• English
  • Business News
Saturday, August 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Wike Ya Kafa Tirihin Gudanar Da Ayyukan Ci Gaba A Abuja

by Abubakar Abba
1 year ago
in Labarai
0
Yadda Wike Ya Kafa Tirihin Gudanar Da Ayyukan Ci Gaba A Abuja
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ayyukan ci gaba da aka samar a cikin shekara daya a Abuja, babban birin tarayya, a karkashin shugabancin ministan, Nyesom Wike hakan ya yi matukar janyo hankalin Shugaban kasa, Bola Tinubu da kuma mazauna birnin wajen jinjina wa Wike.

Babu wata tantama, tauraruwar Wike ta haska a idon gwamnatin Tinubu a cikin shekara daya da ta gabata.

  • Xi Ya Yi Rangadi A Lardin Qinghai Da Jihar Ningxia
  • Kotu Ta Rushe Dokar Da Ta Tsige Aminu Ado Bayero A Matsayin Sarkin Kano

Bisa wannan ayyukan na ci gaba da Wike ya samar a Abuja, za a iya cewa tamkar ya dora ne kan irin ayyuakn ci gaba da ya samar a lokacin da yake kan karagar mulkin Jihar Ribas, inda ya yi wa’adin mulkinsa na tsawon shekaru takwas wanda har aka yi masa lakabi da sarkin aiki.

A nan za a iya cewa, nada Wike da Tinubu ya yi a matsayin ministan ya sanya shi farin ciki saboda ayyukan ci gaba da ya samar a Abuja, wanda da a ce, Tinubu ya biye wa surutun mutane na kiraye-kirayen da sukai ta faman yi na ganin cewa ba a nada Wike a mukamin minista, da yanzu irin wannnan ayyukan na ci gaba ba za a samu a Abuja ba.

Shi kan shi Tinubu ya tabbatar da cewa, wasu suka ba shi shawara kar ya nada Wike a wani mukami a cikin gwamnatinsa.

Labarai Masu Nasaba

An NaÉ—a Farfesa Adamu MuÆ™amin Mataimakin Shugaban Jami’ar Yakubu Gowon, Abuja

Gwamnan Kano Ya Sallami Mataimaka Biyu Kan Zargin Karkatar Da Kayan Tallafi

Tinubu ya tabbatar da hakan ne a lokacin kammadar da aikin titin ‘Arterial’ da ke a cikin Abuja wadda aka kashe naira miliyan 20, kuma sauya sunan titin zuwa Wole Soyinka Way.

Tinubu ya ce, “Mai girma minista na zo wajen kaddamar da aikin ne domin na gode maka kai da tawagarka, musamman bisa samar da cin nasara ga gwamnatinmu a cikin shekara daya. Ayyukan da ka gudanar a birnin Abuja sun sa mutane sun ji dadi sosai.

“Zuciyarta na cike da farin ciki da kuma alfahari da kai, domin sun yi tunanin cewa Wike ba zai iya yin wani aikin a zo a gani a matsayin minista ba, sai kuma gashi ba ka bai wa mara da kunya ba. Ayyuakan da kake kirkiro da su a birnin Abuja abun yaba wa ne.

Wike daga jam’iyyar PDP ya fito, wanda kuma ya karbi ajandar shirin Tinubu na magance kalubalen tattalin arziki, rashin tsaro da kuma samar da aikin yi tun lokacin kaddamar da yakin neman zaben 2023, da ake kira a turance, ‘Renewed Hope Agenda’.

Bugu da kari, bisa ayyukan ci gaba da Wike ya kirkiro da su a birnin a cikin shekara daya, wadanda kuma ana ganin su a zahari, hakan ya sanya an samar da sauye-sauyin na ci gaba a birnin a fannoni da dama.

Kazalika, a tarihin birnin ba a taba shafe kwanuka tara cur ana kaddamar da wasu ayyuka da aka yi a birinin ba, sai a lokacin mulkin gwamnatin Tinubu, inda shugaban ya kaddamar da ayyuka daban-daban da aka kirkiro da su a karkashin jagorancin Wike.

Ayyuakann sun hada da, kara kaddamar da aikin safarar jirgin kasa da zai yi zirga-zirga a cikin garin Abuja mai daukar fasinjoji kyauta har tsawon watanni bakwai da aikin gina titin ‘Southern Parkway, S8/S9; da na Christian Centre zuwa titin Ring Road 1; da titin B6, B12, da na Circle da aikin gadar Wuye da gidan mataimakin shugaban kasa da suka lashe kudi har naira biliyan 98.8.

A cewar Wike, kaddamar da wadannan ayyukan, sun nuna a zahairi gwamnatin Tinubu ta mayar da hankali wajen inganta harkokin kasuwanci da kuma inganta rayuwar ‘yan Nijeriya.

A lokacin sake kaddamar da aikin jirgin kasan, Wike ya ayyana yin jigilar matafiya kyauta har na tsawon wata biyu, wanda saboda jin dadin wannan ayyanawar ta Wike, sai Tinubu ya kara fadada jigikar zuwa watan Disamba domin a nuna jin kan gwamnatinsa take da shi ga ‘yan Nijeriya a fannin zirga-zirga.

LEADERSHIP ta ruwaito cewa, hukumar kula da raya birnin Abuja ce ta bayar da kwangilar aikin zirga-zirgar jiragen kasa a cikin birnin a 2007, inda aka fara gudanar da aikin gwaji na aikin daga watan Satumban 2018, inda aka kammala aikin a watan Maris na 2020.

Sai dai aikin zirga-zirgar jirgin ya samu koma baya sakamakon bullar annobar Korona da sace wasu manyan kayan aikin wanda hakan ya janyo aikin ya tsaya cak tun a 2020.

A yayin kaddamar da ayyukan titunan Southern Parkway, S8/S9 da na Christian Centre zuwa titin Ring 1, Tinubu ya ce, kammala ayyukan sun nuna zahirin manufar gwamnatinsa da gaske take don samar da ayyukan ci gaba.

Tinubu ya kaddamar da ayyukan da aka kashe naira biliyan 98.8 na aikin hanyoyin B6, B12 da na Circle da ke birnin, ya ce za su kara bunkasa kasuwanci da kuma inganta raruwar ‘yan Nijeriya.

A cewar Tinubu, zai iya bugun kirji da cewa ya kaddamar da ayyukan hanyoyi B6, B12 da na Circle a tsakiyar birnin Abuja a karkashin kulawar Wike. Ya ce wannan ayyukan tamkar zakaran gwajin dafi ne ga mulkinsa.

Aikin gadar Wuye da za ta sada sauran gundumomin da birnin na daga cikin manyan ayyukan ci gaba da Wike ya samar, domin sama da shekaru 20 da suka gabata ba a yi hakan ba.

Tinubu ya jinjina wa Wike bisa sadaukar da kai na cimma muradun ajandar shugabancinsa da ake kira a turance, ‘ Renewed Hope Agenda’, musamman bisa yadda a zahiri ajandar ta inganta rayuwar mazauna birnin.

A makon da ya gabata ne, aka kammala kaddamar ayyukan a cikin kwana tara, inda Tinubu ya sauya wa babban titin M18 da ke a yankin Guzape Lot II a Abuja, zuwa sunan Chinua Achebe.

Wike ya yi alkawarin kammala ayyukan da ke a yankin jakadu da ke a birnin tare da kuma bai wa Tinubu tabbacin kammala ayyukan a shekara mai zuwa.

Tun a farko, Wike ya kaddamar da ayyukan manyan hanyoyi tare da giggina makarantu a yankuna shida na birnin wadanda idan an kammala su, za a kaddamar da su.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AbujaAyyukaCi GabaWike
ShareTweetSendShare
Previous Post

Xi Ya Jaddada Muhimmancin Kare Muhalli A Wuraren Kewayen Rawayen Kogi

Next Post

Kakakin Ma’aikatar Tsaron Kasar Sin Ya amsa Tambayoyin ’Yan Jaridu Game Da Sayarwa Taiwan Makamai Da Amurka Ta Yi A Sabon Zagaye

Related

An NaÉ—a Farfesa Adamu MuÆ™amin Mataimakin Shugaban Jami’ar Yakubu Gowon, Abuja
Manyan Labarai

An NaÉ—a Farfesa Adamu MuÆ™amin Mataimakin Shugaban Jami’ar Yakubu Gowon, Abuja

55 minutes ago
Gwamnan Kano Ya Sallami Mataimaka Biyu Kan Zargin Karkatar Da Kayan Tallafi
Labarai

Gwamnan Kano Ya Sallami Mataimaka Biyu Kan Zargin Karkatar Da Kayan Tallafi

2 hours ago
Tsohon Shugaban PDP Audu Ogbeh Ya Rasu
Labarai

Tsohon Shugaban PDP Audu Ogbeh Ya Rasu

3 hours ago
Sai An Magance Matsalar Asusun Haɗin Gwiwa, Za A Tabbatar Da Cin Gashin Kan Ƙananan Hukumomi
Labarai

Sai An Magance Matsalar Asusun Haɗin Gwiwa, Za A Tabbatar Da Cin Gashin Kan Ƙananan Hukumomi

5 hours ago
Ƴan Bindiga Sun Sace Fasinjoji 9 A Kogi
Labarai

Ƴan Bindiga Sun Sace Fasinjoji 9 A Kogi

8 hours ago
Gwamnatin Tarayya da Ofishin Jakadancin Amurka Sun Haɗa Gwiwa Don Wayar Da Kan ‘Yan Nijeriya Kan Sababbin Ƙa’idojin Samun Biza
Labarai

Gwamnatin Tarayya da Ofishin Jakadancin Amurka Sun Haɗa Gwiwa Don Wayar Da Kan ‘Yan Nijeriya Kan Sababbin Ƙa’idojin Samun Biza

17 hours ago
Next Post
Kakakin Ma’aikatar Tsaron Kasar Sin Ya amsa Tambayoyin ’Yan Jaridu Game Da Sayarwa Taiwan Makamai Da Amurka Ta Yi A Sabon Zagaye

Kakakin Ma’aikatar Tsaron Kasar Sin Ya amsa Tambayoyin ’Yan Jaridu Game Da Sayarwa Taiwan Makamai Da Amurka Ta Yi A Sabon Zagaye

LABARAI MASU NASABA

Man United Sun Kammala Sayen Benjamin Sesko Daga RB Leipzig

Man United Sun Kammala Sayen Benjamin Sesko Daga RB Leipzig

August 9, 2025
An NaÉ—a Farfesa Adamu MuÆ™amin Mataimakin Shugaban Jami’ar Yakubu Gowon, Abuja

An NaÉ—a Farfesa Adamu MuÆ™amin Mataimakin Shugaban Jami’ar Yakubu Gowon, Abuja

August 9, 2025
Gwamnan Kano Ya Sallami Mataimaka Biyu Kan Zargin Karkatar Da Kayan Tallafi

Gwamnan Kano Ya Sallami Mataimaka Biyu Kan Zargin Karkatar Da Kayan Tallafi

August 9, 2025
Tsohon Shugaban PDP Audu Ogbeh Ya Rasu

Tsohon Shugaban PDP Audu Ogbeh Ya Rasu

August 9, 2025
Ina Fatan Taka Inda Yayana Ya Taka A Fagen Ƙwallon Ƙafa A Duniya -Jobe Bellingham

Ina Fatan Taka Inda Yayana Ya Taka A Fagen Ƙwallon Ƙafa A Duniya -Jobe Bellingham

August 9, 2025
Sai An Magance Matsalar Asusun Haɗin Gwiwa, Za A Tabbatar Da Cin Gashin Kan Ƙananan Hukumomi

Sai An Magance Matsalar Asusun Haɗin Gwiwa, Za A Tabbatar Da Cin Gashin Kan Ƙananan Hukumomi

August 9, 2025
Tinubu Ya Gwangwaje Ƴan Wasan Ƙwallon Kwando Ta Mata Da Dala $100,000 Kowace

Jerin Ƴan Wasa Mata Da Suka Samu Kyautar Dala 100,000 Daga Gwamnatin Nijeriya

August 9, 2025
Afrika Ba Ta Cikin Jerin Fannonin Da Muke Ba Fifiko – Amurka

Afrika Ba Ta Cikin Jerin Fannonin Da Muke Ba Fifiko – Amurka

August 9, 2025
Ƴan Bindiga Sun Sace Fasinjoji 9 A Kogi

Ƴan Bindiga Sun Sace Fasinjoji 9 A Kogi

August 9, 2025
ADA/ADC, APC Da PDP: Jam ’iyyun Siyasa Da Ke Shan Jinin ’Yan Nijeriya

ADA/ADC, APC Da PDP: Jam ’iyyun Siyasa Da Ke Shan Jinin ’Yan Nijeriya

August 9, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.