• English
  • Business News
Wednesday, June 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Xi Jinping Ya Yi Shawarwari Tare Da Takwaransa Na Kasar Guinea Bissau

by Sulaiman and CGTN Hausa
11 months ago
in Daga Birnin Sin
0
Xi Jinping Ya Yi Shawarwari Tare Da Takwaransa Na Kasar Guinea Bissau
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Da maraicen yau Laraba 10 ga watan nan ne, a babban dakin taron al’umma dake Beijing, shugaban kasar Sin Xi Jinping, ya yi shawarwari tare da takwaransa na kasar Guinea Bissau, Umaro Mokhtar Sissoco Embaló, wanda a yanzu haka yake ziyarar aiki a kasar, inda shugabannin biyu suka amince da daga matsayin dangantakarsu zuwa dangantakar abokantaka bisa manyan tsare-tsare.

A yayin shawarwarin, Xi Jinping ya bayyana cewa, kasar Sin da Afirka dukkansu suna da wayewar kai mai burgewa, kuma dukkansu na dakon tarihin mulkin mallaka da mamaya da aka musu, kuma dukkansu na mutunta tare da tabbatar da ‘yancin kai da ‘yancin kasa. Kasar Sin da kasashen Afirka na taimakawa juna cikin gaskiya, kuma sun zama abin koyi na hadin gwiwar da ke tsakanin kasashe masu tasowa. Za a gudanar da sabon taron koli na dandalin tattaunawar hadin gwiwa tsakanin Sin da Afirka a Beijing a wannan kaka. Kasar Sin a shirye take ta yi hadin gwiwa tare da Guinea Bissau da sauran kasashen Afirka, domin tattaunawa kan tsare-tsaren hadin gwiwa tsakanin Sin da Afirka a wannan sabon zamani, da kare moriyar kasashe masu tasowa, da daidaito da adalci tsakanin kasa da kasa, da yin hadin gwiwa don gina wata babbar al’umma mai makomar bai daya ga Sin da Afirka, da sa kaimi ga gina al’umma mai makomar bai daya ga bil Adama.

  • Fakewa Da Batun Kasar Sin Ba Zai Taimaka Wa NATO Cimma Burinta Da Ya Shafi Yankin Asiya Da Tekun Pasifik Ba
  • Binciken CGTN Ya Nuna Yadda Masu Bayyana Ra’ayoyi Suka Zargi Nuna Fin Karfi Da Amurka Ta Yi A Harkokin Intanet

A nasa bangare, Embaló ya ce, kasar Sin ba ta taba yin mulkin mallaka ba, ba ta taba tsoma baki cikin harkokin cikin gidan wasu kasashe ba, ba ta taba yin katsalandan ga sauran kasashe ba, kuma tana girmama kananan kasashe da daidaito da mutuntawa. Kasar Sin ta kasance tana bin kalamanta da ayyuka. Abin da kasar Sin ta kawo wa kasashen Afirka shi ne makarantu, asibitoci, hanyoyi da sauran ayyukan hadin gwiwa da ke amfanar jama’ar Afirka. Kasar Guinea-Bissau ta yaba da muhimmiyar rawar da kasar Sin take takawa, da kyakkyawar gudummawar da take bayarwa wajen taimakawa ci gaban nahiyar Afirka, kuma tana goyon bayan kasar Sin sosai wajen karbar bakuncin sabon taron koli na dandalin tattaunawar hadin gwiwar Sin da Afirka.

Bayan tattaunawar, shugabannin kasashen biyu, tare suka rattaba hannu kan wasu takardu kan aiwatar da shirin raya kasa da kasa, da raya tattalin arziki, da binciken kwastam, da nazarin kasa da ma’adinai. (Yahaya)

 

Labarai Masu Nasaba

Manufar Bude Kofa Ta Shaida Niyyar Sin Ta Ingiza Dunkulewar Duniya

Sin Ta Yi Fatali Da Ikirarin Amurka Cewa Ta Karya Yarjejeniyar Tattaunawar Geneva


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AmurkaKasuwanciSin
ShareTweetSendShare
Previous Post

Shugaban Ƙasa Bola Tinubu Ya Yi Sabbin Naɗe-Naɗe 8

Next Post

‘Yansanda Sun Kama Barawon Babura 6 A Sokoto

Related

Manufar Bude Kofa Ta Shaida Niyyar Sin Ta Ingiza Dunkulewar Duniya
Daga Birnin Sin

Manufar Bude Kofa Ta Shaida Niyyar Sin Ta Ingiza Dunkulewar Duniya

15 hours ago
Sin Ta Yi Fatali Da Ikirarin Amurka Cewa Ta Karya Yarjejeniyar Tattaunawar Geneva
Daga Birnin Sin

Sin Ta Yi Fatali Da Ikirarin Amurka Cewa Ta Karya Yarjejeniyar Tattaunawar Geneva

16 hours ago
Karuwar Darajar Sana’ar Samar Da Kayan Laturoni Da Dangoginsu a Sin Cikin Watanni 4 Na Farkon Bana Ya Karu Da 11.3% 
Daga Birnin Sin

Karuwar Darajar Sana’ar Samar Da Kayan Laturoni Da Dangoginsu a Sin Cikin Watanni 4 Na Farkon Bana Ya Karu Da 11.3% 

16 hours ago
Masani Kwadifwa: Kasar Sin Ce Mai Kare Tabbatuwar Adalci A Duniya
Daga Birnin Sin

Masani Kwadifwa: Kasar Sin Ce Mai Kare Tabbatuwar Adalci A Duniya

18 hours ago
An Samu Karuwar Kaso 2.7 Na Yawan Tafiye-Tafiye Zuwa Ketare Yayin Hutun Bikin Dragon Boat Na Kasar Sin
Daga Birnin Sin

An Samu Karuwar Kaso 2.7 Na Yawan Tafiye-Tafiye Zuwa Ketare Yayin Hutun Bikin Dragon Boat Na Kasar Sin

19 hours ago
Darajar Hajojin Da Aka Yi Jigilarsu a Kasuwar Sin Daga Watan Janairu Zuwa Na Afrilu Ta Karu Da 5.6% 
Daga Birnin Sin

Darajar Hajojin Da Aka Yi Jigilarsu a Kasuwar Sin Daga Watan Janairu Zuwa Na Afrilu Ta Karu Da 5.6% 

21 hours ago
Next Post
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

'Yansanda Sun Kama Barawon Babura 6 A Sokoto

LABARAI MASU NASABA

DSS

DSS Da Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 45 A Neja

June 4, 2025
Gwamna Bago Ya Amince Da Biyan Karin Albashin Naira 20,000 Ga Ma’aikata 

Yanzu-yanzu: Gwamnatin Neja Ta Soke Hawan Sallah Sakamakon Ambaliyar Ruwan Mokwa

June 4, 2025
katsina

Gwamnan Katsina Ya Bukaci Hadin Gwiwa Da ‘Yan Kasuwa Domin Cigaban Jihar

June 4, 2025
Ambaliya: Gwamna Zulum Ya Kaddamar Da Rabon Kayan Agaji A Borno

Zulum Ya Yaba Wa Sojoji Kan Kashe Babban Kwamandan ISWAP Abu Fatima

June 4, 2025
Manufar Bude Kofa Ta Shaida Niyyar Sin Ta Ingiza Dunkulewar Duniya

Manufar Bude Kofa Ta Shaida Niyyar Sin Ta Ingiza Dunkulewar Duniya

June 3, 2025
Kocin Inter Milan Simone Inzaghi Ya Bar Kungiyar Kwanaki Biyu Bayan Rashin Nasara A Hannun PSG

Kocin Inter Milan Simone Inzaghi Ya Bar Kungiyar Kwanaki Biyu Bayan Rashin Nasara A Hannun PSG

June 3, 2025
Sin Ta Yi Fatali Da Ikirarin Amurka Cewa Ta Karya Yarjejeniyar Tattaunawar Geneva

Sin Ta Yi Fatali Da Ikirarin Amurka Cewa Ta Karya Yarjejeniyar Tattaunawar Geneva

June 3, 2025
Karuwar Darajar Sana’ar Samar Da Kayan Laturoni Da Dangoginsu a Sin Cikin Watanni 4 Na Farkon Bana Ya Karu Da 11.3% 

Karuwar Darajar Sana’ar Samar Da Kayan Laturoni Da Dangoginsu a Sin Cikin Watanni 4 Na Farkon Bana Ya Karu Da 11.3% 

June 3, 2025
Sanusi

‘Yansanda A Kano Sun Gargaɗi Sarki Sanusi II Kan Fitowa Hawan Sallah

June 3, 2025
Masani Kwadifwa: Kasar Sin Ce Mai Kare Tabbatuwar Adalci A Duniya

Masani Kwadifwa: Kasar Sin Ce Mai Kare Tabbatuwar Adalci A Duniya

June 3, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.