• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Minista Ya Kaddamar Da Taron Horas Da ‘Yan Jarida Kan Yaƙi Da Aƙidun Ta’addanci

by Sulaiman
12 months ago
in Labarai
0
Minista Ya Kaddamar Da Taron Horas Da ‘Yan Jarida Kan Yaƙi Da Aƙidun Ta’addanci
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya ƙaddamar da taron horas da ‘yan jarida na kwana biyu kan inganta rahotonni domin daƙile aƙidar ta’addanci.

An buɗe taron ne a ranar Talata a Abuja a Ofishin Mai Bai Wa Shugaban Ƙasa Shawara Kan Harkokin Tsaro (ONSA), Malam Nuhu Ribadu.

  • Abu Ɗaya Da Ya Rage Kafin Yanke Hukunci Kan Mafi Ƙarancin Albashi
  • Za Mu Canza Salon Yaƙin Da Muke Yi Da Ƴan Bindiga a Nijeriya – Bola Tunibu

A jawabinsa, Idris ya yaba wa Cibiyar Yaƙi da Ta’addanci ta Ƙasa (NCTC) da ONSA bisa irin ingantattun matakan da suka ɗauka na yaƙi da ta’addanci, ciki har da ayyukan ceto da dama da ba a bayyana ba.

Ya bayyana muhimmancin sadarwar da kafafen yaɗa labarai da suke yi a kai a kai, wanda hakan ke taimaka wa jama’a su fahimci al’amuran ta’addanci da tsaron ƙasa.

Ya ce: “Kafofin yaɗa labarai na da ƙarfi sosai wajen yin tasiri ga mutane da kuma inganta zaman lafiya.”

Labarai Masu Nasaba

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

Ministan ya jaddada cewa ko dai ‘yan jarida na iya cutarwa ko kuma su taimaka wajen yaƙi da tsauraran aƙidu inda ya ƙara da cewa kyakkyawan rahoto zai iya ilimantar da jama’a domin su guje wa ta’addanci.

Ya buƙaci ‘yan jarida da su riƙa ba da sahihan labarai da ke cin karo da saƙwannin ‘yan ta’adda da kuma nuna nasarorin shirye-shiryen NCTC da ONSA waɗanda ke taimakawa wajen hana tayar da zaune tsaye da sake dawo da tsofaffin ‘yan ta’adda.

Ya kuma buƙaci ‘yan jarida da su yi aiki tare da masana harkokin tsaro, masana ilimin zamantakewa, masana ilimin halayyar ɗan’adam, da shugabannin al’umma don samar da ra’ayi mabambanta game da ta’addanci da hanyoyin sa.

Idris ya ce yin amfani da bayanai da bincike na iya sa labaran su su zama abin dogaro.

Ya sake jaddada goyon bayan Gwamnatin Tinubu ga aikin jarida, tare da yin alƙawarin ci gaba da bayar da sahihan bayanai na yau da kullum, da damarmarkin horaswa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Ministan Yaɗa LabaraiNUJYada Labarai
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kafa Kananan Rukunoni Ba Zai Haifar Da Komai Ba Face Tsananta Sabani

Next Post

Li Qiang: Sin Za Ta Samar Da Karin Dama Da Yanayi Mai Kyau Ga Masu Zuba Jari Na Kasa Da Kasa

Related

Daurarru
Labarai

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

2 hours ago
Wutar lantarki
Labarai

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

4 hours ago
Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka
Labarai

Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

5 hours ago
Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano
Manyan Labarai

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

6 hours ago
An Kama Wadanda Ake Zargi Da Kai Wa Shugaban Kwadago Hari Ribadu
Labarai

Ribadu Ya Kara Jaddada Gargadinsa Kan Biyan Kudin Fansa Ga Masu Garkuwa Da Mutane

8 hours ago
Gwamnatin Tarayya Na Yunkurin Rage Dala Biliyan 1.5 Da Ake Kashewa Wajen Shigo Da Madara
Labarai

Gwamnatin Tarayya Na Yunkurin Rage Dala Biliyan 1.5 Da Ake Kashewa Wajen Shigo Da Madara

9 hours ago
Next Post
Li Qiang: Sin Za Ta Samar Da Karin Dama Da Yanayi Mai Kyau Ga Masu Zuba Jari Na Kasa Da Kasa

Li Qiang: Sin Za Ta Samar Da Karin Dama Da Yanayi Mai Kyau Ga Masu Zuba Jari Na Kasa Da Kasa

LABARAI MASU NASABA

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

June 6, 2025
Daurarru

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

June 6, 2025
Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

June 6, 2025
Wutar lantarki

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

June 6, 2025
Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

June 6, 2025
Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

June 6, 2025
Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

June 6, 2025
An Kama Wadanda Ake Zargi Da Kai Wa Shugaban Kwadago Hari Ribadu

Ribadu Ya Kara Jaddada Gargadinsa Kan Biyan Kudin Fansa Ga Masu Garkuwa Da Mutane

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.