• English
  • Business News
Sunday, June 1, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Har Yanzu Tukunyar Rikicin Masarautar Kano Na Tafarfasa

by Sulaiman and Abdullahi Muh'd Sheka
11 months ago
in Labarai
0
Kano
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Duk da sa bakin wasu da ake kallo a matsayin wadanda karansu ya kai tsaiko, ku-ma ake da kyakkyawan zaton idan suka ce ga yadda za a yi, to za a yi wa tufkar hanci, amma dai har yanzu kura tukunyar rikicin masarautun Kano na ci gaba da kara tafasa.

Wannan shi ne irinsa na farko a tarihin masarautar Kano, masu sarhi sun hakikance cewar siyasa ce ke zaman musabbabin wannan danbarwa. Wanda kuma idan ba a yi wa tufkar hanci ba, za ta iya zama wata gobara daga teku. Mu-samman Ganin yadda lamarin ya fara yaduwa zuwa wasu masarautun wadan-da zuwa yanzu aka jin yadda aka fara yamutsa gashin baki.

  • Ganduje Da Mai Dakinsa Za Su Gurfana A Gaban Kotu A Kano
  • Matsalar Tsaro: Gwamnatin Zamfara Ta Sanya Dokar Takaita Zirga-zirgar Ababen Hawa

Yanzu haka an fara jin motsin irin wannan matsalar ta fara fitowa a wasu jihohi biyu na arewacin kasar nan, wanda suka hada da Sakwato da Katsina. A Jihar Sakwato har an kai irin wannan kudiri gaban majalisar dokokin jihar, inda ake za-ton irin wannan guguwar na neman yin awon gaba da rawanin Mai Alfarma Sarkin Musulmi, Alhaji Sa’ad Abubakar. Yayin da a Jihar Katsina kuwa, shi ma Mai Martaba Sarkin Kataina, ya karbi takardar da ke neman ya yi bayanin dalilinsa na kin yin hawan sallar da ta gabata.

Yanzu haka lamarin kullum daukar sabon salo yake a Masarautar ta Kano, domin kamar yadda aka sani sarakuna biyu ke mulki a Kano, guda ya samu rakiya tare da kariyar gwamna, wanda aka shigar da shi gidan Rumfa cikin dare, yayin da daya bangaren kuma yake gudanar da mulki daga gidan Nassarawa, wurin da ke samun tsaro daga jami’an ‘yansanda da sojoji.

A bangaren rundunar ‘yansanda kuwa, ta shelanata yin tsayuwar daka kancewar tana bin umarnin kotu ne, don haka take bayar da kariya ga Sarki Aminu Ado Bayero, inda wata kotu ta dakatar da Gwamnan Abba Kabir Yusuf daga ci gaba da daukar kowane irin mataki a kansa har sai ta kammala shari’ar da ke gabanta.

Labarai Masu Nasaba

Bam Ya Kashe Mutane 9 A Wata Tashar Motoci Da Ke Borno 

NDLEA Ta Cafke Masu Tura Alhazai Saudiyya Domin Safarar Hodar Iblis Zuwa Kasar

Sai dai kuma gwamna ya sa kafa ya yi fatali da umarnin na kotun, ya rattaba wa dokar hannu da aka yi wa kwaskwarima tare da damka wa Muhammadu Sanusi II takarda sake dawo da shi a matsayin sarkin Kano na 16.

Haka zalika, ana ta samun mabanbantan tunani, inda wasu ke tururuwar zuwa fadar gidan Runfa domin yin mubayi’a ga Sarki na 16, Muhammadu Sanusi II, mu-samman jami’an gwamnati da masu biyayya ga darikar kwankwasiyya, wannan tasa wata kididdiga ta nuna cewa Sarkin Kano na 16 ya karbi mubayi’ar hakimai sama da guda 40, wanda kuma wannan kamar yadda wata majiya ta tsegunta wa wakilinmu na samun umarnin zuwa mubayi’ar ne daga fadar gwamnati, kuma suna zuwa domin gudun asarar rawaninsu.

Kamar yadda aka sani akwai kararraki har guda uku da ke gaban kotuna, inda wa-ta kotun tuni ta yi fatali da nade-naden da gwamna ya yi ta kuma tabbatar da ce-wa, Aminu Ado ne halastaccen Sarki. Bayan yanke wannan hukunci ne kotun ta mika wa kotun da bangaren gwamnati ta daukaka kara domin ci gaba da shari’ar. Haka kuma akwai kotun da tuni ta yanke hukunci tare da cin tarar gwamnatin Ka-no har naira miliyon 10.

Sannan akwai kotun da gwamnatin Kano tare da majalisar dokokin Jihar Kano su-ka kai kara, inda kotun ta ba da umarnin lallai a fitar Sarki Aminu Ado Bayero daga gidan Nassarawa. Wannan kotun na karkashin Mai Shari’a Amina Adamu Aliyu.

A cikin makon da ya gabata ne kuma aka wayi gari da ganin an tayar da tuta a gidan Sarki Nassarawa, wanda hakan wata shaida ce da ke nuna cewa sarki na nan, kuma bisa muhimmancin wannan tuta wadda ita ce shaidar tutar da Shehu Usman Danfodio ya raba wa sarakunan Musulunci.

A martanin daya bangaren ta bakin shugaban jam’iyyar NNPP, Alhaji Hashimu Dugurawa ya bayyana cewa wannan tuta ba ta wuce kokarin da wani ke yi na ku-la da makabartar da ake bizne iyayensu a ciki ba.

Dugurawa ya ce wadancan sarakuna biyar ba su da maraba da kwamishinoni, domin an nada su ne saboda su taimaka wa Ganduje cin zabe, kuma ya fadi, don haka a cewarsa ya yi mamakin da tuni ma ba su sauka daga kujerun da suke kai ba kasancewar shi ma Ganduje ya bar tasa kujerar.

Yanzu haka dai an samu matsayar kutna biyu cikin ukun da ke gaban alkalai, inda kutuna biyu suka zantar da hukuncin da ke nuni ga halascin Sarkin Aminu Ado Bayero, duk da cewa kotun gwmanatin ta yanke hukunci ne kan nade-naden da Ganaduje ya aiwatar bayan samun umarnin kotu na tsaya wuri guda har zuwa lo-kacin da kotun za ta kammala sauraron korafin da aka gabatar mata.

Gwamna Abba ya yi tali da umarnin na kotu duk irin kallon da duniya ke masa na cewa shi kansa ribar hukuncin kotuna yake ci, domin da kotu ba ta ba shi nasara a shari’ar da kowa ya yanke tsammanin samun nasarar jam’iyyar NNPP ba, sakamakon hukuncin kwace kujerar har karo biyu da kotun farko da ta biyu suka yi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Alakar siyasa da sarautaRikicin Masarautar KanoSarakunan Arewa
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ginin Makaranta Ya Rufta A Jos, Ɗalibai Da Dama Sun Maƙale

Next Post

Cika Shekara 100 A Duniya: Tarihin Shaikh Dahiru Bauchi Daga Bakinsa

Related

bakin wake
Labarai

Bam Ya Kashe Mutane 9 A Wata Tashar Motoci Da Ke Borno 

48 minutes ago
NDLEA Ta Cafke Masu Tura Alhazai Saudiyya Domin Safarar Hodar Iblis Zuwa Kasar
Labarai

NDLEA Ta Cafke Masu Tura Alhazai Saudiyya Domin Safarar Hodar Iblis Zuwa Kasar

3 hours ago
Gwamnan kano
Manyan Labarai

Gwamna Yusuf Ya Bada Hutu A Ranar Litinin Domin Addu’o’i Ga ‘Yan Wasan Kano 22

5 hours ago
Gwamna Dikko Zai Sake Tsarin Babbar Kasuwar Jihar Katsina
Labarai

Majalisar Dokokin Katsina Ta Ayyana Gwamna Radda A Matsayin Dan Takara Daya Tilo A 2027

5 hours ago
An Karrama Dalibar Kaduna Da Ta Zo Ta Biyu A Gasar Karatun Alkur’ani Ta Duniya
Labarai

An Karrama Dalibar Kaduna Da Ta Zo Ta Biyu A Gasar Karatun Alkur’ani Ta Duniya

6 hours ago
Gwamnatin Kano Ta Ba Iyalan Mamatan Wasanni Tallafin Naira Miliyan Ɗaya Kowane
Manyan Labarai

Gwamnatin Kano Ta Ba Iyalan Mamatan Wasanni Tallafin Naira Miliyan Ɗaya Kowane

18 hours ago
Next Post
Cika Shekara 100 A Duniya: Tarihin Shaikh Dahiru Bauchi Daga Bakinsa

Cika Shekara 100 A Duniya: Tarihin Shaikh Dahiru Bauchi Daga Bakinsa

LABARAI MASU NASABA

bakin wake

Bam Ya Kashe Mutane 9 A Wata Tashar Motoci Da Ke Borno 

June 1, 2025
‘Yan Wasan Da Tauraruwar Ronaldo Da Messi Ta Hana Su Haskawa

‘Yan Wasan Da Tauraruwar Ronaldo Da Messi Ta Hana Su Haskawa

June 1, 2025
NDLEA Ta Cafke Masu Tura Alhazai Saudiyya Domin Safarar Hodar Iblis Zuwa Kasar

NDLEA Ta Cafke Masu Tura Alhazai Saudiyya Domin Safarar Hodar Iblis Zuwa Kasar

June 1, 2025
SULEJA – An Ci Moriyar Ganga (3)

SULEJA – An Ci Moriyar Ganga (3)

June 1, 2025
Gwamnan kano

Gwamna Yusuf Ya Bada Hutu A Ranar Litinin Domin Addu’o’i Ga ‘Yan Wasan Kano 22

June 1, 2025
Gwamna Dikko Zai Sake Tsarin Babbar Kasuwar Jihar Katsina

Majalisar Dokokin Katsina Ta Ayyana Gwamna Radda A Matsayin Dan Takara Daya Tilo A 2027

June 1, 2025
An Karrama Dalibar Kaduna Da Ta Zo Ta Biyu A Gasar Karatun Alkur’ani Ta Duniya

An Karrama Dalibar Kaduna Da Ta Zo Ta Biyu A Gasar Karatun Alkur’ani Ta Duniya

June 1, 2025
Yadda Jarumai A Masana’antar Kannywood Ke Auren Junansu

Yadda Jarumai A Masana’antar Kannywood Ke Auren Junansu

June 1, 2025
Alfanu Da Rashin Alfanun Tallata Shirin Aure Tun Kafin Lokacin Ya Zo

Alfanu Da Rashin Alfanun Tallata Shirin Aure Tun Kafin Lokacin Ya Zo

June 1, 2025
Yadda Za Ki Hada Funkasonki

Yadda Za Ki Hada Funkasonki

June 1, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.