• English
  • Business News
Tuesday, July 1, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sabon Jakadan Nijar A Rasha Ya Mika Wasikar Kama Aiki Ga Shugaba Putin

by Sulaiman
8 months ago
in Labarai
0
Sabon Jakadan Nijar A Rasha Ya Mika Wasikar Kama Aiki Ga Shugaba Putin
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban Kasar Rasha Bladimir Putin ya karbi wasikar jakadanci ta sabon jakadan Nijar a kasar Rasha a fadar Kremlin dake Birnin Moscou.

 

Gwamnatin Nijar, a yayin wani zaman taron ministoci na ranar 15 ga watan Mayun shekarar 2024, ta amince da nada Janar Abdou Sidikou Issa a wannan muhimmin matsayi, wanda kuma hakan ya nuna cewa, tsohon shugaban rundunar sojojin Nijar, Janar Abdou Sidikou Issa zai wakilci bangaren diplomasiyyar Nijar a kasar Rasha.

  • EFCC Ta Gurfanar Da Tsofaffin Gwamnoni Da Tsofaffin Ministoci, Bayan Kwato Kadarorin Biliyoyin Naira A Kasashen Waje
  • Ainihin Nufin Philippines Na Kafa Abin Da Take Kira Dokar Yankunan Teku 

Inda ya mika takardar jakadancinsa ga shugaban Kasar Rasha Bladimir Putin a Nuwamban shekarar 2024.

 

Labarai Masu Nasaba

Ba Gaskiya Ba Ne: Ɓarayi Ba Su Sace Ɗan Uwan Gwamnan Zamfara Ba

Uwargidan Gwamnan Kaduna Ta Kaddamar Da Rabon Kayan Noma Ga Mata Manoma

Shi dai tsohon manjo-janar din sojojin Nijar, Abdou Sidikou Issa, sananne ne a fagen siyasar Nijar, kuma mutum ne mai son aiki, da ya taka muhimmiyar rawa a lokacin juyin mulkin ranar 23 ga watan Yulin shekarar 2023.

 

Kazalika a 2024, ministan sadarwa Sidi Mohamed Raliou ya gana da dukkan wakilan gidajen rediyo, talabijin da jaridu na kasashen waje dake aiki a Nijar, ganawar da ta gudana a ofishin ma’aikatar sadarwa dake Birnin Yamai.

 

Wannan ganawa irin ta ta farko, ta kasance wani tsarin tattaunawa, da yin musaya kan batutuwa da dama da suka shafi tsinkayen shugaban kwamitin ceton kasa da kuma daidaita matsayin wakilai da aikinsu a Nijar.

 

Ministan sadarwa ya bukaci ganin goyon bayan wakilan kafofin watsa labarai na kasashen waje dake Nijar game da hangen shugaban kwamitin ceton kasa na CNSP Abdourahamane Tiani da ya rataya kan zaman jituwa tsakanin al’ummar kasa, tsaro da kuma mulki na-gari.

 

Haka zalika, minista Sidi Mohamed Raliou ya ja hankalin wadannan ‘yan Nijar dake ma kafafen sadarwa na kasashen waje aiki a Nijar, da su kasance masu kishin kasa, da su sanya moriyar kasarsu a gaba, da kuma fifita ci gaban kasarsu.

 

A nasu bangare, mahalarta wannan ganawa sun nuna jin dadi da gamsuwarsu game da wannan tunani na ma’aikatar sadarwa bisa ga shirya wannan haduwa.

 

Haka kuma, sun yi amfani da wannan dama, domin bayyanawa minista Sidi Mohamed Raliou, matsalolin da suke fuskanta game da neman labarai daga wajen hukumomi, da kuma fatan ganin an daidaita wadannan matsaloli.

 

Daga karshe, minista Sidi Mohamed Raliou, ya tabbatarwa wadannan ‘yan jarida niyyarsa na rakiyarsu da kuma kasancewa mai saurarensu a kowane lokaci, tare da yin musanya kan batutuwan da za su taimaka musu tafiyar da aikinsu cikin sauki kuma cikin girmama ka’idodin aikin jarida.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Babbar Majalisar Dokokin Kasar Sin Ta Yi Allah Wadai Da Abin Da Ake Kira Dokar Yankunan Teku Na Philippines

Next Post

Shanghai: An Gudanar Da Taron Majalisar Tattalin Arziki Da Zamantakewar Al’ummar Sin Da Ta Afirka Karo Na 4

Related

Ba Gaskiya Ba Ne: Ɓarayi Ba Su Sace Ɗan Uwan Gwamnan Zamfara Ba
Labarai

Ba Gaskiya Ba Ne: Ɓarayi Ba Su Sace Ɗan Uwan Gwamnan Zamfara Ba

17 minutes ago
Uwargidan Gwamnan Kaduna Ta Kaddamar Da Rabon Kayan Noma Ga Mata Manoma
Labarai

Uwargidan Gwamnan Kaduna Ta Kaddamar Da Rabon Kayan Noma Ga Mata Manoma

1 hour ago
Sojoji Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Ta’adda Yellow Danbokolo A Zamfara
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Ta’adda Yellow Danbokolo A Zamfara

4 hours ago
Barau, Ganduje Da Wasu Sun Isa Madina Don Halartar Jana’izar Aminu Dantata
Manyan Labarai

Barau, Ganduje Da Wasu Sun Isa Madina Don Halartar Jana’izar Aminu Dantata

8 hours ago
Duk Da Farfadowar Darajar Naira, Tsadar Kaya Na Ci Gaba Da Lulawa Sama
Manyan Labarai

Faɗuwar Darajar Naira Ta Sa Bashin Nijeriya Ya Ƙaru Zuwa Naira Tiriliyan 149

10 hours ago
Haɗakar Jam’iyyun Adawa Ba Ya Ɗaga Mana Hankali – Sabon Shugaban APC
Manyan Labarai

Haɗakar Jam’iyyun Adawa Ba Ya Ɗaga Mana Hankali – Sabon Shugaban APC

11 hours ago
Next Post
Shanghai: An Gudanar Da Taron Majalisar Tattalin Arziki Da Zamantakewar Al’ummar Sin Da Ta Afirka Karo Na 4

Shanghai: An Gudanar Da Taron Majalisar Tattalin Arziki Da Zamantakewar Al’ummar Sin Da Ta Afirka Karo Na 4

LABARAI MASU NASABA

An Yi Bikin Kade-Kade Don Taya Murnar Cika Shekaru 104 Da Kafuwar JKS

An Yi Bikin Kade-Kade Don Taya Murnar Cika Shekaru 104 Da Kafuwar JKS

July 1, 2025
Ba Gaskiya Ba Ne: Ɓarayi Ba Su Sace Ɗan Uwan Gwamnan Zamfara Ba

Ba Gaskiya Ba Ne: Ɓarayi Ba Su Sace Ɗan Uwan Gwamnan Zamfara Ba

July 1, 2025
Uwargidan Gwamnan Kaduna Ta Kaddamar Da Rabon Kayan Noma Ga Mata Manoma

Uwargidan Gwamnan Kaduna Ta Kaddamar Da Rabon Kayan Noma Ga Mata Manoma

July 1, 2025
Sin Za Ta Gabatar Da Shagulgulan Al’adu Na Bikin Cika Shekaru 80 Da Samun Nasarar Yaki Da Zaluncin Japanawa

Sin Za Ta Gabatar Da Shagulgulan Al’adu Na Bikin Cika Shekaru 80 Da Samun Nasarar Yaki Da Zaluncin Japanawa

July 1, 2025
Xi Jinping Ya Jaddada Niyyar Gina Babbar Kasuwar Kasa Ta Bai Daya, Tare Da Raya Tattalin Arziki Na Teku Mai Inganci

Xi Jinping Ya Jaddada Niyyar Gina Babbar Kasuwar Kasa Ta Bai Daya, Tare Da Raya Tattalin Arziki Na Teku Mai Inganci

July 1, 2025
Labari Mai Daɗi: Asibitin Kwararru Mai Zaman Kansa A Kano Ya Rage Kaso 50 Na kuɗaɗen Ayyukansu 

Labari Mai Daɗi: Asibitin Kwararru Mai Zaman Kansa A Kano Ya Rage Kaso 50 Na kuɗaɗen Ayyukansu 

July 1, 2025
Sojoji Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Ta’adda Yellow Danbokolo A Zamfara

Sojoji Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Ta’adda Yellow Danbokolo A Zamfara

July 1, 2025
Manomi Ya Ceto Jaririya Da Aka Binne Da Ranta A Kebbi

Manomi Ya Ceto Jaririya Da Aka Binne Da Ranta A Kebbi

July 1, 2025
Barau, Ganduje Da Wasu Sun Isa Madina Don Halartar Jana’izar Aminu Dantata

Barau, Ganduje Da Wasu Sun Isa Madina Don Halartar Jana’izar Aminu Dantata

July 1, 2025
Duk Da Farfadowar Darajar Naira, Tsadar Kaya Na Ci Gaba Da Lulawa Sama

Faɗuwar Darajar Naira Ta Sa Bashin Nijeriya Ya Ƙaru Zuwa Naira Tiriliyan 149

July 1, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.