• English
  • Business News
Thursday, July 3, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ministan Yaɗa Labarai Ya Zayyana Wa Masu Zuba Jari Na Faransa Irin Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Nijeriya

by Sulaiman
3 months ago
in Labarai
0
Ministan Yaɗa Labarai Ya Zayyana Wa Masu Zuba Jari Na Faransa Irin Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Nijeriya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya jawo hankalin masu zuba jari daga ƙasar Faransa, inda ya jaddada masu irin sauye-sauyen tattalin arziki masu ƙayatarwa, damar kasuwanci mai faɗi da yanayin da ya dace da masu zuba jari yanzu a Nijeriya, a wani yunƙuri na Gwamnatin Tarayya na ƙara janyo jarin ƙetare na dogon lokaci.

 

A sanarwar da Rabiu Ibrahim, Mai Taimaka wa Ministan kan Harkokin Yaɗa Labarai, ya bayar, Idris ya bayyana ƙudurin sa na zurfafa dangantakar tattalin arziki da Faransa yayin da yake magana a Taron Kasuwanci na Nijeriya da aka gudanar a birnin Paris a ranar Alhamis.

  • An Kaddamar Da Bikin Nuna Fina-Finan Sinanci Na CMG Karo Na 5
  • Huawei Ya Daddale Yarjejeniya Da Kenya Don Habaka Kwarewar Ma’aikatan Kasar A Fannin Dijital

Taron, wanda kamfanin Business France ya shirya, ya samu halartar kamfanonin Faransa fiye da 200 tun a shekarar 2023.

 

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Yobe Ta Rufe Kasuwanni Uku Saboda Fargabar Hare-haren Boko Haram

Ɗan Wasan Liverpool, Diogo Jota, Ya Mutu A Hatsarin Mota

Idris ya gode wa kamfanonin Faransa da suka daɗe suna aiki a Nijeriya, irin su TotalEnergies, Lafarge, Peugeot, Danone, Alstom, Schneider Electric da sauran su, saboda gudunmawar da suke bayarwa a sassa daban-daban na ƙasar nan kamar makamashi, ababen more rayuwa, noma, lafiya da masana’antu.

 

Idris ya ce a ƙarƙashin jagorancin Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu, Nijeriya tana kan “tafarkin sauyi da ba a taɓa ganin irin sa ba” wanda Ajandar Sabunta Fata ke ɗauke da shi.

 

Ya ce: “Waɗannan sauye-sauyen tarihi na gina tattalin arzikin da ya fi gasa, mai gaskiya da amfanar masu zuba jari, suna mayar da Nijeriya ƙofar shiga kasuwar masu saye ta Afirka wadda ke bunƙasa, ƙarƙashin Yankin Ciniki Cikin ’Yanci na Nahiyar Afirka (AfCFTA).”

 

Wasu daga cikin sauye-sauyen da ya yi nuni da su sun haɗa da:

 

Daidaita tsarin musayar kuɗi, cire tallafin mai domin daƙile asara, tsarin farashin wutar lantarki da ya dace domin ɗorewar sabis.

 

Sauran sun haɗa da sauye-sauyen haraji da ke inganta gaskiya da sauƙaƙe kasuwanci, sababbin dokoki da tsare-tsaren kuɗi da ke ba da goyon baya ga masu zaman kan su, sauƙaƙe harkokin shigo da kaya ta hanyar National Single Window, da sauye-sauyen dijital ciki har da tsare-tsaren shige da fice.

 

Ministan ya ce Nijeriya tana da fa’ida ta musamman ga masu zuba jari: ita ce mafi girman tattalin arziki a Afirka, yawan jama’a fiye da miliyan 220 — fiye da kashi 70 nasu kuma matasa ne ‘yan ƙasa da shekaru 35 — da kuma shekaru sama da 26 na dimokiraɗiyya ba tare da katsewa ba.

 

Ya ƙara da cewa gwamnati tana tabbatar da cewa tattalin arzikin ƙasar yana gudana ne ƙarƙashin ƙa’idojin doka, tare da tallafin hukumomin da suka haɗa da CBN, NIPC, SEC, da FCCPC.

 

Ministan ya ce a cikin watanni 20 kacal da gwamnatin Tinubu, an sauya tsarin kuɗi na ƙasa, inda aka samu ƙaruwa da kashi 3.84 na GDP a zangon farko na shekarar 2024, da samun ƙarin kuɗin shiga fiye da kashi 20, tare da rage yawan kuɗin da ake kashewa wajen biyan bashi.

 

Ya ce: “Gwamnatin ta kasance mai ƙarfafawa wajen haɓaka sashen masu zaman kan su ta hanyar wasu muhimman shirye-shirye kamar Asusun Raya Ababen More Rayuwa na Sabunta Fata (RHIDF), Hukumar Bai wa Jama’a Lamunin Kaya ta Nijeriya (CrediCorp), Shirin Fadar Shugaban Ƙasa na CNG, Asusun Zuba Jari na Gidaje na MOFI (MREIF), da wasu da dama.

 

“Waɗannan shirye-shiryen suna shimfiɗa tubalin da za a iya dogaro da shi wajen jawo zuba jari na tiriliyan-triliyan na naira daga sashen masu zaman kan su a fannonin ababen more rayuwa, lamunin kayan masarufi, kiwon lafiya, gidaje, da sauran su.”

 

Ya kuma bayyana cewa bankunan Nijeriya suna ƙara faɗaɗa zuwa Turai, ciki har da buɗe ofisoshi a birnin Paris, yana mai cewa Nijeriya za ta ƙara samun wakilci a Faransa ta fannoni kamar ƙere-ƙere, fasaha da yaɗa labarai.

 

Ya gayyaci kamfanonin Faransa — musamman masu sha’awar harkar noma — da su ci gajiyar sababbin damarmakin da ke akwai a sashen kiwon dabbobi na Nijeriya, inda sabuwar Ma’aikatar Raya Kiwon Dabbobi ta buɗe ƙofofin sababbin haɗin gwiwa.

 

Ya ce: “Dole ne mu shirya wa gaba da ƙwazo da fata mai kyau, tare da ƙarfin gwiwar da kakannin mu suka nuna.”

 

A yayin zaman sa a Paris, Minista Idris zai gana da manyan hukumomin yaɗa labarai da al’adu na Faransa, kamar France Médias Monde, ARCOM, Ma’aikatar Al’adu, da Thomson Broadcast, domin ƙarfafa dangantaka tsakanin Faransa da Nijeriya a fannin watsa shirye-shirye da yaɗa labarai.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Darussa Daga Tafsirin Ramadan Daga Masu Bibiya (2): Kyawawan Dabi’u Ke Fayyace Tsoron Allah A Musulunci

Next Post

Gobara Ta Ƙone Shaguna 12 A Kasuwar Siminti Ta Oyo

Related

Gwamnatin Yobe Ta Rufe Kasuwanni Uku Saboda Fargabar Hare-haren Boko Haram
Manyan Labarai

Gwamnatin Yobe Ta Rufe Kasuwanni Uku Saboda Fargabar Hare-haren Boko Haram

24 minutes ago
Ɗan Wasan Liverpool, Diogo Jota, Ya Mutu A Hatsarin Mota
Manyan Labarai

Ɗan Wasan Liverpool, Diogo Jota, Ya Mutu A Hatsarin Mota

2 hours ago
Mun Shirya Fuskantar APC Domin Ceto Talakawa – Abubakar Malami
Manyan Labarai

Mun Shirya Fuskantar APC Domin Ceto Talakawa – Abubakar Malami

5 hours ago
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba
Labarai

’Yansanda Sun Ceto Ɗan Ghana, Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 3

7 hours ago
Buhari Ba Shi Da Lafiya, Amma Yana Samun Sauƙi A Birtaniya — Garba Shehu
Manyan Labarai

Buhari Ba Shi Da Lafiya, Amma Yana Samun Sauƙi A Birtaniya — Garba Shehu

8 hours ago
Gwamnatin Kano Ta Haramta Shigo Ƙarafu Daga Arewa maso Gabas
Labarai

Gwamnatin Kano Ta Haramta Shigo Ƙarafu Daga Arewa maso Gabas

17 hours ago
Next Post
Gobara Ta Ƙone Shaguna 12 A Kasuwar Siminti Ta Oyo

Gobara Ta Ƙone Shaguna 12 A Kasuwar Siminti Ta Oyo

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Yobe Ta Rufe Kasuwanni Uku Saboda Fargabar Hare-haren Boko Haram

Gwamnatin Yobe Ta Rufe Kasuwanni Uku Saboda Fargabar Hare-haren Boko Haram

July 3, 2025
Ɗan Wasan Liverpool, Diogo Jota, Ya Mutu A Hatsarin Mota

Ɗan Wasan Liverpool, Diogo Jota, Ya Mutu A Hatsarin Mota

July 3, 2025
Mun Shirya Fuskantar APC Domin Ceto Talakawa – Abubakar Malami

Mun Shirya Fuskantar APC Domin Ceto Talakawa – Abubakar Malami

July 3, 2025
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Ceto Ɗan Ghana, Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 3

July 3, 2025
Buhari Ba Shi Da Lafiya, Amma Yana Samun Sauƙi A Birtaniya — Garba Shehu

Buhari Ba Shi Da Lafiya, Amma Yana Samun Sauƙi A Birtaniya — Garba Shehu

July 3, 2025
Kayayyakin Sin Sun Kara Baiwa Masu Sayayya Na Kasa Da Kasa Damar Samun Zabi

Kayayyakin Sin Sun Kara Baiwa Masu Sayayya Na Kasa Da Kasa Damar Samun Zabi

July 2, 2025
Gwamnatin Kano Ta Haramta Shigo Ƙarafu Daga Arewa maso Gabas

Gwamnatin Kano Ta Haramta Shigo Ƙarafu Daga Arewa maso Gabas

July 2, 2025
Firaministan Sin Zai Halarci Taron Shugabannin Kasashen BRICS Na 17 A Brazil Da Kuma Ziyarar Aiki A Masar

Firaministan Sin Zai Halarci Taron Shugabannin Kasashen BRICS Na 17 A Brazil Da Kuma Ziyarar Aiki A Masar

July 2, 2025
Sin Na Ci Gaba Da Cika Alkawarin Bude Kasuwarta Ga Duniya

Sin Na Ci Gaba Da Cika Alkawarin Bude Kasuwarta Ga Duniya

July 2, 2025
Tinubu Ya Ƙaddamar Da Cibiyar Fasahar Da Aka Lalata Lokacin Zanga-Zanga A Kano

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Cibiyar Fasahar Da Aka Lalata Lokacin Zanga-Zanga A Kano

July 2, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.