• English
  • Business News
Thursday, July 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yajin Aikin ASUU: Kungiyar Dalubai Ta Bukaci A Kori Ministan Ilimi

by Abubakar Abba
3 years ago
in Labarai
0
Yajin Aikin ASUU: Kungiyar Dalubai Ta Bukaci A Kori Ministan Ilimi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Biyo bayan wa’adin da aka bai wa Ministan Ilimi, Malam Adamu Adamu na lalubo mafita kan yajin aikin ASSU, Kungiyar Dalibai ta Kasa (NANS), ta yi kira da a sauke ministan daga kan mukaminsa.  

In ba a manta ba shugaba Muhammadu Buhari a ranar 19 ga watan Julin 2022, ya bai wa Adamu wa’adin sati biyu da ya kawo karshen yajin aikin aikin da ASUU ke yi domin daliban da ke karatu a jami’oi su koma bakin karatunsu.

  • 2023: Fintiri Ya Zabi Mace A Matsayin Abokiyar Takararsa
  • Kwamishinan Yobe, Goni Bukar, Ya Rasu A Hadarin Mota

Sai dai, wannan wa’adin na sati biyun ya kare ba tare da samar da wani daidaito ba, inda hakan ya janyo ASUU ta kara tsawaita yajin aikinta da sati hudu.

Da yake mayar da martani kan lamarin shugaban NANS, Kwamared Sunday Asefon, a cikin sanarwar da ya bai wa LEADERSHIP, a yau Laraba, alamu sun nuna cewa, Adamu bai da wani kwarin gwiwa wajen tafiyar da ma’aikatarsa.

Asefon, ya ci gaba da cewa, “A bisa wannan dalilin ne, muke yin tambaya kan wacce irin kwarewa ce Adamu yake da ita da har aka nada shi a mukamin Ministan Ilimi domin bai da wata tausaya wa kan abin da ya shafi matsalar daliban.

Labarai Masu Nasaba

Sojoji Sun Kama Jami’an NURTW 2, Da Mai Karɓar Harajin IPOB

Babu Wata Sabuwar Ƙungiyar  Ƴan Ta’adda Mai Suna Fethulla A Nijeriya – DHQ

“Tun lokacin da aka nada Adamu mukamin minista, ASUU ta shiga yajin aiki na kusan watanni 18 haka fannin ilimin manyan makarantun kasar ya tabarbare.

“Ya zama wajibi mu yi kira ga shugaba Buhari da ya gaggauta sauke Adamu daga kan mukaminsa na Ministan Ilimi ya maye gurbinsa da kwararren da ya dace.”

Ya ce, ba za su yi kasa a gwiwa ba wajen ganin an amince da wannan bukatar tasu ta sauke Adamu daga kan mukamin nasa, inda suka a sanar da cewa, dole ne Adamu ya sauka.

A karshe dhugaban ya ce, ya zama wajbi masu kishin kasar nan su matsa wa gwamnatin tarayya lamba don a sauke Adamu daga kan mukaminsa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BuhariKungiyar DalibaiMalam Adamu AdamuMinistan IlimiNANSYajin Aikin ASUU
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kasa Da Kasa Sun Fahimci Ainihin Manufar Ziyarar Pelosy A Taiwan

Next Post

Matsalar Tsaro: Majalisa Ta Gana Da Shugabannin Hukumomin Tsaro

Related

Sojoji Sun Kama Jami’an NURTW 2, Da Mai Karɓar Harajin IPOB
Labarai

Sojoji Sun Kama Jami’an NURTW 2, Da Mai Karɓar Harajin IPOB

33 minutes ago
Babu Wata Sabuwar Ƙungiyar  Ƴan Ta’adda Mai Suna Fethulla A Nijeriya – DHQ
Tsaro

Babu Wata Sabuwar Ƙungiyar  Ƴan Ta’adda Mai Suna Fethulla A Nijeriya – DHQ

2 hours ago
Manufar Raya Biranen Kasar Sin: Ba Wai Kawai a Tabbatar Da “Tsayi” Ba Ne Har Ma Da “Zafi”
Ra'ayi Riga

Manufar Raya Biranen Kasar Sin: Ba Wai Kawai a Tabbatar Da “Tsayi” Ba Ne Har Ma Da “Zafi”

3 hours ago
Sojoji Sun Ƙi Karɓar Cin Hancin Miliyan 13 Daga Ƴan Ta’adda A Filato
Manyan Labarai

Sojoji Sun Ƙi Karɓar Cin Hancin Miliyan 13 Daga Ƴan Ta’adda A Filato

4 hours ago
Kano Pillars Ta Ƙulla Yarjejeniya Da Gidan Rediyon RFI Hausa
Labarai

Kano Pillars Ta Ƙulla Yarjejeniya Da Gidan Rediyon RFI Hausa

6 hours ago
Dele Momodu Ya Fice Daga Jam’iyyar PDP Zuwa ADC
Manyan Labarai

Dele Momodu Ya Fice Daga Jam’iyyar PDP Zuwa ADC

8 hours ago
Next Post
Matsalar Tsaro: Majalisa Ta Gana Da Shugabannin Hukumomin Tsaro

Matsalar Tsaro: Majalisa Ta Gana Da Shugabannin Hukumomin Tsaro

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kama Jami’an NURTW 2, Da Mai Karɓar Harajin IPOB

Sojoji Sun Kama Jami’an NURTW 2, Da Mai Karɓar Harajin IPOB

July 17, 2025
Roy Jakobs: Ba Za A Iya Rabuwa Da Tsarin Samar Da Kayayyaki Na Sin Ba

Roy Jakobs: Ba Za A Iya Rabuwa Da Tsarin Samar Da Kayayyaki Na Sin Ba

July 17, 2025
Babu Wata Sabuwar Ƙungiyar  Ƴan Ta’adda Mai Suna Fethulla A Nijeriya – DHQ

Babu Wata Sabuwar Ƙungiyar  Ƴan Ta’adda Mai Suna Fethulla A Nijeriya – DHQ

July 17, 2025
Mataimakin Shugaban Kasar Sin Ya Gana Da Takwaransa Na Kasar Afirka Ta Kudu

Mataimakin Shugaban Kasar Sin Ya Gana Da Takwaransa Na Kasar Afirka Ta Kudu

July 17, 2025
Ƴansanda Sun Kama Ɗalibai 11 Kan Kisan Wasu Ɗalibai 2 A Kano

Ƴansanda Sun Kama Ɗalibai 11 Kan Kisan Wasu Ɗalibai 2 A Kano

July 17, 2025
Manufar Raya Biranen Kasar Sin: Ba Wai Kawai a Tabbatar Da “Tsayi” Ba Ne Har Ma Da “Zafi”

Manufar Raya Biranen Kasar Sin: Ba Wai Kawai a Tabbatar Da “Tsayi” Ba Ne Har Ma Da “Zafi”

July 17, 2025
Sojoji Sun Ƙi Karɓar Cin Hancin Miliyan 13 Daga Ƴan Ta’adda A Filato

Sojoji Sun Ƙi Karɓar Cin Hancin Miliyan 13 Daga Ƴan Ta’adda A Filato

July 17, 2025
Kano Pillars Ta Ƙulla Yarjejeniya Da Gidan Rediyon RFI Hausa

Kano Pillars Ta Ƙulla Yarjejeniya Da Gidan Rediyon RFI Hausa

July 17, 2025
Dele Momodu Ya Fice Daga Jam’iyyar PDP Zuwa ADC

Dele Momodu Ya Fice Daga Jam’iyyar PDP Zuwa ADC

July 17, 2025
Gwamna Lawal Ya Bai Wa Dalibai Sama Da 8,000 Tallafi A Zamfara

Gwamna Lawal Ya Bai Wa Dalibai Sama Da 8,000 Tallafi A Zamfara

July 17, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.