• English
  • Business News
Wednesday, August 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mata A Dage Da Tsare Mutuncin Kai – Zainab Muhammad

by Bilkisu Tijjani
1 year ago
in Adon Gari
0
Mata A Dage Da Tsare Mutuncin Kai – Zainab Muhammad
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Labarai Masu Nasaba

Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa

Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa

ZAINAB MUHAMAD mai neman ilimi kuma ‘yar kasuwancin sayar da kayan kamshi na mata ‘yar asalin Garin Hadejia ta yi wa shafi Adon Gari karin haske kan yadda ta tsinci kanta a harkar kasuwaci wanda ta ce ta samu rufin asiri sosai a cikinta, sannan ta yi kira ga mata da su koyi sana’a domin su tsira da mutuncinsu, kamar yadda za ku ji a wannan hira da wakiliyarmu BILIKSU TIJJANI KASSIM.

Da fari za mu so sanin cikakken sunanki da tarihinki

Suna na Zainab Muhammad Sambo, ni cikakkiyar ‘ya Hadejia ce an haife ni a Garin Hadejia a shekara ta 1997 a Unguwar Wuriwa, na yi makaranta a Garin Hadejia

Shin Zainab matar aure ce?

A’a ni ba matar aure bace muna niyya in sha Allahu.

‘Yar kasuwa ce ko ma’aikaciya?

A a ni ba ma’aikaciya bace, ina dan taba kasuwanci haka-kadan dai wanda ba’a rasa ba.

Wanne irin kasuwanci kike yi?

Kayan kamshi nake sayarwa

Shin me kasuwancin naki ya kunsa?

Kamar turaren wuta, Humura da duk nau’ika na kayan kamshi da sauransu.

To ke kuwa me ya ja hankalinki har kika shiga wannan kasuwanci?

Saboda ni ma’abociyar san kamshi ce.

Me ye matakin karatunki?

Na gama Difiloma.

Wanne irin kalubale kika taba fuskanta a cikin sana’arki?

Kalubalan da na fuskanta akwai ranar da wata ta sani na hada mata turaren wuta amma ba ta saya ba shi ne kalubale na da na taba fuskanta, saboda abin ya bani haushi kin san dai yadda hadin turare yake da wahala ka kwana kana yi sai da na gama ba ta kara magana ba.

Zuwa yanzu wanne irin nasarori kika cimma?

Na samu nasarori da dama bikin kawayena da taron makaranta duk da sana’ ata nake yi har na tallafa wa mabukata

Wanne abu ne ya fi faranta miki rai game da sana’arki?

Alhamdu lillah idan na yi turare a ce ya yi dadi ana so wannan yana faranta min rai ina jin dadin haka sosai.

Ta wacce hanya kike bi wajen tallata sana’arki?

Ta hanyar intanet kamar whatsapp, facebook, instagram, da dai sauransu.

Dame kike so mutane su rika tunawa dake?

Ina so mutane su rika tunawa da ni a kan kamshina da kuma fara’a ta da wasa da dariya.

Ga karatu, ga kuma kila kina taya mama ayyukan gida, shin ta yaya kike samun damar gudanar da hutunki?

Kome nawa a tsare yake komai na ba shi lokacinsa.

Wace irin addu’a ce idan aka yi miki kike jin dadi?

In aka min addu’ar Allah ya jikan mahaifina ina jin dadi sosai

Wane irin goyon baya kike samu daga wajen iyaye da ‘yan uwanki?

 Alhamdu lillah ina samun goyan baya dari bisa dari a wurin iyayena da ‘yan uwana babu abin da zan ce musu sai godiya da kuma addu’ar Allah ya saka musu da alkhairi.

Kawaye fa?

Ni ban da kawaye, ‘yan uwana su ne kawayena

Me kika fi so cikin kayan sawa fa kayan kwalliya?

Ina son leshi da doguwar riga ta komai kayan kwalliya kuma ba na son na ga idona babu kwalli.

A karshe wace irin shawara za ki bawa ‘yan uwanki mata?

Shawarata ga mata ‘yan uwana su dage su nemi sana’a kuma su tsare mutumcinsu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Adon GariMataMutuncin Kai
ShareTweetSendShare
Previous Post

An Kori Shugaban Jam’iyyar APC Na Jihar Zamfara Tukur Danfulani Daga Jamiyyar

Next Post

Sanata Iya Abbas Ya Jajantawa Mutanen Da Iftila’in Iskar Hadarin Ruwa Ta Shafa A Hong

Related

Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa
Ado Da Kwalliya

Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa

3 days ago
Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa
Adon Gari

Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa

1 week ago
Wasu Kyawawan Ɗabi’u Da Suke Ƙarfafa Zamantakewar Aure
Adon Gari

Wasu Kyawawan Ɗabi’u Da Suke Ƙarfafa Zamantakewar Aure

3 months ago
Ko Kin San… Yadda Ake Nagartaccen Tsumi?
Adon Gari

Ko Kin San… Yadda Ake Nagartaccen Tsumi?

3 months ago
Mata Mu Tsaya Da Kafafunmu Kar Mu Tsaya Sai An Bamu – Khadeejah Abdullahi
Adon Gari

Mata Mu Tsaya Da Kafafunmu Kar Mu Tsaya Sai An Bamu – Khadeejah Abdullahi

6 months ago
Mata Mu Dage Da Neman Ilimi Da Neman Na Kanmu -Hassana Umar
Adon Gari

Mata Mu Dage Da Neman Ilimi Da Neman Na Kanmu -Hassana Umar

6 months ago
Next Post
Sanata Iya Abbas Ya Jajantawa Mutanen Da Iftila’in Iskar Hadarin Ruwa Ta Shafa A Hong

Sanata Iya Abbas Ya Jajantawa Mutanen Da Iftila'in Iskar Hadarin Ruwa Ta Shafa A Hong

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kama Mai Yi Wa Boko Haram Safarar Man Fetur A Borno

Sojoji Sun Kama Mai Yi Wa Boko Haram Safarar Man Fetur A Borno

August 6, 2025
Matar Marigayi MKO Abiola, Ta Rasu Tana Da Shekaru 82

Matar Marigayi MKO Abiola, Ta Rasu Tana Da Shekaru 82

August 6, 2025
Remi Tinubu Ta Bai Wa WaÉ—anda Ambaliya Ta Shafa A Neja Tallafin N1bn

Remi Tinubu Ta Bai Wa WaÉ—anda Ambaliya Ta Shafa A Neja Tallafin N1bn

August 6, 2025
Gwamnatin Tarayya Za Ta FarfaÉ—o Da Noman Dabino – Shettima

Gwamnatin Tarayya Za Ta FarfaÉ—o Da Noman Dabino – Shettima

August 6, 2025
Kwamishinan Sufuri Ya Yi Murabus Kan Belin Wani Da Ake Zargi Da Laifin Safarar Kwaya A Kano

Kwamishinan Sufuri Ya Yi Murabus Kan Belin Wani Da Ake Zargi Da Laifin Safarar Kwaya A Kano

August 6, 2025
Hare-haren Boko Haram Da ‘Yan Bindiga Ya Ragu A Cikin Shekaru Biyu – Ribadu

Hare-haren Boko Haram Da ‘Yan Bindiga Ya Ragu A Cikin Shekaru Biyu – Ribadu

August 5, 2025
Kasar Sin Ta Sanar Da Matakan Fara Bayar Da Ilimin Kafin Firamare Kyauta

Kasar Sin Ta Sanar Da Matakan Fara Bayar Da Ilimin Kafin Firamare Kyauta

August 5, 2025
Shugaban IWGA: Birnin Chengdu Zai Karbi Bakuncin Gasar Wasanni Mafi Kyau A Tarihi

Shugaban IWGA: Birnin Chengdu Zai Karbi Bakuncin Gasar Wasanni Mafi Kyau A Tarihi

August 5, 2025
Jigawa Ta Fitar Da ₦1.5bn Na Lamunin Noma Ga Ma’aikatan Gwamnati Kashi Na Biyu

Jigawa Ta Fitar Da ₦1.5bn Na Lamunin Noma Ga Ma’aikatan Gwamnati Kashi Na Biyu

August 5, 2025
Matakin Baiwa Kansa Hakuri Ba Zai Kawar Da Matsayin Gwamnatin Lai Ching-te Na Kasancewa ’Yar Dara A Hannun Amurka Ba

Matakin Baiwa Kansa Hakuri Ba Zai Kawar Da Matsayin Gwamnatin Lai Ching-te Na Kasancewa ’Yar Dara A Hannun Amurka Ba

August 5, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.