• English
  • Business News
Sunday, November 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shirin NG-CARES: Gwamna Lawal Ya Tallafawa Mutane 44,000 Da Fiye Da Naira Biliyan 4 

by Sulaiman
11 months ago
NG-CARES

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal ya ƙaddamar da rabon kuɗaɗe don tallafa wa masu ƙaramin ƙarfi a jihar.

 

Rabon kuɗaɗen wani ɓangare ne na Farfaɗo da Ayyukan Tattalin Arziki da suka durƙushe a sanadiyyar COVID-19 na ‘NG-CARES’, wanda aka gudanar a ɗakin taro na Garba Nadama, Sakatariyar JB Yakubu a Gusau.

  • Babu Wanda Zai Ci Nasara Daga Ayyukan Lalata Tsarin Samar Da Kayayyaki Na Duniya
  • Shehu Sani Ya Ƙalubalanci Sarki Sanusi II Kan Maganar ‘Mari’

Shirin kyautata jin daɗin jama’ar ya shafi masu ƙaramin ƙarfi 44,000 a faɗin ƙananan hukumomi 14 a wani ɓangare na shirin Gwamnatin Jihar Zamfara.

 

LABARAI MASU NASABA

NBA Ta Yi Allah Wadai Da Yadda Hukuncin Alƙalai Ke Karo Da Juna

Mataimakin Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kebbi Bagudo Ya Shaƙi Iskar ‘Yanci Daga ‘Yan Bindiga

A yayin ƙaddamar da shirin miƙa tallafin, Gwamna Lawal ya bayyana cewa za a raba Naira Miliyan 4,964,000,000 ga masu ƙaramin ƙarfi a matsayin waɗanda za su amfana.

 

Gwamnan ya jaddada cewa, ta hanyar ƙaddanar da shirin kyaitata jin daɗin jama’a, jihar Zamfara ta samu ci gaba mai ma’ana, inda sama da mutane miliyan 1.1 suka ci gajiyar shirin a sassa daban-daban.

 

“Waɗannan nasarorin sun samu ne daga Hukumar Cigaban Al’umma tamu, Fadama III Project, da ma’aikatar kasuwanci da dai sauransu.

 

“Shirin ya ba da sakamakonbda ake so, kuma an yi shi cikin tsari, tare da samun kusan Naira biliyan 64 a cikin zagaye uku. Wannan nasara ce ta sa jiharmu ta samu karbuwa a matakin ƙasa.

 

“Na ratsa ɗaukacin ƙananan hukumomi 14 na jihar domin ƙaddamar da shirin Farfaɗo da Tattalin Arziki na COVID-19 a ƙarƙashin ƙungiyar FADAMA III tsakanin watan Janairu zuwa Fabrairu 2024. Mun tabbatar da cewa ba a bar wata al’umma a baya ba; wannan yunƙurin da aka yi ya ba da gudunmawa sosai wajen ganin jiharmu ta samu gagarumar kima a idon Bankin Duniya saboda bajintar da muka yi wajen aiwatar da shirin.”

 

Bugu da ƙari, Gwamna Lawal ya jaddada cewa bangaren miƙa kufi na shirin yana da nau’i huɗu. “Na farko shi ne tsarin samar da ayyukan yi ga al’umma, wanda duk wanda ya ci gajiyar shirin zai riƙa karbar Naira 20,000 duk wata a tsawon shekara ɗaya.

 

“Domin tabbatar da daidaito, kashi 60 na wannan kason an ware shi ne ga mata, yayin da sauran kashi 40 na maza ne.

 

“Kashi 60 ɗin na mata zai shafi matan da mazansu suka mutu, waɗanda aka kashe, da kuma ma’aikatan asibitin sa kai waɗanda ke hidima ba tare da albashi ba.

 

“Yayin da ake amfani da rajistar zamantakewa, sarakunanmu masu daraja za su taka muhimmiyar rawa wajen zaƙulo wafanda suka cancanta daga al’ummominsu.

 

“Kashi na biyu kuma shi ne na ‘Social Transfers’, inda za a riƙa bayar da Naira 10,000 duk wata na tsawon shekara faɗa ga bangaren nakasassu, marasa lafiya da kuma tsofaffi.

 

“Wannan tallafin an yi niyya ne don sauƙaƙe nauyi a kan waɗanda ke fuskantar ƙalubale yau da kullum da kuma tabbatar da cewa za su iya rayuwa cikin mutunci da kwanciyar hankali.

 

“Tallafin Rayuwa na biyan Naira 150,000 zai dunfari masu ƙananan sana’o’i ne.

 

“An yi la’akari daidai wa daida ga maza da mata, wanda ake so ya ƙara bunƙasa sa’o’in al’umma. Tun daga samarwa zuwa sayarwa, wannan yunƙuri na da niyyar farfaɗo da ƙananan sana’o’i da haifar da tasirin ci gaban tattalin arziki a cikin al’ummominmu.

 

“Hakazalika, tallafin Naira 50,000 wnada za a biya a lokaci ɗaya zai shafi ƙungiyoyin da aka yi niyya, waɗanda suka haɗa da ’Yan Agaji, gidajen mata, da kuma malamai na Makarantun Allo da Islamiyya. An tsara wannan matakin ne don ƙarfafa sassa daban-daban na jama’a da kuma ƙarfafa tushen tattalin arzikin yankinmu.”

 

Gwamnan ya yaba wa kwamitin gudanarwa na NG-CARES da sassan aiwatarwa bisa jajircewarsu wajen ganin an samu sakamakon da ake buƙata.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

NBA Ta Yi Allah Wadai Da Yadda Hukuncin Alƙalai Ke Karo Da Juna
Labarai

NBA Ta Yi Allah Wadai Da Yadda Hukuncin Alƙalai Ke Karo Da Juna

November 9, 2025
Mataimakin Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kebbi Bagudo Ya Shaƙi Iskar ‘Yanci Daga ‘Yan Bindiga
Labarai

Mataimakin Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kebbi Bagudo Ya Shaƙi Iskar ‘Yanci Daga ‘Yan Bindiga

November 9, 2025
Soludo Ya Sake Lashe Zaɓen Gwamnan Anambra
Labarai

Soludo Ya Sake Lashe Zaɓen Gwamnan Anambra

November 9, 2025
Next Post
NEMA Ta Bayar Da Tallafin Kayan Agaji Ga Wadanda Harin ‘Yan Bindiga Ya Shafa A Zamfara

NEMA Ta Bayar Da Tallafin Kayan Agaji Ga Wadanda Harin ‘Yan Bindiga Ya Shafa A Zamfara

LABARAI MASU NASABA

Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Na Ci Gaba Da Zama Muhimmin Ginshiki Ga Ci Gaban Nahiyar 

Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Na Ci Gaba Da Zama Muhimmin Ginshiki Ga Ci Gaban Nahiyar 

November 9, 2025
An Rufe Taron Kolin Wuzhen Na Ayyukan Yanar Gizo Na Duniya Na Shekarar 2025

An Rufe Taron Kolin Wuzhen Na Ayyukan Yanar Gizo Na Duniya Na Shekarar 2025

November 9, 2025
Katsina United Ta Shiga Komar Hukuncin Hukumar NPFL

Katsina United Ta Shiga Komar Hukuncin Hukumar NPFL

November 9, 2025
Xi Ya Gana Da Shugabar IOC Tare Da Shugaban IOC Na Karramawa

Xi Ya Gana Da Shugabar IOC Tare Da Shugaban IOC Na Karramawa

November 9, 2025
CMG Ya Cimma Yarjejeniyar Samun Iznin Watsa Shirye-shiryen Wasannin Olympics Daga Shekarar 2026 Zuwa 2032

CMG Ya Cimma Yarjejeniyar Samun Iznin Watsa Shirye-shiryen Wasannin Olympics Daga Shekarar 2026 Zuwa 2032

November 9, 2025
Kasar Sin Ta Yi Nasarar Harba Sabbin Taurarin Dan Adam Na Gwaji

Kasar Sin Ta Yi Nasarar Harba Sabbin Taurarin Dan Adam Na Gwaji

November 9, 2025
Shugaba Xi Ya Ayyana Bude Gasar Wasanni Ta Kasa Karo Na 15

Shugaba Xi Ya Ayyana Bude Gasar Wasanni Ta Kasa Karo Na 15

November 9, 2025
Mizanin Farashin Kayan Masarufi Na Kasar Sin Ya Karu Da 0.2% A Watan Oktoba

Mizanin Farashin Kayan Masarufi Na Kasar Sin Ya Karu Da 0.2% A Watan Oktoba

November 9, 2025
Me Ke Haddasa Yawaitar Farmakar Ƴan Wasa A Gasar Firimiyar Nijeriya

Me Ke Haddasa Yawaitar Farmakar Ƴan Wasa A Gasar Firimiyar Nijeriya

November 9, 2025
NBA Ta Yi Allah Wadai Da Yadda Hukuncin Alƙalai Ke Karo Da Juna

NBA Ta Yi Allah Wadai Da Yadda Hukuncin Alƙalai Ke Karo Da Juna

November 9, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.