• English
  • Business News
Sunday, July 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gbemisola Yusuf: Daga Sayar Da Ruwa A Filin Wasa Na Agege Zuwa Alkaliyar Wasa

by Abba Ibrahim Wada and Sulaiman
10 months ago
in Wasanni
0
Gbemisola Yusuf: Daga Sayar Da Ruwa A Filin Wasa Na Agege Zuwa Alkaliyar Wasa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Matashiya Gbemisola Yusuf mace ce mai hankoron jan ragamar rayuwarta da kanta domin tun tana shekara 21 da haihuwa ta fara alkalancin wasa a Nijeriya inda ta jagoranci wasanni 22 a filin wasa na Maracana da ke Legas.

 

Matakin da take kai a yanzu ba karamin abin alfahari ba ne saboda tana cikin alkalan wasa mata kalilan a Nijeriya duk da cewa an samu karuwar alkalan wasa mata a Afirka a ‘yan shekarun nan, har yanzu mata ba su da yawa a harkar alkalancin wasa a Afirka da duniya baki daya.

  • Aikin Matatar Mai Na Ya Hana Ni Sayen Arsenal A 2020 – Dangote
  • Ba Kare Bin Damo Tsakanin Man City Da Arsenal A Etihad 

Zuwa shekara ta 2023, mata 53 ne kawai ke cikin alkalan wasa na hukumar kwallon kafa ta duniya, kuma sun kunshi mataimaka alkalin wasa, da alkalan wasan kwallon dabe (Futsal), amma hakan ma an samu karuwa duk da haka idan aka kwatanta da shekarun baya.

 

Labarai Masu Nasaba

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

WAFCON 2025: Yau Nijeriya Za Ta Kece Raini Da Moroko A Wasan Ƙarshe

Afirka ta Kudu da Moroko ne suka fi yawan alkalan wasa mata da ke busa wasanni a babban mataki duk da cewa alkalan wasa mata kan fuskanci kalubale mai yawa a Nijeriya da Afirka saboda al’adu da addinai, sai dai da ma can al’adu kan hana mata shiga wasanni musamman ma kwallon kafa.

 

Gbemisola Yusuf, wadda aka haifa a yankin Agege na Jihar Legas, filin wasan da ke yankin muhimmin abu ne a rayuwarta da ma danginta domin lokacin da take yarinya, takan je filin wasan tare da mahaifiyarta suna sayar da ruwa da lemo ga ‘yanwasa, da masu koyarwa, da ma ‘yankallo kuma a wannan lokacin ne sha’awar kwallon kafa ta shiga rayuwarta.

 

Bayan ta fara a matsayin ‘yar wasa, Gbemisola ta koma akalancin wasa domin wani mai gidanta mai suna Dele Atoun, tsohon alkalin wasa kuma sakataren majalisar alkalan wasa ta Legas, kan tuna lokacin da ta fara wasa.

 

Ya ce ta gina kwarin gwiwa a ranta duk da yadda take ganin ana kai wa alkalan wasa hari, ana jifan su, amma kuma ta ga yadda suka yi nasara kuma hakan ya kara wa mata kwarin gwiwa domin nan gaba ma wasu su fito.

 

Gbemisola ta fara alkalancin wasa lokacin da take shekara 14 da haihuwa bayan ta shiga wani shiri da hukumar kwallon kafar Afirka CAFN ta shirya domin zakulowa da kuma ba da horo ga matasa a alkalancin wasa.

 

Sai dai hanyar da ta bi ba mai sauki ba ce musamman a Nijeriya, saboda cin zarafi ta hanyar kalamai da ma yadda magoya baya kan kai wa alkalan wasa da ‘yanwasan hari amma duk da haka ta jure har ta cika burinta.

 

Wani bincike da kungiyar alkalan wasa ta Nijeriya NRA ta gudanar ya nuna cewa kashi 80 cikin 100 na mutanen da suka ba da amsa sun ce sun fuskanci wani nau’i na cin zarafi a lokacin da suke alkalancin wasa.

 

Itama Gbemisola ta fuskanci irin wannan yanayin amma kuma hakan bai sanyaya mata gwiwa ba inda ta ce alkalancin wasa ne aiki mafi wahala a duniya domin za ka yanke hukunci a cikin ‘yan dakikoki, ko da kuwa ka yi daidai ko akasin haka. Muhimmiyar damar da Gbemisola ta samu ita ce, lokacin wani wasa a Legas tana ‘yar shekara 18. Alkalan wasan ba su zo ba, ‘yan mintuna kafin lokacin take wasan, sai aka nemi Gbemisola da ke taimaka wa mahaifiyarta sayar da ruwa a filin wasan ta jagoranci wasan kuma kusan ta yi komai daidai a wasan, kuma hakan ya ja hankalin mutane da yawa.

 

Daga nan ne kuma Gbemisola ta daukaka, inda har ta yi busa a gasar Firimiyar Nijeriya ta mata amma kuma kai wa wannan mataki ma na da nasa kalubalen, musamman ga mata domin hari kan alkalan wasa a Nijeriya ba sabon abu ba ne, kuma ya kan hada da zagi da ma kai hari.

 

A 2021, wasu ‘yankallo sun kori wata alkaliyar wasa yayin wani wasan hamayya, lamarin da ya jawo tir daga hukumar kwallon kafa ta Nijeriya da kuma kiraye-kirayen tsaurara tsaro yayin wasanni musamman kan mata alkalan wasa.

 

Tun daga 2023, babu wata gasa a Nijeriya da ta fara amfani da na’urar BAR mai taimaka wa alkalin wasa, kuma hakan ya sa alkalan wasan Nijeriya ba su iya busa wasanni a wasannin duniya saboda ba su iya amfani da na’urar ba.

 

Gbemisola ta ce idan har ta dage da kokari a aikinta, ba ta da wata fargaba domin kuwa ta kan yi bakin kokarinta kawai ta bar wa Allah sauran domin a alkalancin wasa ba komai za ka yi daidai ba kuma ba zaka taba farantawa kowa rai ba.

 

A rayuwar Gbemisola, filin wasa na Agege ba wuri ba ne kawai, wata alama ce ta mafarin sana’arta domin duk da cewa yanzu ta daina sayar da ruwa saboda Jami’ar Legas da take zuwa karatu, ba ta manta da wannan lokaci ba.

 

“Komai na rayuwata ya ta’allaka ne da filin wasa na Agege domin a nan na samu kwarin gwiwar shiga aikin alkalancin wasa, kuma yankin gaba dayansa ya taimaka min sosai.”

 

A lokacin da take hira da manema labarai.

Gbemisola na cikin alkalan wasan da suka busa gasar makarantu ta Afirka, inda ta shiga wasannin neman gurbi da kuma gasar kanta a Tanzania domin a cewarta, burinta ne ya cika kuma ta ji dadin yin hakan, kamar yadda ta bayyana.

 

Ta ci gaba da cewa “Zuwa kasashe da kuma tattaunawa da alkalai daban-daban, da kuma koyon harsuna abubuwa ne da suka taimaka mata domin iya magana da harsuna daban-daban kan taimaka wa alkalin wasa wajen karfafa ikonsa a cikin fili.

 

Ta kara da cewa abu ne mai muhimmanci sosai saboda ba ta taba tsammanin za ta hadu da mutanen da ta gani ba kuma shi ma mai gidanta Atou ya ce yana alfahari da nasarorinta domin labarinta mai karfafa gwiwa ne da jajircewa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 'Yar WasaFirimiyar Ingila
ShareTweetSendShare
Previous Post

Wani Matashi Ya Sace Rodin Kaburbura Don Sayen Abinci Da Wiwi

Next Post

Sojoji Sun Kashe Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda, Sun Kama Ɓarayin Shanu 22

Related

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 
Wasanni

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

9 hours ago
WAFCON 2025: Yau Nijeriya Za Ta Kece Raini Da Moroko A Wasan Ƙarshe
Wasanni

WAFCON 2025: Yau Nijeriya Za Ta Kece Raini Da Moroko A Wasan Ƙarshe

20 hours ago
Zan Ci Gaba da Taka Leda A Kano Pillars Duk da Matsayin Da Na Samu — Ahmed Musa
Wasanni

Zan Ci Gaba da Taka Leda A Kano Pillars Duk da Matsayin Da Na Samu — Ahmed Musa

4 days ago
Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Kai Wasan Ƙarshe Bayan Doke Afrika Ta Kudu
Wasanni

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Kai Wasan Ƙarshe Bayan Doke Afrika Ta Kudu

5 days ago
Oshoala Za Ta Yi Ritaya Daga Buga Wa Nijeriya Ƙwallo
Wasanni

Oshoala Za Ta Yi Ritaya Daga Buga Wa Nijeriya Ƙwallo

5 days ago
Rashford Na Dab Da Komawa Barcelona A Matsayin Aro
Wasanni

Rashford Na Dab Da Komawa Barcelona A Matsayin Aro

6 days ago
Next Post
Sojoji Sun Kashe Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda, Sun Kama Ɓarayin Shanu 22

Sojoji Sun Kashe Ƙasurgumin Ɗan Ta'adda, Sun Kama Ɓarayin Shanu 22

LABARAI MASU NASABA

Yadda Ake Faten Acca

Yadda Ake Faten Acca

July 27, 2025
Hanyoyin Gyaran Gashi

Hanyoyin Gyaran Gashi

July 27, 2025
Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

July 26, 2025
Musuluntar Wata Ce Ya Ja Hankalina Shiga Fim – Sailuba Dadin Kowa

Musuluntar Wata Ce Ya Ja Hankalina Shiga Fim – Sailuba Dadin Kowa

July 26, 2025
Masanin Kimiyyar Na’ura Mai Kwakwalwa Robert Tarjan Ya Jinjinawa Dabarun Sin Na Ingiza Ilimin Kimiyya

Masanin Kimiyyar Na’ura Mai Kwakwalwa Robert Tarjan Ya Jinjinawa Dabarun Sin Na Ingiza Ilimin Kimiyya

July 26, 2025
Kasar Sin Na Tir Da Harin Isra’ila Kan Makarantu A Gaza Tare Da Kira Da A Dakatar Da Bude Wuta

Isra’ila Na Sanya Alamar Rusau A Dubban Gidajen Fararen Hula A Gaza

July 26, 2025
Firaministan Sin Ya Halarci Taron Kasa Da Kasa Game Da Jagorancin AI

Firaministan Sin Ya Halarci Taron Kasa Da Kasa Game Da Jagorancin AI

July 26, 2025
Gbemisola

Natijojin Auren Dattijo Ga Budurwa

July 26, 2025
An Yi Bikin Karbar Fitilar Gasar Wasannin Kasa Da Kasa Ta Shekarar 2025 A Chengdu

An Yi Bikin Karbar Fitilar Gasar Wasannin Kasa Da Kasa Ta Shekarar 2025 A Chengdu

July 26, 2025
Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (6)

Dalilan Da Suka Sa Cinikin Bayi Bai Yi Nasara A Arewacin Nijeriya Ba

July 26, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.