ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, November 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnan Zamfara Ya Yi Gargaɗi Kan Yanke Wa Ma’aikata Kuɗi Ba Bisa Ƙa’ida Ba

by Leadership Hausa and Sulaiman
1 year ago
Zamfara

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umurnin dakatar da duk wani nau’in cirar kuɗi ba bisa ƙa’ida ba daga albashin ma’aikatan jihar.

 

Wannan ya biyo bayan da Ma’aikatan Zamfara suk koka tare da ƙorafe-ƙorafe da dama dangane cire-ciren kuɗi da ake yi musu a tsarin biyan albashin jihar.

ADVERTISEMENT
  • Uwargidan Shugaban Ƙasa Ta Ƙaddamar Da Atamfar Haɗin Kan Ƙasa Da Tallafin Littafi 50,000 A Zamfara 
  • Kotu Ta Hana CBN Da Sauransu Yi Wa Kudaden Kananan Hukumomi Katsa-Landan

A wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan jihar, Sulaiman Bala Idris ya fitar a Gusau, ya bayyana cewa umurnin da aka bayar ya haramta duk wani nau’in cirar kuɗi ba bisa ƙa’ida ba da ake yi ta hanyar biyan albashin gwamnatin Jihar Zamfara.

 

LABARAI MASU NASABA

Laftanal Yarima Ya Tsallake Rijiya Da Baya A Abuja

Falana Ya Shawarci Waɗanda Suka Biya Kuɗin Fansa Su Kai Gwamnati Kotu Don Ta Biya Su

Sanarwar ta ci gaba da cewa, “A cikin ƙudirinsa na tsaftace tsarin biyan albashin ma’aikatan jihar Zamfara don samun ingantaccen tsarin biyan albashin su a adaidai lokacin da suke fuskantar cire-ciren kuɗi ba bisa ƙa’ida ba, Gwamna Dauda Lawal ya bayar da umarnin dakatar da duk wasu bangarori da ba sa bin doka da oda wajen zaftare wani sashi daga albashin ma’aikata.

 

“An yanke hukuncin ne saboda ƙorafe-ƙorafen da ake yi na cire-ciren kuɗi daga albashin ma’aikata, inda ake zaftare wasu kuɗaɗen da sunan wasu ƙungiyoyin haɗin gwiwa na ‘Cooperatives’, wasu kuma da sunan biyan wasu basukan kayayyaki.

 

“Gwamna Lawal ya umurci kwamishinan kuɗi da ya dakatar da duk irin wannan cire-cire daga albashin ma’aikata tare da isar da umarnin ga duk ƙungiyoyin haɗin gwiwa da sauran masu sayar da kayayyaki.

 

“Don ƙarin haske, bangarorin da aka yarda kaɗai su cire kuɗi su ne: PAYE; Kuɗin ƙungiya; NHF; ZAMCHEMA; kuɗin amfani da ruwa; FMB (Hayar Gida kafin Mallaka); FMB (Gyarar Gida); Kuɗin hannun jari.

 

“Gwamnatin da ke yanzu a jihar Zamfara ta himmatu wajen aiwatar da matakan da za su taimaka wa walwala da ci gaban ma’aikatan ta. Wannan ya haɗa da haɓaka yanayin aiki, samar da albarkatun da suka dace, da kuma samar da yanayi mai kyau don tabbatar da ƙwararewar ma’aikata wajen gudanar da ayyukan su.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Laftanal Yarima Ya Tsallake Rijiya Da Baya A Abuja
Manyan Labarai

Laftanal Yarima Ya Tsallake Rijiya Da Baya A Abuja

November 16, 2025
Falana Ya Shawarci Waɗanda Suka Biya Kuɗin Fansa Su Kai Gwamnati Kotu Don Ta Biya Su
Manyan Labarai

Falana Ya Shawarci Waɗanda Suka Biya Kuɗin Fansa Su Kai Gwamnati Kotu Don Ta Biya Su

November 16, 2025
Ƴan Bindiga Sun Sace Mutane 14 A Wani Sabon Hari A Zamfara
Manyan Labarai

Ƴan Bindiga Sun Sace Mutane 14 A Wani Sabon Hari A Zamfara

November 16, 2025
Next Post
Amurka

Nijeriya Za Ta Kara Haɓaka Alaƙarta Da Sabon Zaɓaɓɓen Shugaban Amurka – Gwamnati

LABARAI MASU NASABA

Laftanal Yarima Ya Tsallake Rijiya Da Baya A Abuja

Laftanal Yarima Ya Tsallake Rijiya Da Baya A Abuja

November 16, 2025
Falana Ya Shawarci Waɗanda Suka Biya Kuɗin Fansa Su Kai Gwamnati Kotu Don Ta Biya Su

Falana Ya Shawarci Waɗanda Suka Biya Kuɗin Fansa Su Kai Gwamnati Kotu Don Ta Biya Su

November 16, 2025
Fasinjojin Da Kasar Sin Ta Yi Jigilarsu Ta Jirgin Kasa Daga Janairu Zuwa Oktoba Sun Kai Biliyan 3.95

Fasinjojin Da Kasar Sin Ta Yi Jigilarsu Ta Jirgin Kasa Daga Janairu Zuwa Oktoba Sun Kai Biliyan 3.95

November 16, 2025
Ƴan Bindiga Sun Sace Mutane 14 A Wani Sabon Hari A Zamfara

Ƴan Bindiga Sun Sace Mutane 14 A Wani Sabon Hari A Zamfara

November 16, 2025
Babban Jirgin Ruwan Yaki Samfurin 076 Na Sin Ya Kammala Gwajinsa Na Farko A Teku

Babban Jirgin Ruwan Yaki Samfurin 076 Na Sin Ya Kammala Gwajinsa Na Farko A Teku

November 16, 2025
Sin Ta Gargadi Philippines A Kan Ci Gaba Da Tayar Da Zaune Tsaye A Tekun Kudancinta

Sin Ta Gargadi Philippines A Kan Ci Gaba Da Tayar Da Zaune Tsaye A Tekun Kudancinta

November 16, 2025
An Yi Taron Karatun Sinanci Na Duniya Na 2025 A Beijing

An Yi Taron Karatun Sinanci Na Duniya Na 2025 A Beijing

November 16, 2025
Ana Mai Da Hankali Kan Dabarun Kasar Sin A Fannin Tinkarar Sauyin Yanayin Duniya A Taron COP30

Ana Mai Da Hankali Kan Dabarun Kasar Sin A Fannin Tinkarar Sauyin Yanayin Duniya A Taron COP30

November 16, 2025
Wata Ƙungiya Ta Fara Bin Digdigin Takardun Karatun Matawalle

Wata Ƙungiya Ta Fara Bin Digdigin Takardun Karatun Matawalle

November 16, 2025
DSS

Hukumar DSS Ta Kama Wani Kan Zargin Ƙerawa Da Rarraba Makamai A Filato

November 16, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.