• English
  • Business News
Tuesday, October 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Me Ya Sa Gasar Cin Kofin Turai Ta Fi Son Yin Hadin Gwiwa Da Kamfanonin Kasar Sin

by Sulaiman and CGTN Hausa
1 year ago
Turai

LABARAI MASU NASABA

Masanan Kasar Sin Da Afirka Sun Hada Karfi Da Karfe Don Habaka Samun Wadatar Abinci Da Zamanantar Da Aikin Gona

Kuri’un Jin Ra’ayin Jama’a Na CGTN Sun Nuna Gamsuwar Jama’a Ga Tsarin Jagoranci Na Sin

A halin yanzu, ana gudanar da gasar cin kofin Turai wato UEFA Euro 2024, wadda ke jan hankulan masu sha’awar wasan kwallon kafa na kasa da kasa. A yayin da ake gudanar da irin wannan gasa ta koli, a kan fitar da muhimman labarai na bunkasuwar tattalin arzikin kasashen duniya. A matsayin gasar wasannin kwallon kafa dake kan matsayin koli, wadda aka gudanar bayan annobar cutar COVID-19, gasar cin kofin Turai ta wannan karo tana da manyan iyayen tafiya guda 13, wadanda aka fi sani da abokan hadin gwiwarta na kasashen duniya. Cikin wadannan manyan iyaye tafiya guda 13, akwai na kasar Sin guda 5, hakan ya sa, Sin ta kasance kasar da gasar cin kofin Turai ta fi samun iyayen tafiya cikin gasar ta wannan karo da ma wanda ya gabata.

A gasar bana, iyayen tafiya guda biyar daga kasar Sin sun hada da sana’o’in samar da na’urorin wutar lantarki masu kwakwalwa, da motoci masu aiki da wutar lantarki, da salula masu kwakwalwa, da masu gudanar da harkokin ciniki ta yanar gizo tsakanin kasa da kasa, gami da sana’ar nazarin fasahohin biyan kudi da sauransu. Dukkansu suna sahun gaba cikin sabbin sana’o’in dake samun bunkasuwa da sauri a kasashen duniya.

  • Shugaba Xi Na Kasar Sin Ya Amsa Wasikar Da Mutanen Gundumar Jingning Suka Aika Masa
  • Xi: A Shirya Sin Take Ta Daukaka Dangantakarta Da Poland Zuwa Sabon Matsayi

Cikin ’yan shekarun nan, wasu kamfanonin kasar Sin dake kan gaba a fannoninsu, sun kafa cibiyoyin nazari da masana’antu a kasashen waje, lamarin da ya samar da guraben ayyukan yi ga kasashen da abin ya shafa, tare da ya ba da gudummawar kyautata fasahohinsu. Wadannan kamfanonin suna ci gaba da sabunta kayayyakinsu, yayin da suke kyautata tsarin gudanarwa da ayyukansu, domin samar wa masu sayyaya na kasashen duniya kyawawan kayayyaki da hidimomi masu inganci, kuma masu kare muhalli. Haka kuma, sun shiga kasuwannin duniya, yayin da suke gasa da kamfanonin kasa da kasa cikin yanayin adalci, bisa tunanin bude kofa ga waje.

A halin yanzu, irin babbar gasar dake jan hankulan jama’ar kasashen duniya kamar gasar cin kofin Turai, suna maraba da kamfanonin kasar Sin, ba kawai domin kamfanonin kasar Sin suna da kudi ba, domin suna amincewa da kasar Sin da yadda take yin kwaskwarimar tattalin arziki a cikin gida, domin sa kaimi ga kamfanonin kasar su yi kirkire-kirkire, da kuma ba da jagoranci ga kasashen duniya wajen sabunta fasahohinsu. Kamar yadda wasu masanan tattalin arzikin kasashen duniya suka bayyana, ya kamata iyayen tafiya na irin wannan gasar da take da tasiri ga al’ummomin kasa da kasa, su kasance daga kamfanonin dake iya alamta bunkasuwar tattalin arzikin duniya, da ma wadanda ke yin muhimmin tasiri ga kasashen duniya. (Mai Fassarawa: Maryam Yang)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Masanan Kasar Sin Da Afirka Sun Hada Karfi Da Karfe Don Habaka Samun Wadatar Abinci Da Zamanantar Da Aikin Gona
Daga Birnin Sin

Masanan Kasar Sin Da Afirka Sun Hada Karfi Da Karfe Don Habaka Samun Wadatar Abinci Da Zamanantar Da Aikin Gona

October 28, 2025
Kuri’un Jin Ra’ayin Jama’a Na CGTN Sun Nuna Gamsuwar Jama’a Ga Tsarin Jagoranci Na Sin
Daga Birnin Sin

Kuri’un Jin Ra’ayin Jama’a Na CGTN Sun Nuna Gamsuwar Jama’a Ga Tsarin Jagoranci Na Sin

October 28, 2025
An Kusa Kammala Shirye-shiryen Baje Kolin CIIE Karo Na Takwas
Daga Birnin Sin

An Kusa Kammala Shirye-shiryen Baje Kolin CIIE Karo Na Takwas

October 28, 2025
Next Post
Ana Ganawa Tsakanin ASUU Da Gwamnatin Tarayya

Ana Ganawa Tsakanin ASUU Da Gwamnatin Tarayya

LABARAI MASU NASABA

Zamfara Ta Fara Sauyawa Zuwa Jihar Fasahar Zamani, In ji Gwamna Lawal

Zamfara Ta Fara Sauyawa Zuwa Jihar Fasahar Zamani, In ji Gwamna Lawal

October 28, 2025
Masanan Kasar Sin Da Afirka Sun Hada Karfi Da Karfe Don Habaka Samun Wadatar Abinci Da Zamanantar Da Aikin Gona

Masanan Kasar Sin Da Afirka Sun Hada Karfi Da Karfe Don Habaka Samun Wadatar Abinci Da Zamanantar Da Aikin Gona

October 28, 2025
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Ajali Tare Da Jikkata Wasu A Gombe

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Ajali Tare Da Jikkata Wasu A Gombe

October 28, 2025
Kuri’un Jin Ra’ayin Jama’a Na CGTN Sun Nuna Gamsuwar Jama’a Ga Tsarin Jagoranci Na Sin

Kuri’un Jin Ra’ayin Jama’a Na CGTN Sun Nuna Gamsuwar Jama’a Ga Tsarin Jagoranci Na Sin

October 28, 2025
Kano Ta Bai Wa Mata 5,200 Tallafin Naira Miliyan 260

Kano Ta Bai Wa Mata 5,200 Tallafin Naira Miliyan 260

October 28, 2025
An Kusa Kammala Shirye-shiryen Baje Kolin CIIE Karo Na Takwas

An Kusa Kammala Shirye-shiryen Baje Kolin CIIE Karo Na Takwas

October 28, 2025
Gwamna Bago Ya Amince Da Biyan Karin Albashin Naira 20,000 Ga Ma’aikata 

Gwamnatin Neja Ta Bayar Da Hutun Kwanaki 2 Don Zaɓen Ƙananan Hukumomi

October 28, 2025
Fasahohin Sin Za Su Iya Kyautata Makomar Nahiyar Afrika

Fasahohin Sin Za Su Iya Kyautata Makomar Nahiyar Afrika

October 28, 2025
Xi Ya Yi Karin Haske Kan Muhimman Shawarwarin Da Kwamitin Kolin JKS Ya Gabatar Yayin Tsara Shirin Raya Kasa Karo Na 15

Xi Ya Yi Karin Haske Kan Muhimman Shawarwarin Da Kwamitin Kolin JKS Ya Gabatar Yayin Tsara Shirin Raya Kasa Karo Na 15

October 28, 2025
gaza

Majalisar Dattawa Ta Maido Da Ranar Tantance Sabbin Shugabannin Sojoji Zuwa Laraba

October 28, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.