• English
  • Business News
Tuesday, October 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Minista Ya Buƙaci Jihohi Su Sake Tunani Kan Duk Wani Yunƙurin Rushe Ma’aikatun Yaɗa Labarai

by Sulaiman
11 months ago
Minista

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya yi kira ga gwamnatocin jihohi da ke tunanin rusawa ko rage matsayin Ma’aikatun yada Labarai da su sake tunani, yana mai jaddada mahimmancin su wajen hulɗa da jama’a, wayar da kai, da kuma haɗin kan al’umma.

 

Idris ya yi wannan kiran ne yayin taron Majalisar Ƙasa kan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai karo na 48 a Kaduna a ranar Juma’a, mai taken “Inganta Gudanar da Yaɗa Labarai don Shugabanci Mai Haɗin Kai: Ajandar Sabunta Fata.”

  • ASUU Reshen Jami’ar Sa’adu Zungur Ta Dakatar Da Yajin Aiki
  • Rai Da Lafiyar Mazajenmu Ya Fi Mana Jarumtarsu

Ya ce, “A wannan lokaci, ina son yin roƙo mai matuƙar mahimmanci ga wasu daga cikin gwamnatocin jihohin mu, musamman kan matsayi da ayyukan Ma’aikatun Yaɗa Labarai na Jihohi.

 

LABARAI MASU NASABA

An Matsa Min Sai Na Koma Jam’iyyar APC – Gwamnan Filato

’Yansanda Sun Ƙaryata Rahoton Ƙone Gidan Shugaban Jam’iyyar PDP A Bauchi

“Kuma roƙo na shi ne: a shugabanci, ba za a taɓa musanta muhimmancin Ma’aikatun Labarai ba a matakin tarayya da jiha. Waɗannan Ma’aikatu sun zama wata gada tsakanin manufofin gwamnati da ‘yan ƙasa da aka tsara su amfana da su, ta yadda za su samar da gaskiya, da riƙon amana, waɗanda su ne ginshiƙan kowace dimokiraɗiyya mai ci gaba.”

 

Idris ya jaddada cewa Ma’aikatun Yaɗa Labarai suna da matuƙar muhimmanci wajen wayar da kan jama’a, yaƙi da labaran ƙarya, da tabbatar da isar da manufofi da shirye-shiryen gwamnati yadda ya kamata.

 

Ya bayyana ma’aikatar a matsayin “jigon dimokiraɗiyya da cigaba,” musamman a ƙasa mai ɗimbin bambance-bambance kamar Nijeriya.

 

Da yake magana akan Ajandar Sabunta Fata na Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu, Idris ya ce wannan kira ne na shugabanci mai kawo sauyi wanda ya dogara kan haɗin kai da gaskiya.

 

Ya ce shugabanci ya ta’allaƙa ne ga iyawarsa na haɗawa, sadarwa, da ƙarfafa haɗin gwiwar jama’a.

 

Ministan ya shawarci Manajojin Watsa Labarai da su yi amfani da fasaha, ciki har da na’ura mai ƙwaƙwalwa (AI), don inganta sauri da sahihancin saƙonnin su.

 

Ya kuma jaddada muhimmancin muhawarar jama’a wajen gyaran manufofi, yana bada misali da tattaunawar da ake yi kan sauye-sauyen haraji da Shugaba Tinubu ya gabatar.

 

“A kowace dimokuraɗiyya, karfin shugabanci yana da tushe sosai a cikin ikonsa na nuna muradun jama’a. Manufofin jama’a, yayin da aka ƙera su da kyakkyawar niyya, dole ne su ci gaba da bunƙasa don biyan buƙatu da tsammanin ‘yan ƙasa,” inji Idris.

 

Idris ya kuma jaddada buƙatar horas da jami’an yaɗa labarai kan dabarun tabbatar da gaskiya da haɓaka haɗin gwiwa da kafofin watsa labarai don yaƙi da labaran ƙarya.

 

Ya bayyana cewa Shugaba Tinubu kwanan nan ya amince da sakin kuɗi don fara aiki da Cibiyar UNESCO ta Category-2 Media and Information Literacy (MIL), wacce za a kafa a Buɗaɗɗiyar Jami’ar Nijeriya (NOUN) da ke Abuja.

 

Ya ce, “A lokacin da labaran ƙarya, furofaganda, da rahotannin son zuciya ke iya tasiri sosai kan ra’ayin jama’a da yanke shawara, fahimtar kafofin watsa labarai yana ƙarfafa tunani mai zurfi.

 

“Yana taimaka wa mutane su nazarci manufar saƙonnin kafofin watsa labarai, su fahimci yanayin da aka gabatar da su, da kuma tantance sahihancin su.

 

“Don haka ina kira ga Kwamishinonin Yaɗa Labarai da su yi amfani da wannan cibiya mai matuƙar muhimmanci da zarar ta fara aiki domin ƙara inganta ƙwarewar ma’aikatansu wajen yaƙar labaran ƙarya,” inji shi.

 

Gwamnan Jihar Kaduna, Sanata Uba Sani, shi ne ya buɗe taron.

 

Taron ya samu halartar manyan masu ruwa da tsaki da suka haɗa da Sanata Kenneth Eze, Shugaban Kwamitin Majalisar Dattawa kan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, da Hon. Olusola Steve Fatoba, Shugaban Kwamitin Majalisar Wakilai kan Yaɗa Labarai, Wayar da Kai, Ɗa’a, da Ɗabi’u.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

An Matsa Min Sai Na Koma Jam’iyyar APC – Gwamnan Filato
Manyan Labarai

An Matsa Min Sai Na Koma Jam’iyyar APC – Gwamnan Filato

October 28, 2025
’Yansanda Sun Ƙaryata Rahoton Ƙone Gidan Shugaban Jam’iyyar PDP A Bauchi
Labarai

’Yansanda Sun Ƙaryata Rahoton Ƙone Gidan Shugaban Jam’iyyar PDP A Bauchi

October 28, 2025
Mutum 18 Sun Mutu, 40 Sun Jikkata A Hatsarin Mota A Kebbi 
Labarai

An Kashe Mutum 10 A Harin Ramuwar Gayya A Jihar Kebbi

October 28, 2025
Next Post
Sin Ta Fitar Da Matakan Zamanantar Da Sana’ar Hada-Hadar Kayayyaki

Sin Ta Fitar Da Matakan Zamanantar Da Sana'ar Hada-Hadar Kayayyaki

LABARAI MASU NASABA

An Matsa Min Sai Na Koma Jam’iyyar APC – Gwamnan Filato

An Matsa Min Sai Na Koma Jam’iyyar APC – Gwamnan Filato

October 28, 2025
’Yansanda Sun Ƙaryata Rahoton Ƙone Gidan Shugaban Jam’iyyar PDP A Bauchi

’Yansanda Sun Ƙaryata Rahoton Ƙone Gidan Shugaban Jam’iyyar PDP A Bauchi

October 28, 2025
Mutum 18 Sun Mutu, 40 Sun Jikkata A Hatsarin Mota A Kebbi 

An Kashe Mutum 10 A Harin Ramuwar Gayya A Jihar Kebbi

October 28, 2025
Ganduje Na Kara Shan Matsin Lamba A Kan Ya Sauka

Zargin Almundahana: An Ɗage Shari’ar  Ganduje Da Matarsa Saboda Rashin Miƙa Takardu

October 28, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

Sojoji Sun Kashe Masu Yi Wa ISWAP 4 Safarar Makamai A Borno

October 28, 2025
Minista

APC Ta Yi Barazanar Dakatar Duk Kwamishinan Da Bai Sanya Irin Hular Tinubu Ba

October 27, 2025
An Yi Taron Tattaunawa Tsakanin Kasa Da Kasa A Amurka

An Yi Taron Tattaunawa Tsakanin Kasa Da Kasa A Amurka

October 27, 2025
Wakilan Sin Da Na Amurka Sun Yi Tattaunawa Mai Ma’ana Da Zurfi Da Kuma Amfani

Wakilan Sin Da Na Amurka Sun Yi Tattaunawa Mai Ma’ana Da Zurfi Da Kuma Amfani

October 27, 2025
Ribar Manyan Masana’antun Kasar Sin Ta Karu Da Kashi 3.2 Cikin Dari A Watanni Tara Na Farkon Bana

Ribar Manyan Masana’antun Kasar Sin Ta Karu Da Kashi 3.2 Cikin Dari A Watanni Tara Na Farkon Bana

October 27, 2025
Gwamnan Bauchi Ya Tabbatar Da Burgediya Janar Yake a Matsayin Sarkin Ƙabilar Sayawa

Gwamnan Bauchi Ya Tabbatar Da Burgediya Janar Yake a Matsayin Sarkin Ƙabilar Sayawa

October 27, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.