• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ko Kin San…Abin Da Ke Kawo Warin Gaba? (2)

by Bilkisu Tijjani
1 year ago
in Kiwon Lafiya
0
Ko Kin San…Abin Da Ke Kawo Warin Gaba? (2)
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Assalamu alaikum masu karatu, barkammu da sake haduwa daku a wannan makon a cikin shirin namu mai farin jini da albarka na Ko Kin San.

A yau shafin namu yana ci gaba da bayani ne kan abin da ke kawo warin gaba:
Auduga mai laushi na taimakawa wurin bai wa gaba iska kuma yana yin kyakkyawan aiki a wurin kawar da gumi da ruwa daga jikinku. Yawan danshi zai iya sa ki kamu da kwayoyin cuta da za su yi wa gabanki illa.

Sannan ya kamata ki kula da yawan sauya kamfai da siket saboda idan suka yi datti kuma kika maimaita su to akwai yiwuwar su haifar da warin gaba.

Sanin lokacin ganin likita:
Idan wannan warin yana tare da alamun da ba ku saba gani ko ji ba, ya kamata ku guji yin magani a gida ku tuntubi likitoci.

Misali: Idan warin gaba ya fi na al’ada karfi kuma kin lura cewa yana kara karfi, to kina bukatar ganin likita.
Haka nan, idan kin ji gabanki ya fara wari kamar na “kifi” wannan ma ya kamata ki yi saurin ganin likita. Wari mara kyau alama ce ta kamuwa da cutar gaba. Ba za ku so ku jinkirta magance matsalar ba domin cutar gaban da ba a nemi maganinta ba kan iya jawo matsalar rashin haihuwa idan ta dade ana fama da ita.

Labarai Masu Nasaba

Kwararraun Likitocin Tiyata 6 Ne Kacal Suka Rage A Kano – Farfesa Sani

Cutar Hawan Jini Na Ci Gaba Da Yi Wa ‘Yan Nijeriya Kisan Mummuke

Wasu ruwa da ke fitowa daga gaban mace na iya zama na ka’ida. Idan kin lura da canji a launin ruwan, misali launin da kika saba gani fari ne ko bai da kala amma sai kika fara ganin wani launin daban, to zai iya yiwuwa kin kamu da cuta.

Yawanci kaikayin al’aura ba matsala ba ce, amma idan kuka fara jin kaikayin ya fara yawa ko kuma ya fara zafi da radadi, to alama ce na babbar matsala.

Hanyar magance sake warin gaba:
Da zarar kin kawar da warin gaba wanda ba a saba ji ba, to ki kiyaye wadannan shawarwari don hana wata matsalar.

Kula da cin lafiyayyen abinci mai sinadiran gina jiki. Yawaita cin ‘ya’yan itace, da kayan lambu. Daidaitaccen abinci yana samar da lafiyayyen jiki, kuma hakan ya hada da gabanki.Kasance mai yawan shan ruwa. Shan ruwa mai yawa yana da amfani sosai a dukkan jiki ba sai ga fata ba kawai. Yana iya taimaka wa ga lafiyar gabanki, kuma ta hanyar karfafa gumi mai kyau.

Ki dinga wanke gabanki kafin saduwa da kuma bayan saduwa. Jima’i kan iya kawo yaduwar kwayoyin cuta da maniyyi daga kwaroron roba.

Ku daina amfani da matsattsun kaya. Tufafi masu matsewa ba sa barin gabanku ya sha iska. Samun isasshiyar iskar na da muhimmanci ga lafiyar gaban mace.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 'Yan MataAl'adamatsaloln mata
ShareTweetSendShare
Previous Post

Bincike: Kamfanonin Kasashen Waje Na Da Karin Kwarin Gwiwa Kan Kasuwar Sin 

Next Post

Za A Watsa Shirin “Labarun Da Xi Jinping Ya Fi So” A Gidajen Watsa Labarai Na Faransa

Related

Kwararraun Likitocin Tiyata 6 Ne Kacal Suka Rage A Kano – Farfesa Sani
Kiwon Lafiya

Kwararraun Likitocin Tiyata 6 Ne Kacal Suka Rage A Kano – Farfesa Sani

1 week ago
Cutar Hawan Jini Na Ci Gaba Da Yi Wa ‘Yan Nijeriya Kisan Mummuke
Kiwon Lafiya

Cutar Hawan Jini Na Ci Gaba Da Yi Wa ‘Yan Nijeriya Kisan Mummuke

1 week ago
Cutar Cholera Ta Ɓarke A Filato, Mutane 4 Sun Mutu
Kiwon Lafiya

Cutar Cholera Ta Ɓarke A Filato, Mutane 4 Sun Mutu

4 weeks ago
Cutar Mashaƙo Ta Kashe Yara Biyu A Kaduna
Kiwon Lafiya

Cutar Mashaƙo Ta Kashe Yara Biyu A Kaduna

1 month ago
Nau’in Abinci Biyar Da Ke Lalata Hanta
Kiwon Lafiya

Nau’in Abinci Biyar Da Ke Lalata Hanta

2 months ago
Sirrin da ke Tattare da Ganyen Mangwaro Ga Lafiyar Ɗan Adam
Kiwon Lafiya

Sirrin da ke Tattare da Ganyen Mangwaro Ga Lafiyar Ɗan Adam

2 months ago
Next Post
Za A Watsa Shirin “Labarun Da Xi Jinping Ya Fi So” A Gidajen Watsa Labarai Na Faransa

Za A Watsa Shirin “Labarun Da Xi Jinping Ya Fi So” A Gidajen Watsa Labarai Na Faransa

LABARAI MASU NASABA

Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

June 7, 2025
Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

June 7, 2025
Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

June 7, 2025
Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

June 7, 2025
Neja

Dalilin Rashin Fara Aikin Kamfanin Takin Zamani Na Gwamnatin Jihar Neja

June 7, 2025
Adawa

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

June 7, 2025
2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

June 7, 2025
Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

June 7, 2025
Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.