• English
  • Business News
Saturday, November 1, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ministan Yaɗa Labarai Ya Yaba Wa BPP Kan Fayyace Gaskiya Wajen Sayen Kayayyaki

by Sulaiman
9 months ago
BPP

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya yaba wa Hukumar Sayen Kayayyaki ta Ƙasa (BPP) kan ƙoƙarin ta na inganta gaskiya da riƙon amana a wajen sayen kayayyaki da bayar da kwangiloli.

A wata ganawa da ya yi a Abuja a ranar Alhamis tare da Babban Daraktan BPP, Dakta Adebowale Adedokun, da wasu shugabannin hukumar, Idris ya jinjina wa ƙoƙarin hukumar na sauƙaƙa tsarin sayan kayayyaki.

  • Sojoji Sun Kashe Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda, Sun Kama Masu Safarar Makamai, Sun Ceto Mutane
  • ‘Yan Nijeriya Za Su Maka Gwamnati A Kotu Kan Karin Kudin Kiran Waya

Ya nanata jajircewar Gwamnatin Tarayya ƙarƙashin Ajandar Sabunta Fata na tabbatar da gaskiya wajen bayar da kwangiloli.

Ya ce: “Kafin yanzu, ana ɓoye-ɓoye wajen sayen kayayyaki sau da yawa. Ina farin cikin cewa kuna bayyana komai yanzu. Babu abin da ya kamata a ɓoye. Idan wannan kamfani ya samu kwangila, a bari kowa ya sani cewa wannan kamfani ya samu kwangilar kuma waɗannan su ne dalilan. Idan aka ci gaba da wannan bayyana gaskiyar da hukumar ku ke yi, to zan iya tabbatar maku da cewa idan mutum ya rasa wata kwangila ba zai yi baƙin ciki ba.”

Idris ya bayyana sabon tsarin BPP na kammala sayen kayayyaki cikin kwana 20 a matsayin wani babban cigaba wanda ke nuna ƙwaƙƙwaran jagoranci da sha’awar kawo gyara.

LABARAI MASU NASABA

Trump Ya Ayyana Nijeriya A Matsayin Ƙasar Da Rayuwar Kiristoci Ke Cikin Hatsari

An Tsare Wani Mutum A Gidan Yari Kan Zargin Kashe Matarsa Saboda Ƙuli-Ƙuli A Kano

Ya ƙara da cewa ingantaccen tsarin sayen kayayyaki zai taimaka wajen adana albarkatu don kawar da talauci a ƙasa.

Ministan ya kuma tabbatar da cewa ma’aikatar sa za ta haɗa kai da BPP wajen wayar da kan jama’a kan tsarin sayen kayayyaki da kuma yaƙi da lalata kayan gwamnati.

Ya kuma bayyana cewa an sauya sunan ma’aikatar sa zuwa Ma’aikatar Yaɗa Labarai da Wayar da Kai ne domin a mayar da hankali kan wayar da kan jama’a da dawo da ƙimar ƙasa.

Ya ce: “Abin da Shugaban Ƙasa ke ƙoƙarin faɗi shi ne cewa akwai sabon mayar da hankali kan wayar da kai da dawo da darajar ƙasa, kuma Shugaban Ƙasa zai ƙaddamar da Yarjejeniyar Ɗa’a ta Ƙasa nan ba da jimawa ba a madadin ’yan Nijeriya.”

A nasa ɓangaren, Babban Daraktan jukumar ta BPP, Dakta Adebowale Adedokun, ya jaddada ƙoƙarin hukumar na aiwatar da tsarin sayen kayayyaki mai gaskiya da adalci.

Ya bayyana cewa dole ne dukkan ma’aikatu da hukumomin gwamnati su kammala sayen kayayyaki kafin ƙarshen rabin shekara.

Dakta Adedokun ya sanar da cewa hukumar tana komawa tsarin sayen kayayyaki na onlayin don bai wa masu kwangila daga sassa daban-daban na ƙasa da ƙetare damar shiga tsarin.

Ya kuma ce an fara tantance masu ba da shawara da masu ba da sabis don taimaka wa ‘yan kwangilar gida su iya yin gasa a yadda ake yi a ko’ina a duniya.

Domin inganta gaskiya, ya ce dole ne ma’aikatu da hukumomin gwamnati su gabatar da rahotannin kwata-kwata na kwangilolin da aka bayar, ciki har da sunayen ‘yan kwangilar, waɗanda za a wallafa su a gidan yanar BPP.

Haka kuma an samar da sababbin ƙa’idojin sayen kayayyakin aikin asibiti, tsaro na abinci, da motoci don tabbatar da daidaiton tsarin.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Donald Trump Zai Gurfana A Gaban Kotu Kan Tuhumar Da Ake Masa
Manyan Labarai

Trump Ya Ayyana Nijeriya A Matsayin Ƙasar Da Rayuwar Kiristoci Ke Cikin Hatsari

October 31, 2025
Yadda Waliyin Amarya Ya Sace Sadaki A Kano
Manyan Labarai

An Tsare Wani Mutum A Gidan Yari Kan Zargin Kashe Matarsa Saboda Ƙuli-Ƙuli A Kano

October 31, 2025
Gwamna Uba Sani Ya Gabatar Da Kudirorin Raya Jihar Kaduna A Taron Ƙoli Na Biranen Asiya A Dubai 
Labarai

Gwamna Uba Sani Ya Gabatar Da Kudirorin Raya Jihar Kaduna A Taron Ƙoli Na Biranen Asiya A Dubai 

October 31, 2025
Next Post
NPA Ta Tara Kudin Shiga Naira Biliyan 758.2 A 2024

NPA Ta Tara Kudin Shiga Naira Biliyan 758.2 A 2024

LABARAI MASU NASABA

CMG Ta Kammala Gabatar Da Rahoto Kan Ganawar Shugabannin Sin Da Amurka

CMG Ta Kammala Gabatar Da Rahoto Kan Ganawar Shugabannin Sin Da Amurka

October 31, 2025
Ministan Wajen Malawi: Tsarin Ci Gaban Kasar Sin Ya Samar Da Darussa Ga Kasashe Masu Tasowa

Ministan Wajen Malawi: Tsarin Ci Gaban Kasar Sin Ya Samar Da Darussa Ga Kasashe Masu Tasowa

October 31, 2025
Xi: A Shirye Sin Take Ta Hada Hannu Da Canada Wajen Mayar Da Dangantakarsu Bisa Turbar Da Ta Dace

Xi: A Shirye Sin Take Ta Hada Hannu Da Canada Wajen Mayar Da Dangantakarsu Bisa Turbar Da Ta Dace

October 31, 2025
Donald Trump Zai Gurfana A Gaban Kotu Kan Tuhumar Da Ake Masa

Trump Ya Ayyana Nijeriya A Matsayin Ƙasar Da Rayuwar Kiristoci Ke Cikin Hatsari

October 31, 2025
Yadda Waliyin Amarya Ya Sace Sadaki A Kano

An Tsare Wani Mutum A Gidan Yari Kan Zargin Kashe Matarsa Saboda Ƙuli-Ƙuli A Kano

October 31, 2025
Xi Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Kolin Shugabannin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

Xi Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Kolin Shugabannin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

October 31, 2025
Gwamna Uba Sani Ya Gabatar Da Kudirorin Raya Jihar Kaduna A Taron Ƙoli Na Biranen Asiya A Dubai 

Gwamna Uba Sani Ya Gabatar Da Kudirorin Raya Jihar Kaduna A Taron Ƙoli Na Biranen Asiya A Dubai 

October 31, 2025
Ya Kamata Sin Da Amurka Su Zama Kawayen Juna Ba Abokan Gaba Ba

Ya Kamata Sin Da Amurka Su Zama Kawayen Juna Ba Abokan Gaba Ba

October 31, 2025
Zaben 2027 Zai Kasance Ne Tsakanin Mulkin Tinubu Da Zabin Ƴan Nijeriya —Atiku Abubakar

Zaben 2027 Zai Kasance Ne Tsakanin Mulkin Tinubu Da Zabin Ƴan Nijeriya —Atiku Abubakar

October 31, 2025
Makarantar Kogi Poly Ta Bankaɗo Masu Ƙirƙirar Takardun Kammala Karatu na Bogi

Makarantar Kogi Poly Ta Bankaɗo Masu Ƙirƙirar Takardun Kammala Karatu na Bogi

October 31, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.