• English
  • Business News
Saturday, November 1, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bauchi Za Ta Gudanar Da Zaɓen Shugabannin Ƙananan Hukumomi A Watan Agusta

by Khalid Idris Doya
1 year ago
Bauchi

Hukumar shirya zaɓe mai zaman kanta ta jihar Bauchi (BASIEC) ta shirya gudanar da zaɓen shugabannin ƙananan hukumomi 20 da suke jihar Bauchi ranar 10 ga watan Agustan 2024. 

Shugaban hukumar BASIEC, Ahmed Makama, shi ne ya sanar da hakan a hirarsa da manema labarai a ranar Juma’a, ya na mai bada tabbatar cewa hukumar ta shirya gudanar da sahihi, ingattaccen kuma karɓaɓɓen zaɓe ga kowani ɓangare.

  • Goron Juma’a
  • Yajin Aiki: NAHCON Ta Gargadi NLC Kan Janyo Cikas Ga Jigilar Maniyyata

Ya ce bisa yadda suke ƙunshe a dokoki, BASIEC ta samu umarnin gudanar da zaɓen shugabannin ƙananan hukumomi cikin kwanaki 60 masu zuwa.

A cewarsa, “Idan ku ka lissafi kwanaki 60 daga yau, zai kasance ranar 6 ga watan Agusta ne kuma ba ranar Asabar ba, sannan, yawancin lokuta an saba gudanar da zaɓuka a ranakun Asabar. Don haka mun tura zaɓen zuwa ranar 10 ga watan Agustan 2024.”

Ahmed Malama ya cigaba da cewa BASIEC za ta yi amfani da adadin masu rajistan zaɓe na hukumar zaɓe mai zaman kanta ta ƙasa (INEC) wajen gudanar da zaɓen, yana mai cewa su a ɓangarensu ba su cika ajiye jerin masu rijistan zaɓe ba.

LABARAI MASU NASABA

Trump Ya Ayyana Nijeriya A Matsayin Ƙasar Da Rayuwar Kiristoci Ke Cikin Hatsari

An Tsare Wani Mutum A Gidan Yari Kan Zargin Kashe Matarsa Saboda Ƙuli-Ƙuli A Kano

Shugaban hukumar zaɓen ya kuma sanar da cewa an fara sayar da fom ɗin neman tsayawa takara ga dukkanin mutanen da suke da buƙata da su fito su sayi fom ɗin.

Daga bisani sai shugaban ya yi ƙira ga jam’iyyun siyasa da masu ruwa da tsaki da su bi dokokin da aka gindaya wajen taimaka wa shirye-shiryen gudanar da zaɓen domin ganin an yi cikin kwanciyar hankali.

Ahmed ya tunatar da ‘yan siyasa da jam’iyyunsu cewa lokacin fara gangamin yaƙin neman zaɓe zai fara ne kwanaki 30 da lokacin gudanar da zaɓen kamar yadda yake ƙunshe cikin doka. Sai ya shawarci masu ruwa da tsaki da su yi biyayya.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Donald Trump Zai Gurfana A Gaban Kotu Kan Tuhumar Da Ake Masa
Manyan Labarai

Trump Ya Ayyana Nijeriya A Matsayin Ƙasar Da Rayuwar Kiristoci Ke Cikin Hatsari

October 31, 2025
Yadda Waliyin Amarya Ya Sace Sadaki A Kano
Manyan Labarai

An Tsare Wani Mutum A Gidan Yari Kan Zargin Kashe Matarsa Saboda Ƙuli-Ƙuli A Kano

October 31, 2025
Gwamna Uba Sani Ya Gabatar Da Kudirorin Raya Jihar Kaduna A Taron Ƙoli Na Biranen Asiya A Dubai 
Labarai

Gwamna Uba Sani Ya Gabatar Da Kudirorin Raya Jihar Kaduna A Taron Ƙoli Na Biranen Asiya A Dubai 

October 31, 2025
Next Post
Cinikayya Tsakanin Sin Da Ketare Ta Karu Da Kaso 6.3

Cinikayya Tsakanin Sin Da Ketare Ta Karu Da Kaso 6.3

LABARAI MASU NASABA

CMG Ta Kammala Gabatar Da Rahoto Kan Ganawar Shugabannin Sin Da Amurka

CMG Ta Kammala Gabatar Da Rahoto Kan Ganawar Shugabannin Sin Da Amurka

October 31, 2025
Ministan Wajen Malawi: Tsarin Ci Gaban Kasar Sin Ya Samar Da Darussa Ga Kasashe Masu Tasowa

Ministan Wajen Malawi: Tsarin Ci Gaban Kasar Sin Ya Samar Da Darussa Ga Kasashe Masu Tasowa

October 31, 2025
Xi: A Shirye Sin Take Ta Hada Hannu Da Canada Wajen Mayar Da Dangantakarsu Bisa Turbar Da Ta Dace

Xi: A Shirye Sin Take Ta Hada Hannu Da Canada Wajen Mayar Da Dangantakarsu Bisa Turbar Da Ta Dace

October 31, 2025
Donald Trump Zai Gurfana A Gaban Kotu Kan Tuhumar Da Ake Masa

Trump Ya Ayyana Nijeriya A Matsayin Ƙasar Da Rayuwar Kiristoci Ke Cikin Hatsari

October 31, 2025
Yadda Waliyin Amarya Ya Sace Sadaki A Kano

An Tsare Wani Mutum A Gidan Yari Kan Zargin Kashe Matarsa Saboda Ƙuli-Ƙuli A Kano

October 31, 2025
Xi Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Kolin Shugabannin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

Xi Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Kolin Shugabannin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

October 31, 2025
Gwamna Uba Sani Ya Gabatar Da Kudirorin Raya Jihar Kaduna A Taron Ƙoli Na Biranen Asiya A Dubai 

Gwamna Uba Sani Ya Gabatar Da Kudirorin Raya Jihar Kaduna A Taron Ƙoli Na Biranen Asiya A Dubai 

October 31, 2025
Ya Kamata Sin Da Amurka Su Zama Kawayen Juna Ba Abokan Gaba Ba

Ya Kamata Sin Da Amurka Su Zama Kawayen Juna Ba Abokan Gaba Ba

October 31, 2025
Zaben 2027 Zai Kasance Ne Tsakanin Mulkin Tinubu Da Zabin Ƴan Nijeriya —Atiku Abubakar

Zaben 2027 Zai Kasance Ne Tsakanin Mulkin Tinubu Da Zabin Ƴan Nijeriya —Atiku Abubakar

October 31, 2025
Makarantar Kogi Poly Ta Bankaɗo Masu Ƙirƙirar Takardun Kammala Karatu na Bogi

Makarantar Kogi Poly Ta Bankaɗo Masu Ƙirƙirar Takardun Kammala Karatu na Bogi

October 31, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.