• English
  • Business News
Wednesday, August 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sanata Saliu Ya Raba Taki Da Injinan Ban Ruwa Ga Manoman Kwara

by Abdulrazaq Yahuza
1 year ago
in Labarai
0
Sanata Saliu Ya Raba Taki Da Injinan Ban Ruwa Ga Manoman Kwara
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

 Shugaban kwamitin majalisar dattijai mai kula da ayyukan noma da raya karkara, Sanata Saliu Mustapha ya kaddamar da rabon taki buhu 3,500 mai nauyin kilogiram 50, ga kananan manoma a fadin kananan hukumomi hudu na gundumar mazabar Kwara ta tsakiya da yake wakilta a majalisar dattawa.

Sanatan ya ce rabon kayan shi ne matakin farko na dabarun da za a tabbatar da dorewar ayyukan noma a gundumar.

  • Champions League: Real Madrid Ta Zama Zakara Bayan Doke Dortmund
  • Gwamnatin Kebbi Ta Ayyana Asabar Ɗin Karshe Wata A Matsayin Ranar Tsaftar Muhalli

Wadanda suka ci gajiyar rabon kayan noman da dan majalisar ya yi sun hada da mambobin kungiyar manoma ta Najeriya AFAN, da daidaikun jama’a, da ‘ya’yan jam’iyyar All Progressives Congress (APC), wadanda suke noma.

A lokacin rabon kayayyakin noman a filin wasa na hukumar raya kogin Neja ta karamar hukumar Ilorin, Mustafa ya ce, wasu karin manoma za su ci gajiyar shirin nan gaba kadan.

Sanata Saliu

Labarai Masu Nasaba

Allah Zai Kunyata Masu Ɗaukar Nauyin ’Yan Ta’adda – Gwamnan Zamfara

2027: Jagororin APC Na Kudu-maso-Yamma Sun Amince Da Tinubu Ya Sake Tsayawa Takara

Ya Kara da cewa shirin mai taken: “Tallafawa Manoman Kwara ta Tsakiya: Bude hanyoyin dogaro da kai wajen samar da abinci,” na da nufin tallafa ayyukan noma da habaka samun yabanya ga manoman mazabar.

“Tasirin sauyin yanayi da kuma yawaitar noman gonaki yana da illa ga ingancin kasar noma. Wannan ya haifar da raguwar amfanin amfanin gonar da ake samu.

“Yana da mahimmanci in jaddada cewa ni da kaina na sayi buhunan taki guda 3,500 da aka raba a yau domin karfafa wa manomanmu gwiwa da inganta amfanin gonakinsu,” in ji Sanata Mustafa.

Mustapha ya bayyana cewa rabon taki mai yawa irin wannan na nuni da yadda ake zuba jari mai yawa a fannin noma, wanda hakan ke nuna aniyar inganta samar da abinci da tallafawa rayuwar manoma domin bunkasa noman abinci a jihar.

Sanatan na Kwara ya yi amfani da wannan dama wajen nuna wasu daga cikin nasarorin da ya samu cikin shekara daya da shafe a matsayinsa na dan majalisa da ya hada da gudanar da aikin sake gina titi Mai tsawon kilomita daya a daura da Jami’ar Al-Hikmah wanda ya dangana da titin Oke zuwa Foma a karamar hukumar Ilorin ta yamma.

Sanata Saliu

Ya kara da cewa, an kuma gina rijiyoyin burtsatse masu amfani da hasken rana da sanya fitulun titi a fadin kananan hukumomin hudu na mazabar domin taimakawa kokarin gwamnatin jihar na ganin jama’a sun samu tsaftataccen ruwan sha.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Noman alkamaNoman raniTsadar kayan abinci
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kwamishinan Bauchi Ya Rasu A Hatsarin Mota

Next Post

Matar Gwamnan Kebbi Ta Gudanar da Bikin Ranar Tsaftar Jinin Al’ada Ta Duniya A Argungu

Related

Allah Zai Kunyata Masu Ɗaukar Nauyin ’Yan Ta’adda – Gwamnan Zamfara
Labarai

Allah Zai Kunyata Masu Ɗaukar Nauyin ’Yan Ta’adda – Gwamnan Zamfara

42 minutes ago
APC
Labarai

2027: Jagororin APC Na Kudu-maso-Yamma Sun Amince Da Tinubu Ya Sake Tsayawa Takara

3 hours ago
Tinubu
Labarai

Rangwame: Tinubu Ya Bada Umarnin Sake Bitar Tsarin Yadda Ake Karɓar Haraji 

4 hours ago
Gwamnatin Tarayya Ta Dakatar Da Kafa Sabbin Manyan Makarantu Na Tsawon Shekaru 7
Manyan Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Dakatar Da Kafa Sabbin Manyan Makarantu Na Tsawon Shekaru 7

6 hours ago
Majalisar Kano Na Shirin Zartar Da Dokar Gwajin Kwayoyin Jini, Kanjamau Da Cutar Hanta Kafin Aure
Manyan Labarai

Majalisar Kano Ta Dakatar Da Shugaban Karamar Hukuma Bisa Zargin Kara Farashin Takin Gwamnati

7 hours ago
NDLEA Ta Kama Dilolin Ƙwaya 49 A Kano
Labarai

NDLEA Ta Kama Dilolin Ƙwaya 49 A Kano

9 hours ago
Next Post
Matar Gwamnan Kebbi Ta Gudanar da Bikin Ranar Tsaftar Jinin Al’ada Ta Duniya A Argungu

Matar Gwamnan Kebbi Ta Gudanar da Bikin Ranar Tsaftar Jinin Al'ada Ta Duniya A Argungu

LABARAI MASU NASABA

Allah Zai Kunyata Masu Ɗaukar Nauyin ’Yan Ta’adda – Gwamnan Zamfara

Allah Zai Kunyata Masu Ɗaukar Nauyin ’Yan Ta’adda – Gwamnan Zamfara

August 13, 2025
Gyaruwar Alakar Kasuwancin Sin Da Amurka Ta Zarce Bukatun Kasashen Biyu

Gyaruwar Alakar Kasuwancin Sin Da Amurka Ta Zarce Bukatun Kasashen Biyu

August 13, 2025
APC

2027: Jagororin APC Na Kudu-maso-Yamma Sun Amince Da Tinubu Ya Sake Tsayawa Takara

August 13, 2025
Sin Ta Dauki Matakan Mayar Da Martani Kan Bankuna Biyu Na EU

Sin Ta Dauki Matakan Mayar Da Martani Kan Bankuna Biyu Na EU

August 13, 2025
Tinubu

Rangwame: Tinubu Ya Bada Umarnin Sake Bitar Tsarin Yadda Ake Karɓar Haraji 

August 13, 2025
Sashen Tattalin Arzikin Teku Na Sin Ya Bunkasa A Rabin Farko Na Bana

Sashen Tattalin Arzikin Teku Na Sin Ya Bunkasa A Rabin Farko Na Bana

August 13, 2025
Farfado Da Karkarar Sin: Canjin Gaisuwa Daga “Shin Ka Ci Abinci?” Zuwa “Yaya Rayuwarka A Gari?”

Farfado Da Karkarar Sin: Canjin Gaisuwa Daga “Shin Ka Ci Abinci?” Zuwa “Yaya Rayuwarka A Gari?”

August 13, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Dakatar Da Kafa Sabbin Manyan Makarantu Na Tsawon Shekaru 7

Gwamnatin Tarayya Ta Dakatar Da Kafa Sabbin Manyan Makarantu Na Tsawon Shekaru 7

August 13, 2025
Aikin Hakar Kwal Ta Hanyar Amfani Da Fasahar Zamani Ya Fara Wuce 50% a Kasar Sin

Aikin Hakar Kwal Ta Hanyar Amfani Da Fasahar Zamani Ya Fara Wuce 50% a Kasar Sin

August 13, 2025
Majalisar Kano Na Shirin Zartar Da Dokar Gwajin Kwayoyin Jini, Kanjamau Da Cutar Hanta Kafin Aure

Majalisar Kano Ta Dakatar Da Shugaban Karamar Hukuma Bisa Zargin Kara Farashin Takin Gwamnati

August 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.