Rashin Cika Alƙawarin Gwamnati

SSANU Da NASU Sun Yi Zanga-Zanga A Abuja Kan Rashin Cika Alƙawarin Gwamnati

October 9, 2025
An Umurci Manyan Makarantu Su Mayar Da Kuɗaɗen TETFund Da Ba Su Kashe Ba

An Umurci Manyan Makarantu Su Mayar Da Kuɗaɗen TETFund Da Ba Su Kashe Ba

October 9, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.