• English
  • Business News
Sunday, June 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kiyaye Rayukan Al’umma: Majalisa Na Shirin Keɓe Wa Masu Sayar Da Iskar Gas Wuri A Wajen Birnin Kano

by Sulaiman
7 months ago
in Manyan Labarai
0
Kiyaye Rayukan Al’umma: Majalisa Na Shirin Keɓe Wa Masu Sayar Da Iskar Gas Wuri A Wajen Birnin Kano
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Majalisar dokokin jihar Kano ta fara yunkurin garambawul ga dokar hukumar kashe gobara ta jihar mai lamba 17 ta shekarar 1970 domin sanya wani sashe na doka kan yawaitar masu sayar da iskar gas – na girki a cikin birnin Kano.

 

Hakan ya biyo bayan gabatar da rahoton da kwamitin kula da ayyuka na musamman ya gabatar a kan binciken da ya yi kan sayar da iskar gas a cikin unguwanni a yayin zaman majalisar da kakakin majalisar Hon. Ismail Falgore ya jagoranta.

  • Majalisar Dokokin Kano Ta Yi Watsi Da Ƙudirin Gyaran Dokar Haraji A Nijeriya
  • An Gudanar Da Dandalin Tattaunawa Tsakanin Kafofin Watsa Labarai Na Bidiyo Na Kasa Da Kasa Karo Na 12 A Birnin Quanzhou

Da yake gabatar da rahoton, shugaban kwamitin wanda kuma shi ne mamba mai wakiltar mazaɓar Gezawa, Abdullahi Yahaya, ya bayyana cewa, hukumar kashe gobara ta jihar Kano ta bayar da rahoton kimanin gidaje 475 na masu sayar da iskar gas ba bisa ka’ida ba bayan tattaunawa da masu ruwa da tsaki a jihar.

 

Labarai Masu Nasaba

Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

Ya kuma kara da cewa, alkaluman da hukumar sa ido kan harkokin man fetur ta Nijeriya (NMDPRA) reshen jihar Kano ta fitar ya nuna cewa, akwai masu sayar da iskar gas guda 234 da ba su da lasisi a jihar.

 

A cewarsa, an gudanar da binciken ne biyo bayan wani kudiri da dan majalisa mai wakiltar mazaɓar Kiru, Hon. Tasiu Abubakar ya gabatar game da hatsarin da ke tattare da sayar da iskar gas acikin al’umma da kuma buƙatar samar masu wasu keɓaɓɓun wurare domin kiyaye rayuka da dukiyoyin al’umma.

 

Shugaban kwamitin ya ce, binciken ya takaita ne a kan babban birnin Kano, kuma ‘yan kadan ne daga cikin masu sayar da iskar gas din da suka yi rajista da NMDPRA.

 

Sai dai kwamitin ya ba da shawarar cewa, ya kamata gwamnatin jihar ta samar da wurin dindindin ga masu sayar da iskar gas a kofofin shiga birnin Kano guda shida, kamar dai yadda ta yi wa masu sayar da magunguna da wayar salula a jihar, inda ta kebe musu wuri daban.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: GobaraLPGMan iskar gas
ShareTweetSendShare
Previous Post

Sin Ta Jaddada Kudurinta Na Kara Inganta Daidaito Da Tsaro A Tekun Guinea

Next Post

Hukumar NDLEA Ta Kama Mutane 14,480 A Cikin Watanni 10 – Marwa

Related

Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki
Manyan Labarai

Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki

12 hours ago
Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa
Manyan Labarai

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

1 day ago
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe
Manyan Labarai

Rasuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Afirka – Atiku

1 day ago
Rasuwar Ɗantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu
Manyan Labarai

Rasuwar Ɗantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu

1 day ago
Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe
Manyan Labarai

Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe

1 day ago
Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa
Manyan Labarai

Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

1 day ago
Next Post
Hukumar NDLEA Ta Kama Mutane 14,480 A Cikin Watanni 10 – Marwa

Hukumar NDLEA Ta Kama Mutane 14,480 A Cikin Watanni 10 – Marwa

LABARAI MASU NASABA

Shugaban Majalisar Dokokin Jama’ar Kasar Mexico: Tunanin Raya Al’umma Mai Kyakkyawar Makoma Ga Dukkan Bil’adama Da Shugaba Xi Jinping Ya Gabatar Ya Kayatar

Shugaban Majalisar Dokokin Jama’ar Kasar Mexico: Tunanin Raya Al’umma Mai Kyakkyawar Makoma Ga Dukkan Bil’adama Da Shugaba Xi Jinping Ya Gabatar Ya Kayatar

June 29, 2025
Sin Na Adawa Da Duk Wata Yarjejeniyar Haraji Da Ka Iya Illata Moriyarta

Sin Na Adawa Da Duk Wata Yarjejeniyar Haraji Da Ka Iya Illata Moriyarta

June 29, 2025
2027: Ƴan Adawa Na Ƙara Ƙaimin Kawar Da Tinubu

2027: Ƴan Adawa Na Ƙara Ƙaimin Kawar Da Tinubu

June 29, 2025
Yadda Yaƙin Iran Da Isra’ila Zai Iya Shafar Zamantakewa Da Tattalin Arziƙin Nijeriya

Yadda Yaƙin Iran Da Isra’ila Zai Iya Shafar Zamantakewa Da Tattalin Arziƙin Nijeriya

June 29, 2025
Ƙwallon Mata: Rivers United Ta Doke Nasarawa Amazons A Wasan Ƙarshe Na Kofin Shugaban Ƙasa

Ƙwallon Mata: Rivers United Ta Doke Nasarawa Amazons A Wasan Ƙarshe Na Kofin Shugaban Ƙasa

June 29, 2025
Xi Ya Yi Kira Ga Mazauna Wani Kauye Dake Xizang Da Su Rike ‘Yan Uwantakar Kabila

Xi Ya Yi Kira Ga Mazauna Wani Kauye Dake Xizang Da Su Rike ‘Yan Uwantakar Kabila

June 29, 2025
Zaben 2027 Yaƙi Ne Tsakanin Talakawa Da Masu Mulki – Sanata Kaita 

Zaben 2027 Yaƙi Ne Tsakanin Talakawa Da Masu Mulki – Sanata Kaita 

June 29, 2025
Gyaran Tsarin Mulki: Majalisa Ta Shirya Sauraron Jin Ra’ayoyin Jama’a A Wasu Sassan Nijeriya

Gyaran Tsarin Mulki: Majalisa Ta Shirya Sauraron Jin Ra’ayoyin Jama’a A Wasu Sassan Nijeriya

June 29, 2025
Yara 150,000 Ake Haifa Da Cutar Sikila A Nijeriya Duk Shekara – Rahoto

Yara 150,000 Ake Haifa Da Cutar Sikila A Nijeriya Duk Shekara – Rahoto

June 29, 2025
Mutuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya – Gov Ododo

Mutuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya – Gov Ododo

June 29, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.