• English
  • Business News
Thursday, November 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ministan Wajen Sin Ya Gana Da Manyan Jami’an Kasashe Daban Daban

by CGTN Hausa and Sulaiman
9 months ago
Sin

A jiya Asabar, ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi, ya gana da manyan jami’an kasashen Jamus, da Faransa, da Isra’ila, da Ukraine, da sauransu, a birnin Munich na kasar Jamus.

Yayin ganawarsa da shugaban gwamnatin kasar Jamus Olaf Scholz, mista Wang Yi ya ce, kasar Sin na son zurfafa hadin kai daga dukkan fannoni tare da kasar Jamus, don tabbatar da kyautatar huldar kasashen 2, da samun kwanciyar hankali a duniya. Kana a nasa bangare, mista Olaf Scholz ya ce kasar Jamus ba ta yarda da yunkurin ta da “yakin harajin kwastam” a duniya ba, kuma tana fatan ganin bangarorin Turai da Sin su cimma matsaya cikin sauri, wajen daidaita sabanin ra’ayinsu ta fuskar cinikayyar motoci masu amfani da wutar lantarki.

  • Tinubu Ya Buƙaci A Mayar Wa BUK Filin Rimin Zakara Da Ake Taƙaddama A Kai
  • Kishin Ƙasa Da Tsoron Allah Ne Mafita Daga Matsin Tattalin Arziƙin Ƙasar Nan – Malam Usman

Sa’an nan, duk a jiya Asabar din, Wang Yi ya gana da takwaransa na kasar Faransa, Jean-Noel Barrot, inda bangarorin 2 suka amince da karfafa hadin gwiwar kasashensu kan batun kula da al’amuran duniya, da ingiza hadin kan kasashen duniya a kokarin tinkarar kalubalolin da dan Adam ke fuskanta.

Ban da haka, yayin da yake ganawa da ministan harkokin wajen kasar Isra’ila Gideon Sa’ar, minista Wang Yi ya ce, mafitar da ake da ita wajen daidaita batun Gabas ta Tsakiya, ta shafi aiwatar da manufar tabbatar da wanzuwar kasashe 2, wato Isra’ila da Falasdinu, a yankin da suke ciki, ta yadda za a cimma burin kasancewar kasashen 2 cikin lumana a karshe. A nata bangare, kasar Sin za ta ci gaba da kokarin kare adalci, da samar da gudunmowa ga aikin daidaita maganar Falasdinu daga tushenta, in ji mista Wang.

Haka zalika, a lokacin da yake ganawa da Andriy Sybiga, ministan harkokin wajen kasar Ukraine, Wang Yi ya ce, kungiyar “Abokan zaman lafiya” da Sin da sauran kasashe masu tasowa suka kafa, za ta ci gaba da taka rawar gani, a kokarin kawo karshen yakin da ake yi a Ukraine ta hanyar sulhuntawa da shawarwari.

LABARAI MASU NASABA

Mao Ning: Harka Da Kasar Sin Mabudi Ne Na Samun Damammaki

Li Chenggang Ya Gana Da Tawagar Cinikayyar Kayan Noma Ta Amurka

Har ila yau a jiya Asabar, Wang Yi ya kuma gana da jami’an kasahen Brazil, da Czech, gami da Austria. (Bello Wang)

 

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Mao Ning: Harka Da Kasar Sin Mabudi Ne Na Samun Damammaki
Daga Birnin Sin

Mao Ning: Harka Da Kasar Sin Mabudi Ne Na Samun Damammaki

November 5, 2025
Li Chenggang Ya Gana Da Tawagar Cinikayyar Kayan Noma Ta Amurka
Daga Birnin Sin

Li Chenggang Ya Gana Da Tawagar Cinikayyar Kayan Noma Ta Amurka

November 5, 2025
Yanayi Mai Launin Zinare A Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Yanayi Mai Launin Zinare A Kasar Sin

November 5, 2025
Next Post
Ƴansanda Sun Kama Saurayin Da Ya Kashe Budurwarsa Ta Facebook A Kwara

Ƴansanda Sun Kama Saurayin Da Ya Kashe Budurwarsa Ta Facebook A Kwara

LABARAI MASU NASABA

Jirgin Ƙasa Ya Murƙushe Direban Adaidaita Sahu Da Fasinja A Jos

Jirgin Ƙasa Ya Murƙushe Direban Adaidaita Sahu Da Fasinja A Jos

November 6, 2025
Osimhen Ya Kafa Tarihi A Gasar Zakarun Turai Bayan Zura Ƙwallo 3 A Ragar Ajax

Osimhen Ya Kafa Tarihi A Gasar Zakarun Turai Bayan Zura Ƙwallo 3 A Ragar Ajax

November 6, 2025
Ɓarayi Sun Shiga Ofishin Shugaban Karama Hukuma A Kano, Sun Tafka Sata

Ɓarayi Sun Shiga Ofishin Shugaban Karama Hukuma A Kano, Sun Tafka Sata

November 6, 2025
Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP

Majalisa Ta Ɗage Tantance Ministan Tinubu Saboda Rashin Rahoton Tsaro

November 6, 2025
Mao Ning: Harka Da Kasar Sin Mabudi Ne Na Samun Damammaki

Mao Ning: Harka Da Kasar Sin Mabudi Ne Na Samun Damammaki

November 5, 2025
Yadda Gwamna Lawal Ya Aiwatar Da Ayyukan Gina Zamfara Na Naira Biliyan 140

Yadda Gwamna Lawal Ya Aiwatar Da Ayyukan Gina Zamfara Na Naira Biliyan 140

November 5, 2025
Li Chenggang Ya Gana Da Tawagar Cinikayyar Kayan Noma Ta Amurka

Li Chenggang Ya Gana Da Tawagar Cinikayyar Kayan Noma Ta Amurka

November 5, 2025
Majalisar Dattawa

Majalisa Ta Amince Da Ɗaurin Shekaru 14 A Gidan Yari Ga Malamai Masu Cin Zarafin Mata A Jami’o’i

November 5, 2025
Yanayi Mai Launin Zinare A Kasar Sin

Yanayi Mai Launin Zinare A Kasar Sin

November 5, 2025
Dantsoho Ya Nemi Hadin Kan Kasashen Afrika Wajen Bunkasa Tashoshin Jiragen Ruwa

Dantsoho Ya Nemi Hadin Kan Kasashen Afrika Wajen Bunkasa Tashoshin Jiragen Ruwa

November 5, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.