• English
  • Business News
Thursday, September 18, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Halin Da Ake Ciki A ‘Yandoton Daji Bayan Nadin Sarautar Dan Ta’adda

…Ya Kashe Mutum 100 A Katsina, In Ji ‘Yansanda

by Hussein Yero
3 years ago
in Labarai
0
Dan Ta’addar Da Aka Nada Sarauta A Zamfara Ya Kashe Mutum 100 A Katsina – ‘Yansanda
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Nadin sarautar da Sarkin ‘Yandoton Daji ya yi wa jigo ga ‘yan bindiga da ya addabi jihohin Zamfara, Katsina da Sakwato, Ado Aleru ya tayar da kura, inda lamarin ya janyo dakatar da Sarkin ‘Yandoto Daji, Alhaji Aliyu Garba Marafa daga karagar mulki da kuma soke Sarautar Sarkin Fulanin da aka yi wa Aleru.

Wannan ne ya sanya LEADERSHIP Hausa ta garzaya yankin Masarautar Sarkin ‘Yandoto Daji domin jin ra’ayin al’ummar yankin na soke Sarautar Sarkin Fulani Aleru da shi kansa Sarkin ‘Yandoto da yanzu haka Gwamna Matawallen Maradu ya dakatar da shi.

  • Gwamnatin Zamfara Ta Hana Nadin Sarauta A Fadin Jihar 

Malam Alhassan Muntaka ‘Yankuzo, mazaunin ‘Yankuzo ne inda shi Sarkin Fulani Aleru yake da zama da iyalasa, ya bayyana wa wakilinmu cewa, Ado Aleru duk abubuwan da aka ce yana yi na ta’addanci bai taba yin su a Tsafe ta gabas ba.

Ya ce, “Duk fadin yankinmu na Tsafe ta gabas babu wani dan ta’addan da yake shigowa yankin domin cutar da mu. Kuma yanzu haka manomanmu da matafiyanmu suna gudanar da harkokinsu yadda ya kamata cikin ‘yanci tun kafin a ba shi sarautar Sarkin Fulani Tsafe ta Gabas.

“Zamowar Ado Aleru a yankin Tsafe ta gabas alheri ne a wajanmu, domin bai yarda a kawo mana hari daga baki da ‘yan gida ba. Kuma mutanansa masu kawo masa ziyara dauke da manyan makamai ba su taba cutar da mu ba. Domin haka soke sarautarsa ta Sarkin Fulani ba zai cutar da mu ba ko kadan,” in ji Muntaka ‘Yankuzo.

Labarai Masu Nasaba

Ci Gaban Tattalin Arzikin Sin Na Taimaka Ga Bunkasa Al’adunta Da Mu’amalar Al’adu Tsakaninta Da Kasashen Duniya

’Yansanda Sun Kama Sojan Gona Da Motocin Sata 3 A Jigawa

Hajiya Juma Banakowa, tana daya daga cikin mazauna Garin ‘Yankuzo kuma tana da gida a ‘Yandoto ta shaida wa wakilinmu ra’ayinta na soke Sarautar Sarkin Fulani Aleru kamar haka, Ado Aleru yana da gidaje a cikin ‘Yankuzo kuma yanzu haka nan yake da iyalansa.

Ta ce shi ba ya fita sai dai yana da yara dama, idan ka ga ba ya gari, to ya fita wajen Jihar Zamfara ko Kasar Nijer, domin can ya fi kai hare-harensa.
Juma ta kara da cewa, shi ne sila ta sulhu da aka yi a masarautar Tsafe wanda yanzu haka Fulani na shiga kasuwani, sannan matansu na sayar da nono.

A cewarta, yanzu a yankin Tsafe ta Gabas ba su da fargaba kuma warware rawanin Sarkin Fulani Aleru, ba zai fusata shi ba ya cutar da al’ummar yankin, domin dama bai saba cutar da su ba. Ta ce a yanzu haka yana neman auren wata budurwa a yankin kuma tana son sa duk da mahaifita ya ce ba zai ba shi ba saboda matansa hudu.

Batun dakatar da Sarkin ‘Yandoto kuwa, al’ummar garin murna ta koma cikin, saboda sabuwar masarauta ce wacce ba ta wuce wata biyu da kafa ta ba, kasancewar an cire ta ce daga cikin karamar hukumar Tsafe.

Da yake tofa albarkacin bakinsa, Mujitaba Damo, daya daga cikin mazauna ‘Yandoto, inda yanzu haka nan ne fadar masarautar Sarkin ‘Yandoto ya bayyana ra’ayinsu a kan wannan danbarwa kamar haka, “lallai ba a yi wa Sarkin ‘Yandoto, Aliyu Garba Marafa adalci ba, domin kafin sarkin ya rike wannan mukami ya taba zama uban kasa da hakimi bai taba yin abu ba tare da izini gwamnati ba, ballantana yanzu da ya zama ya samu matsayi na sarki mai daraja ta uku.”
Ya kuma kara da cewa ya san Ado Aleru babban dan ta’adda ne, domin haka sarkin bai da ikon ba shi sarautar Sarkin Fulani sai da izini gwamnati.

Ya ce akwai takarda a rubuce, domin ko a wajen bikin nadin sarautar akwai wasu masu manyan mukaman gwamnati da suka halarci nadin.

Ya yi kira ga kwamitinin da gwamna ya kafa da ya yi wa Sarkin ‘Yandoto adalci, sannan duk wanda ke da hannu a kai komai mukaminsa a hukunta shi, domin ba Sarkin ‘Yandoto kadai ba ne ke da hannu, akwai wasu sarakuna.

Sakamakon Allah wadai da al’ummar kasar nan suka yi saboda nadin kasurgumin dan ta’adda, Ado Aleru a matsayin Sarkin Fulani a karkashi masarautar Sarkin ‘Yandoto, gwamnatin Jihar Zamfara ta nesanta kanta da nadin.

Wannan yana dauke ne cikin wata sanarwa mai dauke da sa hannun sakataren gwamnatin Jihar zamfara, Kabiru Balarabe, wacce aka raba wa manema labarai a Gusau, Babbar birnin Jihar Zamfara.

Sakataren gwamnatin ya bayyana cewa, Gwamna Bello Mohammed Matawalle, ya bayar da umarnin dakatar da Sarkin ‘Yandoto, Mai Martaba Aliyu Garba Marafa nan take. Kuma ya amince da nada kwamitin da zai binciki yadda abun ya kasance.

Wadanda aka nada a matsayin ‘yan kwamitin sun hada da Hon. Yahaya Chado Gora, a matsayin shugaba da Hon. Yahaya Mohd Kanoma da Hon. Muhammad Umar B/Magaji da Hon. Lawal Abubakar Zannah da Isa Muhammad Moriki da Barista Musa Garba.

Kuma a nan take gwamnatin ta bayyana Alhaji Mahe Garba Marafa, wanda shi ne Hakimin ‘Yandoto a matsayin wanda zai kula da harkokin masarautar.

…Ya Kashe Mutum 100 A Katsina, In Ji ‘Yansanda

Rundunar ‘yan sandan jihar Katsina ta tabbatar da cewa har yanzu fitaccen dan Ta’adda Ado Aleru, wanda masarautar Yandoto Daji ta jihar Zamfara ta yi masa rawanin sarauta a ranar Alhamis din da ta gabata, har yanzun yana cikin jerin sunayen wanda take nema ido-rufe.
Rundunar ta ce Alero ya kashe mazauna jihar Katsina 100.

Kakakin rundunar ‘yan sandan jihar, Gambo Isah, ne ya bayyana hakan a lokacin da yake mayar da martani kan sarautar da aka baiwa shugaban ‘yan bindigar a jihar Zamfara.
Isah ya ce rundunar na tuhumar Aleru d

a laifukan da suka hada da kisan kai, ta’addanci, fashi da makami, da kuma garkuwa da mutane a jihar Katsina.
Ya kara da cewa, ana kuma neman Aleru da laifin kashe mutane sama da 100 a kauyen Kadisau da ke karamar hukumar Faskari a jihar.

Rundunar ‘yan sandan jihar Katsina a watan Yunin shekarar da ta gabata na neman Alero mai shekaru 47 da haihuwa a karamar hukumar Tsafe ta jihar Zamfara, ruwa a jallo, inda ta daura kyautar Naira miliyan 5 – a mace ko a raye ga duk wanda ya kawo mata shi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Zargin Almundahana: Yau EFCC Za Ta Gurfanar Da Tsohon Akanta-Janar A Gaban Kotu 

Next Post

Mane Ya Zama Gwarzon Dan Wasan Afirka

Related

Ci Gaban Tattalin Arzikin Sin Na Taimaka Ga Bunkasa Al’adunta Da Mu’amalar Al’adu Tsakaninta Da Kasashen Duniya
Ra'ayi Riga

Ci Gaban Tattalin Arzikin Sin Na Taimaka Ga Bunkasa Al’adunta Da Mu’amalar Al’adu Tsakaninta Da Kasashen Duniya

15 minutes ago
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba
Labarai

’Yansanda Sun Kama Sojan Gona Da Motocin Sata 3 A Jigawa

3 hours ago
Yadda Muka Zama Bayin ‘Yan Bindiga -Mazaunin Wani Kauye
Labarai

’Yan Bindiga Sun Sako Ma’aurata A Katsina Bayan Karɓar N50m A Matsayin Kuɗin Fansa

5 hours ago
Yadda Ribas Ta Yi Cikar Ƙwari Yayin Da Gwamna Fubara Ya Koma Ofis
Manyan Labarai

Yadda Ribas Ta Yi Cikar Ƙwari Yayin Da Gwamna Fubara Ya Koma Ofis

6 hours ago
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku
Manyan Labarai

Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

7 hours ago
’Yansanda Sun Kama Mutane 9 Kan Yin Ƙaryar Sace Su A Jihar Neja
Labarai

’Yansanda Sun Kama Mutane 9 Kan Yin Ƙaryar Sace Su A Jihar Neja

9 hours ago
Next Post
Mane Ya Zama Gwarzon Dan Wasan Afirka

Mane Ya Zama Gwarzon Dan Wasan Afirka

LABARAI MASU NASABA

Ci Gaban Tattalin Arzikin Sin Na Taimaka Ga Bunkasa Al’adunta Da Mu’amalar Al’adu Tsakaninta Da Kasashen Duniya

Ci Gaban Tattalin Arzikin Sin Na Taimaka Ga Bunkasa Al’adunta Da Mu’amalar Al’adu Tsakaninta Da Kasashen Duniya

September 18, 2025
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Kama Sojan Gona Da Motocin Sata 3 A Jigawa

September 18, 2025
Yadda Muka Zama Bayin ‘Yan Bindiga -Mazaunin Wani Kauye

’Yan Bindiga Sun Sako Ma’aurata A Katsina Bayan Karɓar N50m A Matsayin Kuɗin Fansa

September 18, 2025
Yadda Ribas Ta Yi Cikar Ƙwari Yayin Da Gwamna Fubara Ya Koma Ofis

Yadda Ribas Ta Yi Cikar Ƙwari Yayin Da Gwamna Fubara Ya Koma Ofis

September 18, 2025
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

September 18, 2025
’Yansanda Sun Kama Mutane 9 Kan Yin Ƙaryar Sace Su A Jihar Neja

’Yansanda Sun Kama Mutane 9 Kan Yin Ƙaryar Sace Su A Jihar Neja

September 18, 2025
Sojoji Sun Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindiga, Sun Kashe Shugaban IPOB

Sojoji Sun Cafke Babban Kwamandan IPOB

September 18, 2025
Ya Kamata A Kiyaye Nasarorin Da Aka Cimma A Shawarwarin Sin Da Amurka 

Ya Kamata A Kiyaye Nasarorin Da Aka Cimma A Shawarwarin Sin Da Amurka 

September 17, 2025
Yawan Kadarorin Kamfanoni Mallakar Gwamnatin Sin Ya Wuce Yuan Triliyan 90 a Lokacin Shirin Raya Kasa Na 14 Na Shekaru 5 

Yawan Kadarorin Kamfanoni Mallakar Gwamnatin Sin Ya Wuce Yuan Triliyan 90 a Lokacin Shirin Raya Kasa Na 14 Na Shekaru 5 

September 17, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu

Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu

September 17, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.