• English
  • Business News
Tuesday, October 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ko Talakawa Za Su Amfana Da Shinkafar Da Aka Raba Wa Jahohi?

by Khalid Idris Doya
1 year ago
Talakawa

Gwamnatin tarayya ta ce, ta kammala dukkanin shirye-shiryen da suka dace na raba tirelolin shinkafa guda 20 ga kowace jiha daga cikin jihohi 36 da Babban Birnin Tarayya Abuja, domin ganin an rabar wa talakawa da suke fama da talauci da fatara a wani yunkuri na kawo karshen matsalar yunwa da ake ciki a fadin kasar nan.   

Ministan yada labarai da wayar da kan jama’a, Mohammed Idris, shi ne ya shaida hakan a ranar Litinin biyo bayan zaman majalisar zartaswa ta kasa wanda Shugaban kasa, Bola Tinubu ya jagoranta.

  • Sin Ta Kaddamar Da Mataki Na Biyu Na Tallafawa Madagascar Shuka Shinkafa Mai Aure
  • Ina Iya Kera Na’urorin Da Suka Fi Na Kasashen Waje Inganci, In ji Adam

A cewar ministan, majalisar zartaswar ta tattauna sosai kan yadda za a shawo kan matsalolin karancin abinci a fadin kasar nan, don haka ta umarci a rabar da tireloli 20 na shinkafa ga kowace jiha domin rabarwa ga marasa karfi a cikin al’umma don yaki da yunwa.

Ya ce, “Majalisar zartaswar Nijeriya ta yi muhawara sosai kan yadda za a samu raba abinci da kuma kawo karshen karancin abinci a kasar, don haka, zuwa yanzu tireloli 20 na shinkafa tuni aka rabar da su ga kowace jiha ciki har da Babban Birnin Tarayya Abuja.

“Gwamnatin tarayya ta amince da hakan a matsayin matakin farko na rage kaifin matsin rayuwa da jama’an Nijeriya ke ciki, amma abincin zai je hannun marasa karfi ne kawai da suke cikin al’umma,” ya tabbatar.

LABARAI MASU NASABA

GORON JUMA’A

GORON JUMA’A

Sai dai masu sharhi na yau da kullum suna ganin cewa shin kafan ba za su isa zuwa talakawan da ake bukata, domin a baya ai gwamnati ta yi irin wannan kokari amma kuma abun bai yi nasara ba.

Haka kuma wasu na ganin cewa tirilolin shinkafa guda 20 ba abin da zai iya yi a jihohin, domin mabukata suna da matukar yawa a Nijeriya.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Goron Sallah
Madubin Rayuwa

GORON JUMA’A

October 3, 2025
Goron Sallah
Madubin Rayuwa

GORON JUMA’A

September 26, 2025
Yadda Wasu Mata Ke Gwada Mazansu Ta Hanyar Magana Da Su Ta Wasu Hanyoyi Don Sanin Ku Suna Kula Mata
Madubin Rayuwa

Yadda Wasu Mata Ke Gwada Mazansu Ta Hanyar Magana Da Su Ta Wasu Hanyoyi Don Sanin Ku Suna Kula Mata

September 21, 2025
Next Post
Kwamitin Tsakiyar Jami’iyyar Kwaminis Ta Kasar Sin Ya Kira Taron Ba Mambobinsa Ba

Kwamitin Tsakiyar Jami’iyyar Kwaminis Ta Kasar Sin Ya Kira Taron Ba Mambobinsa Ba

LABARAI MASU NASABA

Fasahohin Sin Za Su Iya Kyautata Makomar Nahiyar Afrika

Fasahohin Sin Za Su Iya Kyautata Makomar Nahiyar Afrika

October 28, 2025
Xi Ya Yi Karin Haske Kan Muhimman Shawarwarin Da Kwamitin Kolin JKS Ya Gabatar Yayin Tsara Shirin Raya Kasa Karo Na 15

Xi Ya Yi Karin Haske Kan Muhimman Shawarwarin Da Kwamitin Kolin JKS Ya Gabatar Yayin Tsara Shirin Raya Kasa Karo Na 15

October 28, 2025
gaza

Majalisar Dattawa Ta Maido Da Ranar Tantance Sabbin Shugabannin Sojoji Zuwa Laraba

October 28, 2025
Duk Da Barazanar Tattalin Arzikin Duniya, Kasar Sin Ta Sanya Tabbaci Da Kwanciyar Hankali A Duniyarmu Mai Cike Da Ruɗani

Duk Da Barazanar Tattalin Arzikin Duniya, Kasar Sin Ta Sanya Tabbaci Da Kwanciyar Hankali A Duniyarmu Mai Cike Da Ruɗani

October 28, 2025
Ina Fatan Buga Kofin Duniya Na 2026 — Messi

Ina Fatan Buga Kofin Duniya Na 2026 — Messi

October 28, 2025
Tsohon Kwamishina Ya Zargi Gwamnatin Kano Da Sayar Da Filin Makaranta Kan Miliyan 100

Tsohon Kwamishina Ya Zargi Gwamnatin Kano Da Sayar Da Filin Makaranta Kan Miliyan 100

October 28, 2025
An Matsa Min Sai Na Koma Jam’iyyar APC – Gwamnan Filato

An Matsa Min Sai Na Koma Jam’iyyar APC – Gwamnan Filato

October 28, 2025
’Yansanda Sun Ƙaryata Rahoton Ƙone Gidan Shugaban Jam’iyyar PDP A Bauchi

’Yansanda Sun Ƙaryata Rahoton Ƙone Gidan Shugaban Jam’iyyar PDP A Bauchi

October 28, 2025
Mutum 18 Sun Mutu, 40 Sun Jikkata A Hatsarin Mota A Kebbi 

An Kashe Mutum 10 A Harin Ramuwar Gayya A Jihar Kebbi

October 28, 2025
Ganduje Na Kara Shan Matsin Lamba A Kan Ya Sauka

Zargin Almundahana: An Ɗage Shari’ar  Ganduje Da Matarsa Saboda Rashin Miƙa Takardu

October 28, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.