• English
  • Business News
Friday, August 22, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Trump Ya Sha Alwashin Fatattakar Baki Daga Amurka Idan Aka Sake Zaben Sa

by Sulaiman and Rabi'u Ali Indabawa
1 year ago
in Labarai
0
trump
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Donald Trump ya kara jaddada matsayarsa a kan kwararar baki cikin Amurka, inda ya sha alwashin aiwatar da manufarsa ta fatattakar baki ”mafi girma a tarihi”, idan ya sake zama shugaban kasa.

 

A hirar da ya yi kai tsaye da shugaban shafin sada zumunta na D, Elon Musk, Mr Trump ya yi karin haske kan matsayar sa game da baki masu shiga Amurka ba bisa ka’ida ba, da kuma yunkurin kashe shi da aka yi.

  • Shugaban Seychelles: Raya Shawarar “Ziri Daya Da Hanya Daya” Na Da Makoma Mai Haske
  • Nazari Kan Dabarun Koyarwa Da Amfaninsu

An dan samu tsaiko kafin fara tattaunawar da dinbin jama’a suka yi ta jira domin sauraro a shafin X.

 

Labarai Masu Nasaba

An Ceto Mutane 41, 4 Sun Rasu A Hatsarin Kwale-Kwale A Sakkwato

An San Masu Ɗaukar Nauyin Boko Haram, Kariya Ake Ba Su – Tsohon Babban Soja

Shi dai Mr Elon Musk ya alakanta jinkirin da aka samu ne da yunkurin yin kutse da ya ce wasu sun rika yi cikin shafin, a daidai lokacin da ake shirin fara tattaunawar.

 

Dan takarar shugabancin Amurkan a jam’iyyar Republican, ya shaidawa hamshakin attajirin cewa ba zai yi wata-wata ba, wajen zartar da korar baki mafi girma a tarihi, idan har ya lashe zaben shugaban kasa a watan Nuwamba mai zuwa.

 

Mr Trump ya ce ba gudu babu ja da baya a shirin sa na gina katangar da za ta zamo shinge domin kare kasarsa daga kwararar bakin da za su zame mata barazana.

 

Ya ce: “Aikata laifi ya ragu a duniya baki daya, kuma ka jira tukun sai ka ga alkalumman da muke da su.

 

Wannan babban laifi ne, shiga kasa ba bisa ka’ida ba. Ya kara da cewa ”Mutane ne abin tsoro. Mutane ne da aka tura gidan yari saboda aikata kisan kai da sauran manyan laifuka, kuma sun zo suna turo mana su cikin kasarmu, suna kuma gargadin su cewa idan har suka koma za a kashe su.

 

Ko dai za a yanke masu hukuncin kisa ko kuma a kashe su nan take, idan har suka koma kasashen nasu. Wadan nan fa masu laifi ne da tsananin laifinsu ya sa muke kallon namu masu laifin kamar ba masu laifi ba, abin da suke aikatawa ya yi muni sosai.’’

 

An dai yi wannan tattaunawa ce bayan abokiyar hamayyar Donald Trump, Kamala Harris, ta shige gabansa a kuri’ar jin ra’ayin jama’a.

 

Mr Musk ya fito fili ya bayyana goyon bayansa ga Mr Trump ne bayan an yi yunkurin kashe tsohon shugaban Amurkan a wajen yakin neman zabe a watan jiya.

 

A ranar Litinin Donald Trump ya koma amfani da shafin D, a karon farko cikin kusan shekara guda, kuma ya wallafa sakonni bidiyo na neman zabensa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Alakar Nijeriya da TuraiAmurkaEU
ShareTweetSendShare
Previous Post

Dasuki Ya Kaddamar Da Shirin Tallafa Wa Masu Kananan Sana’o’i Da Manoma

Next Post

Mutum 68 Sun Mutu Sakamakon Ambaliyar Ruwa A Sudan

Related

An Ceto Mutane 41, 4 Sun Rasu A Hatsarin Kwale-Kwale A Sakkwato
Labarai

An Ceto Mutane 41, 4 Sun Rasu A Hatsarin Kwale-Kwale A Sakkwato

19 minutes ago
An San Masu Ɗaukar Nauyin Boko Haram, Kariya Ake Ba Su – Tsohon Babban Soja
Manyan Labarai

An San Masu Ɗaukar Nauyin Boko Haram, Kariya Ake Ba Su – Tsohon Babban Soja

2 hours ago
Yawaitar Haduran Kwale-kwale A Arewa: Ina Mafita?
Manyan Labarai

Yawaitar Haduran Kwale-kwale A Arewa: Ina Mafita?

5 hours ago
Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP
Manyan Labarai

Bukatar Farfado Da Cibiyoyin Bincike Don Bunkasa Kasa

6 hours ago
EFCC Na Neman Surukin Atiku Abubakar Ruwa A Jallo
Manyan Labarai

EFCC Na Neman Surukin Atiku Abubakar Ruwa A Jallo

14 hours ago
Sanata Wadada Ya Fice Daga Jam’iyyar SDP Bayan Ganawa Da Tinubu
Manyan Labarai

Sanata Wadada Ya Fice Daga Jam’iyyar SDP Bayan Ganawa Da Tinubu

18 hours ago
Next Post
Mutum 68 Sun Mutu Sakamakon Ambaliyar Ruwa A Sudan

Mutum 68 Sun Mutu Sakamakon Ambaliyar Ruwa A Sudan

LABARAI MASU NASABA

An Ceto Mutane 41, 4 Sun Rasu A Hatsarin Kwale-Kwale A Sakkwato

An Ceto Mutane 41, 4 Sun Rasu A Hatsarin Kwale-Kwale A Sakkwato

August 22, 2025
NBS Ta Bayyana Dalilin Raguwar Farashin Kaya A Nijeriya

NBS Ta Bayyana Dalilin Raguwar Farashin Kaya A Nijeriya

August 22, 2025
Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci Bunkasa Fannin Mai Da Ake Hakowa A Teku

Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci Bunkasa Fannin Mai Da Ake Hakowa A Teku

August 22, 2025
An San Masu Ɗaukar Nauyin Boko Haram, Kariya Ake Ba Su – Tsohon Babban Soja

An San Masu Ɗaukar Nauyin Boko Haram, Kariya Ake Ba Su – Tsohon Babban Soja

August 22, 2025
Dalilin Da Ya Sa Gwamnatin Jihar Kuros Ribas Ta Yi Hadaka Da Hukumar NPA

Dalilin Da Ya Sa Gwamnatin Jihar Kuros Ribas Ta Yi Hadaka Da Hukumar NPA

August 22, 2025
Yaushe Shugaban Kasa Zai Ba ‘Yan Matan Yobe Nasu Kyaututtukan

Yaushe Shugaban Kasa Zai Ba ‘Yan Matan Yobe Nasu Kyaututtukan

August 22, 2025
Yawaitar Haduran Kwale-kwale A Arewa: Ina Mafita?

Yawaitar Haduran Kwale-kwale A Arewa: Ina Mafita?

August 22, 2025
Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP

Bukatar Farfado Da Cibiyoyin Bincike Don Bunkasa Kasa

August 22, 2025
EFCC Na Neman Surukin Atiku Abubakar Ruwa A Jallo

EFCC Na Neman Surukin Atiku Abubakar Ruwa A Jallo

August 21, 2025
Cinikin Waje Na Sin Ya Karu Da Kashi 3.5% A Watanni Bakwai Na Farkon Bana

Cinikin Waje Na Sin Ya Karu Da Kashi 3.5% A Watanni Bakwai Na Farkon Bana

August 21, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.