• English
  • Business News
Wednesday, October 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Aljanu Suka Shiga Zanga-zangar Da Aka Yi A Kano – Dakta Kachako  

by Mustapha Ibrahim
1 year ago
Zanga-zangar

Masanin harkar aljanu da ruhainai kuma tsohon mataimakin kwamadan Hukumar Hisbah ta Jihar Kano, Dakta Maigida Kachako ya bayyana cewa har da aljanu sun shiga zanga-zangar kuncin rayuwa da ya gudana a Jihar Kano.                  

Masanin harkar aljanun ya bayyana hakan ne a zantawarsa da manema labarai Jihar Kano a wanan makon.

  • Firaministan Pakistan: Bunkasuwar Sin Ya Zama Abin Misali Ga Kasar 
  • Gwamnatin Tarayya Za Ta Samar Da Ayyukan Yi Miliyan Ɗaya – Ɗan’agundi

Dakta Kachako ya ce su ma aljanu matsin rayuwar ta shafe su, domin daga cikin manyan abincin aljajanu akwai kashin da mutane suka yi tsotsa suka yar, wanda shi ma kashin ya yi karanci sakamakon matsin rayuwa a Nijeriya, inda hakan ya tillasta wa aljanu shiga sahun mutane wajen gudanar da zanga-zangar a Jihar Kano.

Ko da aka tambayi Dr Kachako, ta wacce hanya ya yi magana da aljanun har ya san za su shiga zanga-zangar, ya ce, sun yi magana da aljanin da ya fada masa hakan ne yayin da yake wa wata mara lafiya rukiya inda aljanin ya tabbatar masa da cewa su ma za su shiga zanga-zangar.

“Kuma tun da na yi rukiyar aljanin ya fita ya bar ta, ka ga ba sai na dawo da shi ba don ya ba ni labarin yadda suka shiga zanga-zangar. Ni ba labarin shigarsu zanga-zangar ya dame ni ba illa samun lafiyar wanda na yi wa rukiyar. Amma dai (aljanin) ya gaya mun cewa za su shiga zanga-zangar kuma na ce masa to su ji tsoron Allah.

LABARAI MASU NASABA

JIBWIS Ta Miƙa Takardar Koke Ga Gwamnatin Kaduna Kan Zargin Wasu Malamai Da Yunƙurin Tada Husuma

Zamfara Ta Fara Sauyawa Zuwa Jihar Fasahar Zamani, In ji Gwamna Lawal

“Lokacin da nake tambayarsa me ya sa ya shiga jikinta ya sa mata ciwon kai da sauransu, sai ya ce shi yanzu ma zai bar jikinta domin za su je su shiga zanga-zangar. Na ce masa kun shirya? Ya ce e, na ce kuna da yawa? Ya ce e, sai na ce masa to muna muku nasiha ku ji tsoron Allah, ka ji yadda abin yake.”

Har ila yau, Dr Kachako ya kara da cewa, bisa yadda zanga-zangar ta kasance da cincirindon jama’a da yadda akayi ta’adi na rashin hankali ya nuna akwai nau’in aljanu daban-daban da su ka shiga cikinta. Yana mai bayyana cewa duk wanda ya san tarihin Musulunci ya san aljanu sun shiga yaki na taimakon addini a zamanin magabata.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

JIBWIS Ta Miƙa Takardar Koke Ga Gwamnatin Kaduna Kan Zargin Wasu Malamai Da Yunƙurin Tada Husuma
Labarai

JIBWIS Ta Miƙa Takardar Koke Ga Gwamnatin Kaduna Kan Zargin Wasu Malamai Da Yunƙurin Tada Husuma

October 28, 2025
Zamfara Ta Fara Sauyawa Zuwa Jihar Fasahar Zamani, In ji Gwamna Lawal
Labarai

Zamfara Ta Fara Sauyawa Zuwa Jihar Fasahar Zamani, In ji Gwamna Lawal

October 28, 2025
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Ajali Tare Da Jikkata Wasu A Gombe
Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Ajali Tare Da Jikkata Wasu A Gombe

October 28, 2025
Next Post
Lallai A Hukunta Waɗanda Suka Kai Mamaya Ofishin NLC – TUC

Lallai A Hukunta Waɗanda Suka Kai Mamaya Ofishin NLC - TUC

LABARAI MASU NASABA

Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Kara Bude Kofa Da Karfafa Daidaita Dabarun Samar Da Ci Gaba

Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Kara Bude Kofa Da Karfafa Daidaita Dabarun Samar Da Ci Gaba

October 28, 2025
JIBWIS Ta Miƙa Takardar Koke Ga Gwamnatin Kaduna Kan Zargin Wasu Malamai Da Yunƙurin Tada Husuma

JIBWIS Ta Miƙa Takardar Koke Ga Gwamnatin Kaduna Kan Zargin Wasu Malamai Da Yunƙurin Tada Husuma

October 28, 2025
An Gudanar Da Taron Musamman Na Tattaunawa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa A Afrika Da Kudu

An Gudanar Da Taron Musamman Na Tattaunawa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa A Afrika Da Kudu

October 28, 2025
Zamfara Ta Fara Sauyawa Zuwa Jihar Fasahar Zamani, In ji Gwamna Lawal

Zamfara Ta Fara Sauyawa Zuwa Jihar Fasahar Zamani, In ji Gwamna Lawal

October 28, 2025
Masanan Kasar Sin Da Afirka Sun Hada Karfi Da Karfe Don Habaka Samun Wadatar Abinci Da Zamanantar Da Aikin Gona

Masanan Kasar Sin Da Afirka Sun Hada Karfi Da Karfe Don Habaka Samun Wadatar Abinci Da Zamanantar Da Aikin Gona

October 28, 2025
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Ajali Tare Da Jikkata Wasu A Gombe

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Ajali Tare Da Jikkata Wasu A Gombe

October 28, 2025
Kuri’un Jin Ra’ayin Jama’a Na CGTN Sun Nuna Gamsuwar Jama’a Ga Tsarin Jagoranci Na Sin

Kuri’un Jin Ra’ayin Jama’a Na CGTN Sun Nuna Gamsuwar Jama’a Ga Tsarin Jagoranci Na Sin

October 28, 2025
Kano Ta Bai Wa Mata 5,200 Tallafin Naira Miliyan 260

Kano Ta Bai Wa Mata 5,200 Tallafin Naira Miliyan 260

October 28, 2025
An Kusa Kammala Shirye-shiryen Baje Kolin CIIE Karo Na Takwas

An Kusa Kammala Shirye-shiryen Baje Kolin CIIE Karo Na Takwas

October 28, 2025
Gwamna Bago Ya Amince Da Biyan Karin Albashin Naira 20,000 Ga Ma’aikata 

Gwamnatin Neja Ta Bayar Da Hutun Kwanaki 2 Don Zaɓen Ƙananan Hukumomi

October 28, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.