• English
  • Business News
Thursday, October 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Ta’aziyyar Rasuwar Babban Limamin Masallacin Minna

by Sulaiman
11 months ago
Masallacin Minna

Ministan Yaɗa Labarai Da Wayar Da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya jajanta wa al’ummar Musulmin garin Minna da Gwamnatin Jihar Neja bisa rasuwar Babban Limamin Masallacin Minna, Sheikh Isah Fari.

 

A cikin wata sanarwa da Mataimakin sa na Musamman kan Harkokin Yaɗa Labarai, Rabiu Ibrahim ya fitar, ministan ya bayyana marigayi Sheikh Fari wanda ya rasu yana da shekaru 93 a duniya a matsayin babban malamin addini wanda ya sadaukar da rayuwar sa wajen bautar Allah, yaɗa Musulunci, da kuma inganta zaman lafiya a Jihar Neja da ma ƙasar baki ɗaya.

  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Buƙaci ‘Yansanda Su Rungumi Yarjejeniyar Ɗa’a ta Ƙasa
  • ‘Yan Bindiga Sun Kone Gonakin Manoma A Zamfara

Ya ce: “Marigayi Sheikh Isah Fari ya nuna maƙasudin addinin Musulunci, wanda shi ne fifikon zaman lafiya da haɗin kai a tsakanin al’umma, ta yadda a shekarun da ya yi yana matsayin Babban Limamin Babban Masallacin Minna an ɗauke shi a matsayin wanda ke jaddada zaman lafiya da kwanciyar hankali a Jihar Neja.”

 

LABARAI MASU NASABA

Baba-Ahmed Ya Zargi El-Rufai Da APC Kan Haifar Da Rashin Tsaro Don Neman Mulki

Jami’an FRSC Sun Mayar Da N6.2m Da Suka Tsinta Bayan Aukuwar Hatsarin Mota A Katsina

Idris ya miƙa ta’aziyyar sa ga Gwamnan Jihar Neja, Alhaji Umaru Bago, da Sarkin Minna, Alhaji Dakta Umar Faruq Bahago, tare da jaddada gagarumar gudunmawar da marigayi Babban Limamin ya bayar wajen bunƙasa zamantakewa da tattalin arzikin Masarautar Minna da Jihar Neja.

 

Ya ce: “Ina miƙa alhini na ga Gwamnan Jihar Neja, Mai Girma Umaru Bago, da Sarkin Minna, Mai Martaba Sarkin Minna, Alhaji Dr Umar Faruq Bahago, bisa rashin wani masani wanda ilimin sa ya zame tushe na shawarwari masu inganci don cigaban zamantakewa da tattalin arzikin masarautar Minna da Jihar Neja baki ɗaya.”

 

Ministan ya buƙaci al’ummar Jihar Neja da su kiyaye koyarwar soyayya, haƙuri da juna da haɗin kai da Sheikh Fari ya bayar a lokacin rayuwar sa, tare da yin addu’ar Allah ya jiƙan marigayin.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Baba-Ahmed Ya Zargi El-Rufai Da APC Kan Haifar Da Rashin Tsaro Don Neman Mulki
Manyan Labarai

Baba-Ahmed Ya Zargi El-Rufai Da APC Kan Haifar Da Rashin Tsaro Don Neman Mulki

October 16, 2025
Jami’an FRSC Sun Mayar Da N6.2m Da Suka Tsinta Bayan Aukuwar Hatsarin Mota A Katsina
Labarai

Jami’an FRSC Sun Mayar Da N6.2m Da Suka Tsinta Bayan Aukuwar Hatsarin Mota A Katsina

October 16, 2025
An Kashe Mutum 13 A Wasu Sabbin Hare-Hare A Ƙauyukan Filato
Manyan Labarai

An Kashe Mutum 13 A Wasu Sabbin Hare-Hare A Ƙauyukan Filato

October 16, 2025
Next Post
Sauye-sauyen Manufofin Gwamnati Na Iya Hana Masu HND Zuwa NYSC

Gwamnati Ta Ɗage Haramcin Tura Masu Yi Wa Ƙasa Hidima Bankuna Da Sauran Masana’antu 

LABARAI MASU NASABA

Gwamnan Edo Ya Umarci Kwamishinoni Su Riƙa Sanya Hular Tinubu

Gwamnan Edo Ya Umarci Kwamishinoni Su Riƙa Sanya Hular Tinubu

October 16, 2025
Baba-Ahmed Ya Zargi El-Rufai Da APC Kan Haifar Da Rashin Tsaro Don Neman Mulki

Baba-Ahmed Ya Zargi El-Rufai Da APC Kan Haifar Da Rashin Tsaro Don Neman Mulki

October 16, 2025
Jami’an FRSC Sun Mayar Da N6.2m Da Suka Tsinta Bayan Aukuwar Hatsarin Mota A Katsina

Jami’an FRSC Sun Mayar Da N6.2m Da Suka Tsinta Bayan Aukuwar Hatsarin Mota A Katsina

October 16, 2025
An Kashe Mutum 13 A Wasu Sabbin Hare-Hare A Ƙauyukan Filato

An Kashe Mutum 13 A Wasu Sabbin Hare-Hare A Ƙauyukan Filato

October 16, 2025
Sauya Sheƙa: Diri Da Wasu Na Guje Wa Matsalolin Da Suka Ƙirƙiro – Dickson

Sauya Sheƙa: Diri Da Wasu Na Guje Wa Matsalolin Da Suka Ƙirƙiro – Dickson

October 16, 2025
Sashen Cinikayyar Kamfanonin Sarrafa Hajoji Na Sin Ya Bunkasa Da Kaso 4.7 Bisa Dari Cikin Watanni Tara Na Farkon Shekarar Nan

Sashen Cinikayyar Kamfanonin Sarrafa Hajoji Na Sin Ya Bunkasa Da Kaso 4.7 Bisa Dari Cikin Watanni Tara Na Farkon Shekarar Nan

October 15, 2025
Kafafen Sada Zumunta Na Zamani Suna Taimakawa Wajen Ta’azzara Matsalar Tsaro A Arewa – Yari 

Kafafen Sada Zumunta Na Zamani Suna Taimakawa Wajen Ta’azzara Matsalar Tsaro A Arewa – Yari 

October 15, 2025
Nazarin CGTN: Jamaar Duniya Sun Yi Ammana Amurka Za Ta Fi Jin Jiki Daga Yakin Haraji 

Nazarin CGTN: Jamaar Duniya Sun Yi Ammana Amurka Za Ta Fi Jin Jiki Daga Yakin Haraji 

October 15, 2025
Kotu Ta Ɗaure Mai Horas Da ‘Yan Wasa Shekaru 8 Sakamakon Zargin Luwaɗi Da Ƙaramin Yaro A Kano

Kotu Ta Ɗaure Mai Horas Da ‘Yan Wasa Shekaru 8 Sakamakon Zargin Luwaɗi Da Ƙaramin Yaro A Kano

October 15, 2025
Sojoji Sun Yi Juyin Mulki A Ƙasar Madagascar

Sojoji Sun Yi Juyin Mulki A Ƙasar Madagascar

October 15, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.