• English
  • Business News
Sunday, September 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NIS Reshen Jihar Bayelsa Za Ta Fara Bayar Da Sabon Ingantaccen Fasfo

by yahuzajere
3 years ago
in Labarai
0
NIS Reshen Jihar Bayelsa Za Ta Fara Bayar Da Sabon Ingantaccen Fasfo
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hukumar Kula da Shige da Fice (NIS) reshen Jihar Bayelsa za ta fara bayar da sabon ingantaccen fasfo, a wani yunƙuri da hukumar ke yi na sauyawa daga tsohon yayi na fasfon zuwa sabon da aka samar.

Shi dai sabon fasfon yana ƙumshe da abubuwa na tsaro sama da 25, kana an tsara shi a bisa ingancin da duniya ta amince da shi wanda sannu a hankali zai maye gurbin tsohon samfurin fasfon da ake bayarwa.

  • Yadda Aka Ƙaddamar Da Ƙungiyar SURE 4U Domin Jin Ƙan Marasa Galihu

Sanarwar da ta fito daga Jami’in hulɗa da jama’a na hukumar a Bayelsa, ta shawarci masu neman fasfo a yankin jihar su bi ƙa’idar da hukumar ta sa wajen gabatar da buƙatarsu ta hanyar amfani da sadarwar intanet a dukkan matakan da ake bi tun daga cike takardar nema zuwa biyan kuɗi da ɗaukar hoto da sanin ranar karɓa wanda hakan zai hana mai nema faɗawa hannun bara-gurbi masu tatsar kuɗi.

Ita dai NIS ta duƙufa wajen ganin mutane suna samun fasfo ba tare da katsalandan daga wani ba. Ministan Cikin Gida Rauf Aregbesola tare da Kwanturola Janar na NIS Isah Jere Idris za su ƙaddamar da babbar cibiyar fasfon a Jihar Ribas wadda za ta karaɗe ofisoshin fasfo na Jihohin Akwa-Ibom, Bayelsa, da Kuros Ribas.

Sabon ingantaccen fasfon dai yana da tsare-tsare na musamman da aka kasafta zuwa matakai guda uku. Akwai mai shafi 32 da yake aiki na tsawon shekara 5, sai mai shafi 64 da yake aiki na tsawon shekara 5 da kuma mai shafi 64 da yake aiki na tsawon shekara 10.
Hanya mafi sauƙi da mutum zai bi ya nemi fasfon ita ce ya shiga adireshin intanet na: passport.immigration.gov.ng, yana shiga zai ga fom sai ya cike tare da biyan kuɗi, duka dai ta intanet. Daga nan sai ya sauke takardar shaidar biyan kuɗi da ta lokacin da aka ba shi na zuwa ɗaukar hoto tare da wallafawa.

Labarai Masu Nasaba

DAPPMAN Ta Soki Matatar Dangote Kan Rage Farashin Man Fetur

Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro

Mutum zai ziyarci ofishin fasfo ne kawai a ranar da aka ce ya je, sai ya tafi da abubuwan da aka ce ya tanada ciki har da takardar shaidar biyan kuɗinsa.

 

Wajibi ne dai ga kowane mai neman fasfo ya yi amfani da lambarsa ta shaidar ɗan ƙasa wajen neman fasfo. Wa’adin samun fasfo ga sabbin shiga shi ne mako shida, yayin da na waɗanda za su sabunta kuma bai wuce mako uku ba.

  • https://m.facebook.com/LeadershipNGA/photos/a.251250111575686/4899099793457338/

Domin ƙarin bayani ana iya kiran wannan lambar: 08021819988 ko a ziyarci adireshin NIS na intanet ta: www.immigration.gov.ng


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Manufar Rungumar Makomar Dan Adam Ta Bai Daya Ta Nuna Inda Duniyarmu Za Ta Dosa

Next Post

Bisa Aiki Tukuru Sin Ta Samu Karbuwa A Kasashen Afirka

Related

Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12
Manyan Labarai

DAPPMAN Ta Soki Matatar Dangote Kan Rage Farashin Man Fetur

6 hours ago
Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro
Tsaro

Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro

8 hours ago
An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu
Labarai

An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu

9 hours ago
An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta
Manyan Labarai

An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta

10 hours ago
Etsu Nupe Ginshiƙin Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ne A Nijeriya — Ministan Yaɗa Labarai
Labarai

Etsu Nupe Ginshiƙin Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ne A Nijeriya — Ministan Yaɗa Labarai

13 hours ago
Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro
Tsaro

Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro

14 hours ago
Next Post
Bisa Aiki Tukuru Sin Ta Samu Karbuwa A Kasashen Afirka

Bisa Aiki Tukuru Sin Ta Samu Karbuwa A Kasashen Afirka

LABARAI MASU NASABA

Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12

DAPPMAN Ta Soki Matatar Dangote Kan Rage Farashin Man Fetur

September 13, 2025
Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro

Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro

September 13, 2025
Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya

Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya

September 13, 2025
An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu

An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu

September 13, 2025
An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu

An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu

September 13, 2025
An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta

An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta

September 13, 2025
Kasar Sin Za Ta Kare Hakkin Kamfanoninta Ciki Har Da Tiktok

Kasar Sin Za Ta Kare Hakkin Kamfanoninta Ciki Har Da Tiktok

September 13, 2025
Aleksandar Vucic: Serbia Na Goyon Bayan Shawarar Kula Da Harkokin Duniya Da Kasar Sin Ta Gabatar

Aleksandar Vucic: Serbia Na Goyon Bayan Shawarar Kula Da Harkokin Duniya Da Kasar Sin Ta Gabatar

September 13, 2025
Etsu Nupe Ginshiƙin Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ne A Nijeriya — Ministan Yaɗa Labarai

Etsu Nupe Ginshiƙin Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ne A Nijeriya — Ministan Yaɗa Labarai

September 13, 2025
Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro

Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro

September 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.