• English
  • Business News
Thursday, September 18, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hukumar SEMA Ta Jihar Kebbi Ta Tallafa Wa Mutanen Da Ambaliyar Ruwan Sama Ta Shafa A Argungu

by Sulaiman and Umar Faruk Birnin Kebbi
1 year ago
in Labarai
0
Hukumar SEMA Ta Jihar Kebbi Ta Tallafa Wa Mutanen Da Ambaliyar Ruwan Sama Ta Shafa A Argungu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A sanyin safiyar Lahadi ne ambaliyar ruwa ta mamaye wasu kauyukan masarautar Argungu da ke jihar Kebbi, inda ta lalata gidaje fiye da 200 a masarautar.

 

Dangane da wannan iftila’in, Shugaban Hukumar ba da agajin gaggawa ta Jihar Kebbi (SEMA), Barista Bello Yakubu (Rilisco) ne ya jagoranci tawagar manyan jami’an gwamnati da suka hada da Mataimakin Gwamnan Jihar domin kai ziyara kauyukan da abin ya shafa tare da bayar da agajin gaggawa.

  • Gwamnan Filato Ya Ƙaƙaba Dokar Hana Fita Ta Awa 24
  • Tuntuni Muka Yi Gargaɗin Cewa, Zanga-zanga Za Ta Iya Zama Hargitsi – Minista Idris

Rilisco da tawagarsa sun ziyarci garuruwan Bayawa, Tiggi, Fakon Sarki, da unguwar Kara da ke cikin garin Argungu, inda suka tantance barnar da ambaliyar ruwan saman ta yi tare da raba kayayyakin agaji ga mutanen da abin ya shafa. Kayayyakin da aka bayar sun hada da kayan abinci irin su Shinkafa, Wake, Gero, Masara, da kuma abubuwan da ba na abinci ba kamar su man gyada, gidan sauro, sabulu, robobi, katifu, da barguna.

 

Labarai Masu Nasaba

Sojoji Sun Tarwatsa Wata Haramtacciyar Masana’antar Ƙera Makamai A Filato

Ci Gaban Tattalin Arzikin Sin Na Taimaka Ga Bunkasa Al’adunta Da Mu’amalar Al’adu Tsakaninta Da Kasashen Duniya

Haka Kuma, Barista Yakubu ya jajanta wa wadanda abin ya shafa tare da tabbatar musu da kudirin gwamnatin jihar na bayar da tallafi a wannan mawuyacin lokaci. Ya kuma bukaci mazauna yankin da abin ya shafa da su kwantar da hankalinsu, inda ya yi alkawarin cewa, gwamnati za ta yi duk mai yiwuwa don ganin an dakile illar ambaliyar a yankunan nasu,

SEMASEMA

Mataimakin gwamnan wanda ya raka shugaban SEMA, ya kuma jajanta wa wadanda abin ya shafa, ya kuma yaba da kokarin hukumar bada agajin gaggawa na daukar matakan shawo kan bala’in. Ya kuma tabbatar wa mazauna yankin cewa gwamnatin jihar za ta hada gwiwa da hukumomin tarayya domin bayar da karin tallafi da taimako.

 

An raba kayan tallafin ga kauyukan da abin ya shafa, inda kowane kauye ya samu kaso mai kyau na kayayyakin da aka bayar. Mazauna yankin da suka yi ta kokawa kan yadda ambaliyar ruwan ta afku, sun nuna godiya ga gwamnatin jihar da kuma hukumar SEMA bisa daukar matakin a kan lokaci.

SEMA

Ziyarar da gudunmawar kayan agajin da Shugaban Hukumar SEMA da tawagarsa suka kai, ya sanya wa mutanen da abin ya shafa fatan alheri, inda a yanzu suka fara sake gina rayuwarsu bayan da aka yi mummunar barnar ta ambaliyar.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Ambaliyar RuwaAmurkaNijeriya
ShareTweetSendShare
Previous Post

Tuntuni Muka Yi Gargaɗin Cewa, Zanga-zanga Za Ta Iya Zama Hargitsi – Minista Idris

Next Post

Tsadar Rayuwa: Yadda ‘Yan Daba Suka Tarwatsa Masu Zanga-zanga A Legas 

Related

An Damke Basarake Da Wasu Mutum 10 Bisa Zargin Hada Baki Da ‘Yan Bindiga A Kudancin Kaduna
Manyan Labarai

Sojoji Sun Tarwatsa Wata Haramtacciyar Masana’antar Ƙera Makamai A Filato

2 hours ago
Ci Gaban Tattalin Arzikin Sin Na Taimaka Ga Bunkasa Al’adunta Da Mu’amalar Al’adu Tsakaninta Da Kasashen Duniya
Ra'ayi Riga

Ci Gaban Tattalin Arzikin Sin Na Taimaka Ga Bunkasa Al’adunta Da Mu’amalar Al’adu Tsakaninta Da Kasashen Duniya

2 hours ago
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba
Labarai

’Yansanda Sun Kama Sojan Gona Da Motocin Sata 3 A Jigawa

5 hours ago
Yadda Muka Zama Bayin ‘Yan Bindiga -Mazaunin Wani Kauye
Labarai

’Yan Bindiga Sun Sako Ma’aurata A Katsina Bayan Karɓar N50m A Matsayin Kuɗin Fansa

7 hours ago
Yadda Ribas Ta Yi Cikar Ƙwari Yayin Da Gwamna Fubara Ya Koma Ofis
Manyan Labarai

Yadda Ribas Ta Yi Cikar Ƙwari Yayin Da Gwamna Fubara Ya Koma Ofis

8 hours ago
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku
Manyan Labarai

Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

9 hours ago
Next Post
Tsadar Rayuwa: Yadda ‘Yan Daba Suka Tarwatsa Masu Zanga-zanga A Legas 

Tsadar Rayuwa: Yadda 'Yan Daba Suka Tarwatsa Masu Zanga-zanga A Legas 

LABARAI MASU NASABA

Shugaban Guinea-Bissau Ya Goyi Bayan Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya Da Sin Ta Gabatar

Shugaban Guinea-Bissau Ya Goyi Bayan Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya Da Sin Ta Gabatar

September 18, 2025
An Damke Basarake Da Wasu Mutum 10 Bisa Zargin Hada Baki Da ‘Yan Bindiga A Kudancin Kaduna

Sojoji Sun Tarwatsa Wata Haramtacciyar Masana’antar Ƙera Makamai A Filato

September 18, 2025
Ci Gaban Tattalin Arzikin Sin Na Taimaka Ga Bunkasa Al’adunta Da Mu’amalar Al’adu Tsakaninta Da Kasashen Duniya

Ci Gaban Tattalin Arzikin Sin Na Taimaka Ga Bunkasa Al’adunta Da Mu’amalar Al’adu Tsakaninta Da Kasashen Duniya

September 18, 2025
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Kama Sojan Gona Da Motocin Sata 3 A Jigawa

September 18, 2025
Yadda Muka Zama Bayin ‘Yan Bindiga -Mazaunin Wani Kauye

’Yan Bindiga Sun Sako Ma’aurata A Katsina Bayan Karɓar N50m A Matsayin Kuɗin Fansa

September 18, 2025
Yadda Ribas Ta Yi Cikar Ƙwari Yayin Da Gwamna Fubara Ya Koma Ofis

Yadda Ribas Ta Yi Cikar Ƙwari Yayin Da Gwamna Fubara Ya Koma Ofis

September 18, 2025
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

September 18, 2025
’Yansanda Sun Kama Mutane 9 Kan Yin Ƙaryar Sace Su A Jihar Neja

’Yansanda Sun Kama Mutane 9 Kan Yin Ƙaryar Sace Su A Jihar Neja

September 18, 2025
Sojoji Sun Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindiga, Sun Kashe Shugaban IPOB

Sojoji Sun Cafke Babban Kwamandan IPOB

September 18, 2025
Ya Kamata A Kiyaye Nasarorin Da Aka Cimma A Shawarwarin Sin Da Amurka 

Ya Kamata A Kiyaye Nasarorin Da Aka Cimma A Shawarwarin Sin Da Amurka 

September 17, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.