• English
  • Business News
Monday, June 23, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wakilin Sin Ya Yi Allah Wadai Kan Sabon Yaki Da Isra’ila Ta Tayar A Zirin Gaza

by CGTN Hausa and Sulaiman
3 months ago
in Daga Birnin Sin
0
Wakilin Sin Ya Yi Allah Wadai Kan Sabon Yaki Da Isra’ila Ta Tayar A Zirin Gaza
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Sakamakon manyan hare-hare ta sama da Isra’ila ta kaddamar a zirin Gaza, wakilin dindindin na kasar Sin dake MDD Fu Cong ya ce Sin ta yi matukar bakin ciki yadda aka lalata yanayin tsagaita bude wuta mai wahalar gaske da aka cimma a zirin Gaza. Kazalika, Sin na bayyana matukar damuwa, da yin Allah wadai da sake haifar da yakin da Isra’ila ke yi a zirin Gaza.

Fu Cong, wanda ya bayyana hakan a jiya Talata, a taron kwamitin sulhu kan batun Falasdinu da Isra’ila. Ya ce daukar matakan soja ba ita ce hanyar warware matsalar Falasdinu da Isra’ila ba. Kuma kasar Sin na fatan Isra’ila za ta yi watsi da aniyarta ta amfani da karfi, ta dakatar da ayyukan soji a zirin Gaza nan take, sannan ta daina azabtar da fararen hula dake zirin Gaza baki daya.

  • El-Rufai Ya Shiga Tsilla-tsilla Bayan Rasa Kujerar Minista – APC
  • ‘Yan Bindiga Sun Sace Mutum 7 A Jihar Neja

Fu Cong ya ce, kasar Sin na matukar bukatar tsagaita bude wuta mai dorewa a zirin Gaza, tana kuma adawa da mayar da taimakon jin kai wani makami na yaki ko kuma siyasantar da batun. Kasar Sin ta bukaci Isra’ila da ta sauke nauyin da ya rataya a wuyanta, game da mamayar da take yi, a karkashin dokar jin kai ta kasa da kasa, tare da ba da damar ci gaba da shigar da kayayyakin jin kai zuwa zirin Gaza.

Fu Cong ya ce, kasar Sin na kira da a sake farfado da ra’ayin siyasa na kafa “kasashe biyu”, da kuma aiwatar da “manufofin kasashe biyu”, a matsayin hanya daya tilo da za a bi don warware batun Falasdinu.

Bugu da kari, Fu Cong ya bayyana cewa, bangaren Sin yana goyon bayan kwamitin sulhu na MDD, da ya ci gaba da daukar matakai na sa kaimi ga tsagaita bude wuta a zirin Gaza, da maido da zaman lafiya a yankin Gabas ta Tsakiya, da kuma warware batun Falasdinu cikin daidaito, da adalci da yanayi mai dorewa. (Safiyah Ma)

Labarai Masu Nasaba

Za A Gudanar Da Taron Davos Na Yanayin Zafi Na Bana A Birnin Tianjin

Me Ya Sa Kamfanonin Kasa Da Kasa Ke Da Imanin Gudanar Da Harkokinsu A Kasar Sin?


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

‘Yan Bindiga Sun Sace Mutum 7 A Jihar Neja

Next Post

Matatar Dangote Ta Dakatar Da Sayar Da Man Fetur A Naira

Related

Za A Gudanar Da Taron Davos Na Yanayin Zafi Na Bana A Birnin Tianjin
Daga Birnin Sin

Za A Gudanar Da Taron Davos Na Yanayin Zafi Na Bana A Birnin Tianjin

16 hours ago
Me Ya Sa Kamfanonin Kasa Da Kasa Ke Da Imanin Gudanar Da Harkokinsu A Kasar Sin?
Daga Birnin Sin

Me Ya Sa Kamfanonin Kasa Da Kasa Ke Da Imanin Gudanar Da Harkokinsu A Kasar Sin?

18 hours ago
Gwamnatin Hong Kong Ta Gudanar Da Bikin Cika Shekaru Biyar Da Kafuwar Dokar Tsaron Kasa Ta Yankin
Daga Birnin Sin

Gwamnatin Hong Kong Ta Gudanar Da Bikin Cika Shekaru Biyar Da Kafuwar Dokar Tsaron Kasa Ta Yankin

20 hours ago
Sin Ta Yi Matukar Allah Wadai Da Hare-Haren Da Amurka Ta Kaiwa Iran
Daga Birnin Sin

Sin Ta Yi Matukar Allah Wadai Da Hare-Haren Da Amurka Ta Kaiwa Iran

21 hours ago
CMG Ya Ja Hankulan Baki A Dandalin Tattaunawar Tattalin Arziki Na Kasa Da Kasa Na St. Petersburg Karo Na 28 
Daga Birnin Sin

CMG Ya Ja Hankulan Baki A Dandalin Tattaunawar Tattalin Arziki Na Kasa Da Kasa Na St. Petersburg Karo Na 28 

2 days ago
Yankin Taiwan Ya Yi Taron Bikin Bauta Na Kakan Gargajiyar Sin Fuxi
Daga Birnin Sin

Yankin Taiwan Ya Yi Taron Bikin Bauta Na Kakan Gargajiyar Sin Fuxi

2 days ago
Next Post
Matatar dangote

Matatar Dangote Ta Dakatar Da Sayar Da Man Fetur A Naira

LABARAI MASU NASABA

Yanzu-yanzu: Zanga-zanga Ta Ɓarke A Jami’ar Neja Bayan Kashe Ɗalibi

Yanzu-yanzu: Zanga-zanga Ta Ɓarke A Jami’ar Neja Bayan Kashe Ɗalibi

June 23, 2025
Ina Da Isassun Kuɗi, Ban Ciwo Bashin Ko Kwabo Ɗaya Don Gyara Jihar Zamfara Ba – Gwamna Lawal

Ina Da Isassun Kuɗi, Ban Ciwo Bashin Ko Kwabo Ɗaya Don Gyara Jihar Zamfara Ba – Gwamna Lawal

June 23, 2025
NNPCL Ya Rage Farashin Man Fetur Zuwa ₦860 Kan Kowacce Lita – IPMAN

Yakin Iran Da Isra’ila Ya Haifar Da Tashin Farashin Litar Man Fetur A Nijeriya

June 23, 2025
Hajji 2025: Kashi Na Farko Na Alhazan Abuja Sun Dawo Gida Nijeriya

Hajji 2025: Kashi Na Farko Na Alhazan Abuja Sun Dawo Gida Nijeriya

June 23, 2025
Gwamnan Abba Kabir Yusuf tare da Arch. Ali Hassan

Abba Ya Dace Ya Zama Gwamnan Kano Na Har Abada Ba Shekaru 8 Kaɗai Ba – Arch Ali Hassan

June 23, 2025
2027: Wajibi Ne A Saka Sakamakon Zaɓe A Na’ura – Farfesa Jega

2027: Wajibi Ne A Saka Sakamakon Zaɓe A Na’ura – Farfesa Jega

June 22, 2025
Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (6)

Nijeriya Da Brazil Sun Ƙulla Yarjejeniyar Horar Da Matasa Kiwon Dabbobi

June 22, 2025
Za A Gudanar Da Taron Davos Na Yanayin Zafi Na Bana A Birnin Tianjin

Za A Gudanar Da Taron Davos Na Yanayin Zafi Na Bana A Birnin Tianjin

June 22, 2025
Mun Gano Wurare 52 Da Ake Aikata Laifuka A Kano – Janar Mai Adda’u

Mun Gano Wurare 52 Da Ake Aikata Laifuka A Kano – Janar Mai Adda’u

June 22, 2025
Me Ya Sa Kamfanonin Kasa Da Kasa Ke Da Imanin Gudanar Da Harkokinsu A Kasar Sin?

Me Ya Sa Kamfanonin Kasa Da Kasa Ke Da Imanin Gudanar Da Harkokinsu A Kasar Sin?

June 22, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.