• English
  • Business News
Wednesday, August 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ministan Yaɗa Labarai Ya Yaba Wa BPP Kan Fayyace Gaskiya Wajen Sayen Kayayyaki

by Sulaiman
7 months ago
in Labarai
0
Ministan Yaɗa Labarai Ya Yaba Wa BPP Kan Fayyace Gaskiya Wajen Sayen Kayayyaki
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya yaba wa Hukumar Sayen Kayayyaki ta Ƙasa (BPP) kan ƙoƙarin ta na inganta gaskiya da riƙon amana a wajen sayen kayayyaki da bayar da kwangiloli.

A wata ganawa da ya yi a Abuja a ranar Alhamis tare da Babban Daraktan BPP, Dakta Adebowale Adedokun, da wasu shugabannin hukumar, Idris ya jinjina wa ƙoƙarin hukumar na sauƙaƙa tsarin sayan kayayyaki.

  • Sojoji Sun Kashe Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda, Sun Kama Masu Safarar Makamai, Sun Ceto Mutane
  • ‘Yan Nijeriya Za Su Maka Gwamnati A Kotu Kan Karin Kudin Kiran Waya

Ya nanata jajircewar Gwamnatin Tarayya ƙarƙashin Ajandar Sabunta Fata na tabbatar da gaskiya wajen bayar da kwangiloli.

Ya ce: “Kafin yanzu, ana ɓoye-ɓoye wajen sayen kayayyaki sau da yawa. Ina farin cikin cewa kuna bayyana komai yanzu. Babu abin da ya kamata a ɓoye. Idan wannan kamfani ya samu kwangila, a bari kowa ya sani cewa wannan kamfani ya samu kwangilar kuma waɗannan su ne dalilan. Idan aka ci gaba da wannan bayyana gaskiyar da hukumar ku ke yi, to zan iya tabbatar maku da cewa idan mutum ya rasa wata kwangila ba zai yi baƙin ciki ba.”

Idris ya bayyana sabon tsarin BPP na kammala sayen kayayyaki cikin kwana 20 a matsayin wani babban cigaba wanda ke nuna ƙwaƙƙwaran jagoranci da sha’awar kawo gyara.

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Imo Ta Amince Da N104,000 A Matsayin Sabon Mafi Ƙarancin Albashin Ma’aikata 

‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane 8 A Kaduna, Sun Jikkata Wasu

Ya ƙara da cewa ingantaccen tsarin sayen kayayyaki zai taimaka wajen adana albarkatu don kawar da talauci a ƙasa.

Ministan ya kuma tabbatar da cewa ma’aikatar sa za ta haɗa kai da BPP wajen wayar da kan jama’a kan tsarin sayen kayayyaki da kuma yaƙi da lalata kayan gwamnati.

Ya kuma bayyana cewa an sauya sunan ma’aikatar sa zuwa Ma’aikatar Yaɗa Labarai da Wayar da Kai ne domin a mayar da hankali kan wayar da kan jama’a da dawo da ƙimar ƙasa.

Ya ce: “Abin da Shugaban Ƙasa ke ƙoƙarin faɗi shi ne cewa akwai sabon mayar da hankali kan wayar da kai da dawo da darajar ƙasa, kuma Shugaban Ƙasa zai ƙaddamar da Yarjejeniyar Ɗa’a ta Ƙasa nan ba da jimawa ba a madadin ’yan Nijeriya.”

A nasa ɓangaren, Babban Daraktan jukumar ta BPP, Dakta Adebowale Adedokun, ya jaddada ƙoƙarin hukumar na aiwatar da tsarin sayen kayayyaki mai gaskiya da adalci.

Ya bayyana cewa dole ne dukkan ma’aikatu da hukumomin gwamnati su kammala sayen kayayyaki kafin ƙarshen rabin shekara.

Dakta Adedokun ya sanar da cewa hukumar tana komawa tsarin sayen kayayyaki na onlayin don bai wa masu kwangila daga sassa daban-daban na ƙasa da ƙetare damar shiga tsarin.

Ya kuma ce an fara tantance masu ba da shawara da masu ba da sabis don taimaka wa ‘yan kwangilar gida su iya yin gasa a yadda ake yi a ko’ina a duniya.

Domin inganta gaskiya, ya ce dole ne ma’aikatu da hukumomin gwamnati su gabatar da rahotannin kwata-kwata na kwangilolin da aka bayar, ciki har da sunayen ‘yan kwangilar, waɗanda za a wallafa su a gidan yanar BPP.

Haka kuma an samar da sababbin ƙa’idojin sayen kayayyakin aikin asibiti, tsaro na abinci, da motoci don tabbatar da daidaiton tsarin.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

2027: PDP Ta Kara Tsunduma Cikin Rikicin Shugabanci

Next Post

NPA Ta Tara Kudin Shiga Naira Biliyan 758.2 A 2024

Related

Gwamnatin Imo Ta Amince Da N104,000 A Matsayin Sabon Mafi Ƙarancin Albashin Ma’aikata 
Manyan Labarai

Gwamnatin Imo Ta Amince Da N104,000 A Matsayin Sabon Mafi Ƙarancin Albashin Ma’aikata 

35 minutes ago
Mazauna Kuyello A Jihar Kaduna Na Cikin Zullumin Bayyanar ‘Yan Ta’addar Ansaru
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane 8 A Kaduna, Sun Jikkata Wasu

3 hours ago
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba
Labarai

‘Yansanda Sun Ceto Mutum 5 Da Aka Sace A Jihar Kebbi

5 hours ago
Jirgin Ƙasan Abuja-Kaduna Ya Yi Hatsari, Ba A San Halin Da Fasinjoji Ke Ciki Ba
Manyan Labarai

NRC Ta Dakatar Da Sufurin Jirgin Ƙasan Abuja-Kaduna Bayan Hatsarin Da Ya Yi 

5 hours ago
PDP Na Tattaunawa Da Obi Da Jonathan Kan Yi Mata Takarar Shugaban Ƙasa A 2027 – Moro
Manyan Labarai

PDP Na Tattaunawa Da Obi Da Jonathan Kan Yi Mata Takarar Shugaban Ƙasa A 2027 – Moro

7 hours ago
Kwalara Ta Kashe Mutum 7 A Zamfara, Sama Da Mutum 200 Sun Kamu Da Cutar
Manyan Labarai

Kwalara Ta Kashe Mutum 7 A Zamfara, Sama Da Mutum 200 Sun Kamu Da Cutar

8 hours ago
Next Post
NPA Ta Tara Kudin Shiga Naira Biliyan 758.2 A 2024

NPA Ta Tara Kudin Shiga Naira Biliyan 758.2 A 2024

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Imo Ta Amince Da N104,000 A Matsayin Sabon Mafi Ƙarancin Albashin Ma’aikata 

Gwamnatin Imo Ta Amince Da N104,000 A Matsayin Sabon Mafi Ƙarancin Albashin Ma’aikata 

August 27, 2025
Mazauna Kuyello A Jihar Kaduna Na Cikin Zullumin Bayyanar ‘Yan Ta’addar Ansaru

‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane 8 A Kaduna, Sun Jikkata Wasu

August 27, 2025
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

‘Yansanda Sun Ceto Mutum 5 Da Aka Sace A Jihar Kebbi

August 27, 2025
Jirgin Ƙasan Abuja-Kaduna Ya Yi Hatsari, Ba A San Halin Da Fasinjoji Ke Ciki Ba

NRC Ta Dakatar Da Sufurin Jirgin Ƙasan Abuja-Kaduna Bayan Hatsarin Da Ya Yi 

August 27, 2025
PDP Na Tattaunawa Da Obi Da Jonathan Kan Yi Mata Takarar Shugaban Ƙasa A 2027 – Moro

PDP Na Tattaunawa Da Obi Da Jonathan Kan Yi Mata Takarar Shugaban Ƙasa A 2027 – Moro

August 27, 2025
Kwalara Ta Kashe Mutum 7 A Zamfara, Sama Da Mutum 200 Sun Kamu Da Cutar

Kwalara Ta Kashe Mutum 7 A Zamfara, Sama Da Mutum 200 Sun Kamu Da Cutar

August 27, 2025
Gwamnati Ta Fara Aikin Gyara Na’urar Watsa Shirye-shirye Mai Gajeren Zango Ta Gidan Rediyon Muryar Nijeriya

Gwamnati Ta Fara Aikin Gyara Na’urar Watsa Shirye-shirye Mai Gajeren Zango Ta Gidan Rediyon Muryar Nijeriya

August 26, 2025
Shin Mummunan Halin Da Aka Shiga Yayin Yakin Duniya Na II Bai Isa Darasi Ba?

Shin Mummunan Halin Da Aka Shiga Yayin Yakin Duniya Na II Bai Isa Darasi Ba?

August 26, 2025
Gwamna Buni Ya Kaddamar Da Dashen Bishiyoyi Na 2025

Gwamna Buni Ya Kaddamar Da Dashen Bishiyoyi Na 2025

August 26, 2025
Firaministan Kasar Sin Li Qiang Ya Taya Nestor Ntahontuye Murnar Zama Sabon Firaministan Kasar Burundi

Firaministan Kasar Sin Li Qiang Ya Taya Nestor Ntahontuye Murnar Zama Sabon Firaministan Kasar Burundi

August 26, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.